• English
  • Business News
Saturday, November 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zargin Tarayya Da Matar Aure: Miji Ya Ki Amincewa Da Hukuncin Kotun Da Ta Wanke Kwamishinan Jigawa

Gwamnan Jigawa Ya Mayar Da Kwamishinan Kan Mukaminsa

by Sulaiman
12 months ago
Matar aure

Nasiru Buba, mijin da ya zargi kwamishinan ayyuka na musamman na jihar Jigawa, Auwal Danladi Sankara da yin tarayyar da ta bata kamata ba da matarsa, ya ki amincewa da hukuncin da wata kotu ta yanke na wanke kwamishinan daga aikata ba daidai ba.

 

LEADERSHIP ta ruwaito cewa, wata babbar Kotun Shari’ar Musulunci ta Kano ta yi watsi da karar da ake yi wa Sankara a ranar Litinin din da ta gabata, saboda rashin samun hujjoji.

  • Kotu Ta Wanke Kwamishinan Jigawa Daga Zargin Zina
  • Gwamna Lawal Ya Ƙaddamar Da Aikin Gina Tashar Mota Ta Zamani A Gusau

Alkalin kotun, Ibrahim Sarki Yola ya yi fatali da karar bayan da ya amince da rahoton ‘yansandan da ya ce babu wata hujja da ke nuna cewa, Sankara ya aikata zargin da ake yi masa.

 

LABARAI MASU NASABA

Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima

Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori

Da yake mayar da martani ga hukuncin, Buba ya bayyana hakan a matsayin rashin adalci, inda ya dage cewa ya bayar da kwararan hujjoji da za su tabbatar da ikirarin nasa.

 

“Na gabatar da daruruwan shaidun da za a iya tantancewa, wadanda suka hada da hotuna 854, bidiyoyi fiye da 100, bayanan murya fiye da 200 a manhajar WhatsApp, da bayanan kiran waya na sama da sa’o’i 500. Idan kotu ta jefar da wadannan hujjoji, Allah da kuma mutanen da suka san gaskiya, ba za a goge su ba,” in ji Buba yayin da yake zantawa da manema labarai a Kano.

 

Lauyan Buba, Rabi’u Sidi, ya zargi kotun da jingine tawagar lauyoyin mai kara daga cikin shari’ar.

 

“Ba a sanar da mu zaman kotun ba. Babu wanda ya ce mana za a yi zama, kawai mun ji labarin hukuncin ne a cikin labarai,” in ji Sidi.

 

Ya kara da cewa tawagar lauyoyin za ta yi taro domin sanin matakin da za su dauka na gaba.

 

LEADERSHIP ta rahoto cewa, gwamnan jihar Jigawa, Malam Umar Namadi ya mayar da Sankara kan mukaminsa bayan kotu ta wanke zargin da aka yi masa.

 

Umarnin mayar da Kwamishinan bakin aiki na kunshe ne a cikin wata sanarwa da sakataren gwamnatin jihar, Malam Bala Ibrahim ya fitar ranar Talata.

 

Ibrahim ya ce, hukuncin ya biyo bayan wanke Sankara da wata kotun shari’a ta Kano ta yi kan zargin da ake masa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima
Manyan Labarai

Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima

November 1, 2025
Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori
Manyan Labarai

Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori

November 1, 2025
Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna
Manyan Labarai

Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna

November 1, 2025
Next Post
An Kaddamar Da Bikin Kafofin Watsa Labaru Kan Raya Harkokin Matasan Kasashe Masu Tasowa A Birnin Rio de Janeiro

An Kaddamar Da Bikin Kafofin Watsa Labaru Kan Raya Harkokin Matasan Kasashe Masu Tasowa A Birnin Rio de Janeiro

LABARAI MASU NASABA

Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima

Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima

November 1, 2025
Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori

Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori

November 1, 2025
Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna

Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna

November 1, 2025
Sin: Katsalandan Cikin Harkokin Kamfani Da Netherlands Ta Yi Ya Kawo Tsaiko Ga Tsarin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki Na Duniya

Sin: Katsalandan Cikin Harkokin Kamfani Da Netherlands Ta Yi Ya Kawo Tsaiko Ga Tsarin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki Na Duniya

November 1, 2025
An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Duniya Kan Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Ci Gaba Na Bai Daya A Nijeriya

An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Duniya Kan Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Ci Gaba Na Bai Daya A Nijeriya

November 1, 2025
Sabbin ‘Yan Saman Jannatin Kasar Sin Sun Shiga Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar

Sabbin ‘Yan Saman Jannatin Kasar Sin Sun Shiga Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar

November 1, 2025
Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Koriya Ta Kudu Lee Jae-myung 

Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Koriya Ta Kudu Lee Jae-myung 

November 1, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

Babban Burina Zama Fitacciyar Jaruma A Duniya —Aisha Umar

November 1, 2025
Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik

Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik

November 1, 2025
Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami

Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami

November 1, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.