• English
  • Business News
Sunday, October 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ziyarar Firaministan Kasar Tsibiran Solomon A Kasar Sin Tana Da Babbar Ma’ana Ga Kasar

by CMG Hausa
2 years ago
Kasar Tsibiran

Yayin ziyararsa a kasar Sin a ranar 13 ga wannan wata, Firaministan kasar tsibiran Solomon Manasseh Sogavare, ya je lardin Jiangsu na kasar Sin, inda ya ziyarci kauyen Huanglongxian, mai tarihin al’adun shayin. Yayin ziyarar, firaministan ya gano yadda wannan kauye ya kawar da talauci ta hanyar amfani da albarkatun halittu da shuke-shuken shayi, lamarin da ya bayyana a matsayin misali da kasarsa ka iya koyi da shi. 

Wannan shi ne karo na biyu da firaminista Sogavare, ya ziyarci kasar Sin tun bayan kulla dangantakar diplomasiyya tsakanin Sin da kasarsa a shekarar 2019.

  • Kasar Sin Ta Bayyana Gudunmuwar Da Samun Ci Gaba Zai Bayar Ga Tabbatuwar Dukkan Hakkokin Bil Adama

Bugu da kari, yayin ziyarar, kasashen biyu sun kafa dangantakar abokantaka bisa manyan tsare-tsare a dukkan fannoni bisa girmama juna da samun bunkasuwa tare a sabon zamani.

A gun taron koli karo na farko na dandalin tattaunawar hadin gwiwa don samun ci gaban duniya da aka gudanar a birnin Beijing, Sogavare ya bayyana cewa, ana bukatar raya ayyukan more rayuwa masu inganta karfin tattalin arziki don kawar da talauci, kuma kasar Sin, abokiya ce mafi girma ga kasar tsibiran Solomon a wannan fannin. Yanzu, dakin wasannin motsa jiki da kasar Sin ta taimaka wajen ginawa domin gasar wasannin motsa jiki ta yankin tekun Pasifik ta shekarar 2023 a Honiara, babban birnin kasar tsibiran Solomon, ya riga ya kasance wata alama ta birnin.

Har ila yau a yayin ziyarar firaminista Sogavare, kasashen biyu sun daddale yarjejeniyoyi da dama dake shafar fannonin samun bunkasuwa, da cinikayya, da zirga-zirgar jiragen sama, da kwastam, da yanayi da sauransu, ta yadda za a zurfafa hadin gwiwar kasashen biyu. Kana an sada zumunta tsakanin lardin Guangdong da jihar Guadalcanal, da kuma tsakanin birnin Jiangmen da birnin Honiara, lamarin da zai fadada hadin gwiwar dake tsakanin kwamitocin tsakiya na kasashen biyu da kuma tsakanin hukumomin wuraren kasashen biyu, tare da kara fahimtar juna da sada zumunta a tsakanin jama’arsu. (Zainab)

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Ta Samar Da Tallafin Jinya Ga Kananan Yara Kyauta A Togo

An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tawagar Likitocin Sin Ta Samar Da Tallafin Jinya Ga Kananan Yara Kyauta A Togo
Daga Birnin Sin

Tawagar Likitocin Sin Ta Samar Da Tallafin Jinya Ga Kananan Yara Kyauta A Togo

October 19, 2025
An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin
Daga Birnin Sin

An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin

October 18, 2025
Kamfanin Gine-Gine Na CCECC Ya Fara Gina Wani Titin Mota Da Zai Rage Cunkoso A Birnin Abuja Na Tarayyar Najeriya
Daga Birnin Sin

Kamfanin Gine-Gine Na CCECC Ya Fara Gina Wani Titin Mota Da Zai Rage Cunkoso A Birnin Abuja Na Tarayyar Najeriya

October 18, 2025
Next Post
Yadda Kwamishinan Lafiya Na Kano Ke Sa Wa Ma’aikata Ido Don Hana Makara

Yadda Kwamishinan Lafiya Na Kano Ke Sa Wa Ma’aikata Ido Don Hana Makara

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Ta Samar Da Tallafin Jinya Ga Kananan Yara Kyauta A Togo

Tawagar Likitocin Sin Ta Samar Da Tallafin Jinya Ga Kananan Yara Kyauta A Togo

October 19, 2025
Sauya Sheƙa: APC Za Ta Lashe Kashi 95% Na Ƙuri’un Kaduna A 2027 – Gwamna Sani

Sauya Sheƙa: APC Za Ta Lashe Kashi 95% Na Ƙuri’un Kaduna A 2027 – Gwamna Sani

October 19, 2025
Ko Kin San… Yadda Za Ki Gyara Kanki Da Kanki?

Ko Kin San… Maganin Sanyi Na Mata (Infection)?

October 19, 2025
JTF Ta Kama Wani Da Ake Zargin Mai Safarar Miyagun Ƙwayoyi Ne Ga ‘Yan Bindiga A Jihar Kogi

JTF Ta Kama Wani Da Ake Zargin Mai Safarar Miyagun Ƙwayoyi Ne Ga ‘Yan Bindiga A Jihar Kogi

October 19, 2025
Abin Da Nijeriya Ke Bukata Kafin Samun Damar Zuwa Gasar Kofin Duniya

Abin Da Nijeriya Ke Bukata Kafin Samun Damar Zuwa Gasar Kofin Duniya

October 19, 2025
Yadda Ake Alkaki

Yadda Ake Alkaki

October 19, 2025
Kar Ki Yi Kuskuren Da Za Ki Yi Da Na Sani A Kai (1)

Kar Ki Yi Kuskuren Da Za Ki Yi Da Na Sani A Kai (2)

October 19, 2025
An Sanya Hannu Kan Yarjejiyar Zaman Lafiya A Gaza

An Sanya Hannu Kan Yarjejiyar Zaman Lafiya A Gaza

October 19, 2025
Nijar

Gwamnatin Nijar Ta Yaye Tsofaffin Mayaka 369 Da Aka Bai Wa Horon Sauya Tunani

October 19, 2025
Yadda Zargin Takardar Karatun Bogi Ta Tilasta Wa Minista Nnaji Murabus

‘Yan Siyasa 11 Da Suka Faɗa Dambarwar Takardar Shaidar Karatu Ta Bogi

October 19, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.