• English
  • Business News
Saturday, June 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zargin Tarayya Da Matar Aure: Miji Ya Ki Amincewa Da Hukuncin Kotun Da Ta Wanke Kwamishinan Jigawa

Gwamnan Jigawa Ya Mayar Da Kwamishinan Kan Mukaminsa

by Sulaiman
7 months ago
in Manyan Labarai
0
Zargin Tarayya Da Matar Aure: Miji Ya Ki Amincewa Da Hukuncin Kotun Da Ta Wanke Kwamishinan Jigawa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Nasiru Buba, mijin da ya zargi kwamishinan ayyuka na musamman na jihar Jigawa, Auwal Danladi Sankara da yin tarayyar da ta bata kamata ba da matarsa, ya ki amincewa da hukuncin da wata kotu ta yanke na wanke kwamishinan daga aikata ba daidai ba.

 

LEADERSHIP ta ruwaito cewa, wata babbar Kotun Shari’ar Musulunci ta Kano ta yi watsi da karar da ake yi wa Sankara a ranar Litinin din da ta gabata, saboda rashin samun hujjoji.

  • Kotu Ta Wanke Kwamishinan Jigawa Daga Zargin Zina
  • Gwamna Lawal Ya Ƙaddamar Da Aikin Gina Tashar Mota Ta Zamani A Gusau

Alkalin kotun, Ibrahim Sarki Yola ya yi fatali da karar bayan da ya amince da rahoton ‘yansandan da ya ce babu wata hujja da ke nuna cewa, Sankara ya aikata zargin da ake yi masa.

 

Labarai Masu Nasaba

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

Da yake mayar da martani ga hukuncin, Buba ya bayyana hakan a matsayin rashin adalci, inda ya dage cewa ya bayar da kwararan hujjoji da za su tabbatar da ikirarin nasa.

 

“Na gabatar da daruruwan shaidun da za a iya tantancewa, wadanda suka hada da hotuna 854, bidiyoyi fiye da 100, bayanan murya fiye da 200 a manhajar WhatsApp, da bayanan kiran waya na sama da sa’o’i 500. Idan kotu ta jefar da wadannan hujjoji, Allah da kuma mutanen da suka san gaskiya, ba za a goge su ba,” in ji Buba yayin da yake zantawa da manema labarai a Kano.

 

Lauyan Buba, Rabi’u Sidi, ya zargi kotun da jingine tawagar lauyoyin mai kara daga cikin shari’ar.

 

“Ba a sanar da mu zaman kotun ba. Babu wanda ya ce mana za a yi zama, kawai mun ji labarin hukuncin ne a cikin labarai,” in ji Sidi.

 

Ya kara da cewa tawagar lauyoyin za ta yi taro domin sanin matakin da za su dauka na gaba.

 

LEADERSHIP ta rahoto cewa, gwamnan jihar Jigawa, Malam Umar Namadi ya mayar da Sankara kan mukaminsa bayan kotu ta wanke zargin da aka yi masa.

 

Umarnin mayar da Kwamishinan bakin aiki na kunshe ne a cikin wata sanarwa da sakataren gwamnatin jihar, Malam Bala Ibrahim ya fitar ranar Talata.

 

Ibrahim ya ce, hukuncin ya biyo bayan wanke Sankara da wata kotun shari’a ta Kano ta yi kan zargin da ake masa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Kotun shari'aZargin lalata da matar aure
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamna Lawal Ya Ƙaddamar Da Aikin Gina Tashar Mota Ta Zamani A Gusau

Next Post

An Kaddamar Da Bikin Kafofin Watsa Labaru Kan Raya Harkokin Matasan Kasashe Masu Tasowa A Birnin Rio de Janeiro

Related

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa
Manyan Labarai

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

2 hours ago
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe
Manyan Labarai

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

3 hours ago
Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu
Manyan Labarai

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

6 hours ago
Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe
Manyan Labarai

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

7 hours ago
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa
Manyan Labarai

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

7 hours ago
Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu
Manyan Labarai

Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu

12 hours ago
Next Post
An Kaddamar Da Bikin Kafofin Watsa Labaru Kan Raya Harkokin Matasan Kasashe Masu Tasowa A Birnin Rio de Janeiro

An Kaddamar Da Bikin Kafofin Watsa Labaru Kan Raya Harkokin Matasan Kasashe Masu Tasowa A Birnin Rio de Janeiro

LABARAI MASU NASABA

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

June 28, 2025
Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

June 28, 2025
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

June 28, 2025
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

June 28, 2025
Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

June 28, 2025
An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

June 28, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

June 28, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

June 28, 2025
Sin Ta Samu Nasarorin A Zo A Gani Wajen Yaki Da Miyagun Kwayoyi

Sin Ta Samu Nasarorin A Zo A Gani Wajen Yaki Da Miyagun Kwayoyi

June 28, 2025
Kula Da  Kanki Bayan Haihuwa Abu Ne Muhimmi 4

Kula Da  Kanki Bayan Haihuwa Abu Ne Muhimmi 4

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.