• English
  • Business News
Friday, August 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zargin Da Wasu ’Yan Siyasar Amurka Ke Yi Wa Sin Na Fitar Da Hajoji Fiye Da Kima Ya Sabawa Hujjoji Na Hakika

by CGTN Hausa and Sulaiman
22 hours ago
in Daga Birnin Sin
0
Zargin Da Wasu ’Yan Siyasar Amurka Ke Yi Wa Sin Na Fitar Da Hajoji Fiye Da Kima Ya Sabawa Hujjoji Na Hakika
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A baya bayan nan wasu ’yan siyasar kasar Amurka sun yi zargin cewa wai kasar Sin tana cika kasuwannin duniya da hajoji fiye da kima, don haka kamata ya yi Sin ta sake dadaita tsarin tattalin arzikinta. To sai dai kuma idan mun yi la’akari da dalilai na zahiri, za mu ga cewa wannan zargi ba shi da tushe bare makama. Kawai dai kokari ne na shafawa kasar Sin kashin kaji, musamman a wannan muhimmiyar gaba da ake ganin tattalin arzikin kasar Sin na kara shiga kyakkyawan yanayin ci gaba mai inganci.

Alal hakika, duk da cewa Sin na samar da tarin hajoji da ake fitarwa kasashen ketare, a daya hannun ana iya ganin yadda a shekarun baya bayan nan adadin hajojin kasar da ake fitarwa ketare na ta raguwa, kana Sin na kara fadada shigo da hajoji daga ketare, wadanda ya zuwa shekarar 2024 da ta gabata, darajarsu ta kai sama da dalar Amurka tiriliyan 2.64, adadin da ya ninka na shekara ta 2000 har sama da sau 10.

A yau, ci gaban tattalin arzikin kasar Sin na karuwa bisa dogaro da bukatun cikin gida. Har ma a shekarar 2024, alkaluma suka nuna yadda sayayya a cikin kasar ta samar da gudummawar sama da kaso 40 bisa dari na jimillar GDPn kasar, tare da zama daya daga manyan ginshikan bunkasa tattalin arzikin kasar.

Bugu da kari, Sin ta zamo babbar cibiyar raya bincike da fadada kere-keren masana’antu, wanda hakan ke kara jawo jarin waje zuwa cikin kasar, yayin da kuma sashen masana’antun kasar ke kara sauyawa zuwa mai samar da hajoji masu matukar inganci. Ana iya ganin hakan a fannin kera ababen hawa masu amfani da sabbin makamashi, inda fitar da su da kasar Sin ke yi zuwa ketare ke taimakawa wajen sauya tsarin masana’antunsu a matakin kasa da kasa. Baya ga kera ababen hawa masu aikin da sabbin makamashi, Sin ta kuma zamo cibiyar bincike da gwaje-gwaje a wannan fanni.

Yayin da wasu ’yan siyasar Amurka ke ganin ya zama wajibi Sin ta sauya salon gudanar da tattalin arzikinta, a daya bangaren masharhanta na ganin hakan wani yunkuri ne kawai na ingiza ajandar nan ta raba-gari da Sin, wadda kuma ba za ta taba yin nasara ba. Domin ta hanyar gudanar da sahihin hadin gwiwa ne kadai sassan kasa da kasa za su iya cimma nasarar dunkule tattalin arzikinsu waje guda, ba wai ta hanyar cimma riba ta hanyar gurgunta ci gaban wani bangare ba.

Labarai Masu Nasaba

Zhao Leji Ya Yi Jawabi A Babban Taron Shugabannin Majalisun Kasa Da Kasa Karo Na 6

Sin Ta Samarwa Sassan Kasa Da Kasa Damar Shigowa Ba Tare Da Bukatar Biza Ba


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamna Zulum Ya Sauke Kwamishinoni Biyu Tare Da Maye Gurbinsu Da Wasu

Next Post

Yadda Yajin Aikin Ma’aikatan Jinya Ya Bar Baya Da Kura A Asibitocin Jihar Filato

Related

Zhao Leji Ya Yi Jawabi A Babban Taron Shugabannin Majalisun Kasa Da Kasa Karo Na 6
Daga Birnin Sin

Zhao Leji Ya Yi Jawabi A Babban Taron Shugabannin Majalisun Kasa Da Kasa Karo Na 6

17 minutes ago
Sin Ta Samarwa Sassan Kasa Da Kasa Damar Shigowa Ba Tare Da Bukatar Biza Ba
Daga Birnin Sin

Sin Ta Samarwa Sassan Kasa Da Kasa Damar Shigowa Ba Tare Da Bukatar Biza Ba

1 hour ago
Mujallar Qiushi Za Ta Wallafi Jawabin Xi Jinping Game Da Kiyaye Muhallin Halittu
Daga Birnin Sin

Mujallar Qiushi Za Ta Wallafi Jawabin Xi Jinping Game Da Kiyaye Muhallin Halittu

18 hours ago
Matsayar Bai Daya Da Sin Da Amurka Suka Cimma Ta Fuskar Haraji Na Da Babbar Ma’ana
Daga Birnin Sin

Matsayar Bai Daya Da Sin Da Amurka Suka Cimma Ta Fuskar Haraji Na Da Babbar Ma’ana

20 hours ago
Mutane 44 Suka Mutu Bayan Mamakon Ruwa Da Aka Tafka A Beijing
Daga Birnin Sin

Mutane 44 Suka Mutu Bayan Mamakon Ruwa Da Aka Tafka A Beijing

20 hours ago
Uganda Ta Jinjinawa Gudummawar Sin Ga Manufofin Wanzar Da Zaman Lafiya A Yankin Kahon Afirka
Daga Birnin Sin

Uganda Ta Jinjinawa Gudummawar Sin Ga Manufofin Wanzar Da Zaman Lafiya A Yankin Kahon Afirka

1 day ago
Next Post
Yadda Yajin Aikin Ma’aikatan Jinya Ya Bar Baya Da Kura A Asibitocin Jihar Filato

Yadda Yajin Aikin Ma'aikatan Jinya Ya Bar Baya Da Kura A Asibitocin Jihar Filato

LABARAI MASU NASABA

Zhao Leji Ya Yi Jawabi A Babban Taron Shugabannin Majalisun Kasa Da Kasa Karo Na 6

Zhao Leji Ya Yi Jawabi A Babban Taron Shugabannin Majalisun Kasa Da Kasa Karo Na 6

August 1, 2025
Sin Ta Samarwa Sassan Kasa Da Kasa Damar Shigowa Ba Tare Da Bukatar Biza Ba

Sin Ta Samarwa Sassan Kasa Da Kasa Damar Shigowa Ba Tare Da Bukatar Biza Ba

August 1, 2025
Bashin Naira Tiriliyan 4 Na Barazanar ɗorewar Wutar Lantarki A Nijeriya – Minista

Bashin Naira Tiriliyan 4 Na Barazanar ɗorewar Wutar Lantarki A Nijeriya – Minista

August 1, 2025
Nijeriya Na Asarar Kusan Naira Tiriliyan 17.9 Duk Shekara Sakamakon Cutar Hanta — Gwamnati

Nijeriya Na Asarar Kusan Naira Tiriliyan 17.9 Duk Shekara Sakamakon Cutar Hanta — Gwamnati

August 1, 2025
GORON JUMA’A 01-07-2025

GORON JUMA’A 01-07-2025

August 1, 2025
An Zaɓi Saidu Yahya A Matsayin Shugaban Hukumar Yaƙi Da Cin Hanci Ta Kano

An Zaɓi Saidu Yahya A Matsayin Shugaban Hukumar Yaƙi Da Cin Hanci Ta Kano

August 1, 2025
Tinubu Ya Cika Alƙawurran Da Ya Ɗauka – Ƙungiyar Gwamnonin Arewa

Tinubu Ya Cika Alƙawurran Da Ya Ɗauka – Ƙungiyar Gwamnonin Arewa

August 1, 2025
Maraba Da Shekarar Hijirah Ta 1447 Manzon Allah (SAW) Zai Cika Shekara 1,500 Da Haihuwa

Maraba Da Shekarar Hijirah Ta 1447 Manzon Allah (SAW) Zai Cika Shekara 1,500 Da Haihuwa

August 1, 2025
Shekara 2 Ta Gwamnatin Tinubu: Gwamnonin Arewa Sun ƙaryata Zargin ACF Na Watsi ɗa Yankin

Shekara 2 Ta Gwamnatin Tinubu: Gwamnonin Arewa Sun ƙaryata Zargin ACF Na Watsi ɗa Yankin

August 1, 2025
Osimhen Ya Kammala Komawa Galatasaray

Osimhen Ya Kammala Komawa Galatasaray

August 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.