Har yanzun dai ba a san makomar tsohon mataimakin shugaban majalisar dattawan Nijeriya ba, Ike Ekweremadu, yayin da kotun manyan laifuka ta kasar Birtaniya ta dage sauraron karar da ake masa har sai ranar 31 ga watan Oktoban 2022.
Ekweremadu da Matarsa Beatrice, suna fuskantar tuhuma ne kan daukar wani yaro daga Nijeriya Mai shekaru 21 zuwa Kasar Birtaniya don cire masa Koda.
An kama Ekweremadu da Matarsa Beatrice ne a Birtaniya makonnin da suka gabata saboda zargin hada baki amma daga baya aka bayar da belin matarsa.
Cikakkun bayanai Daga baya…
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp