• English
  • Business News
Friday, July 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ƙasashe 7 Sun Mara Wa Nijeriya Baya Don Kafa Cibiyar Koyar Da Ilimin Yaɗa Labarai Ta UNESCO – Minista

by Sulaiman
6 months ago
in Labarai
0
Ƙasashe 7 Sun Mara Wa Nijeriya Baya Don Kafa Cibiyar Koyar Da Ilimin Yaɗa Labarai Ta UNESCO – Minista
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya bayyana cewa Nijeriya ta samu goyon bayan ƙasashe bakwai tare da alƙawuran ƙasashe 20 domin a kafa Cibiyar Koyar da Ilimin Yaɗa Labarai ta Duniya (IMILI) ta hukumar UNESCO.

 

Ita da UNESCO, ita ce Hukumar Ilimi da Kimiyya da Al’adu ta Majalisar Ɗinkin Duniya.

  • An Kashe Na Biyun Turji A Shugabanci Tare Da Fitattun Kwamandojin ‘Yan Bindiga A Zamfara 
  • Ba Mu Buƙatar Amincewar Sanusi Kan Tsare-tsarenmu Na Tattalin Arziki – Minista

A Turance, IMILI na nufin ‘International Media and Information Literacy Institute’.

 

Labarai Masu Nasaba

Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

Da yake jawabi a Abuja a ranar Talata yayin da ya karɓi baƙuncin tawagar UNESCO da ta zo duba shirin Nijeriya na kafa cibiyar, Idris ya tabbatar da cewa Nijeriya za ta samu amincewar ƙarshe a taron UNESCO na gaba.

 

Ya ce: “Tuni mun samu goyon bayan ƙasashe bakwai, kuma akwai ƙasashe kimanin ashirin da suka nuna shirin su na goyon bayan Nijeriya.

UNESCO

“Mun tabbatar da cewa a taron UNESCO na gaba, za a ba Nijeriya damar kafa MIL a Abuja, a Buɗaɗɗiyar Jami’ar Nijeriya (NOUN).”

 

Ministan ya bayyana farin cikin sa da sakamako mai kyau da aka samu daga tawagar masu duba shirye-shiryen, kuma ya jaddada cewa Nijeriya ta jajirce wajen cika dukkan sharuɗɗan UNESCO na kafa cibiyar.

 

Ya ƙara da cewa wannan shirin ba na Nijeriya kaɗai ba ne, har ma da Afrika da sauran duniya baƙi ɗaya.

 

Ya ce, “Cibiyar Koyar da Ilimin Yaɗa Labarai ba domin al’ummar Nijeriya kawai aka ƙirƙire ta ba, an ƙirƙire ta ne domin al’ummar duniya baki ɗaya.

 

“Wannan wata dama ce ga ƙasar mu ta nuna ƙwarewa, gogewa, da jajircewa kan Ilimin Yaɗa Labarai na duniya.”

 

Idris ya bayyana cewa Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya amince da dukkan kuɗaɗen da ake buƙata domin kafa cibiyar, kuma ya ce Ma’aikatar Yaɗa Labarai tana aiki tare da Ma’aikatar Ilimi da sauran masu ruwa da tsaki domin tabbatar da nasarar shirin.

UNESCO

Ya jaddada cewa Koyar da Ilimin Watsa Labarai yana da matuƙar muhimmanci wajen yaƙi da matsalar yaɗa labaran ƙarya wanda ke barazana ga zaman lafiya da tsaro a duniya.

 

“Yaɗa labaran ƙarya ba matsala ce da ta shafi Nijeriya ita kaɗai ba; matsala ce ta duniya baki ɗaya. Mun yaba da ƙoƙarin da UNESCO ke yi wajen yaƙi da wannan matsalar,” inji Idris.

 

Da yake kira da a haɗa kai a faɗin duniya domin shawo kan wannan matsalar, ministan ya ƙara da cewa yaƙi da baza labaran ƙarya ba yana nufin tauye ’yancin ’yan jarida ne ba.

 

Ya ce: “Domin al’umma ta kasance ’yantacciya kuma dimokiraɗiyya ta bunƙasa, ’yancin ’yan jarida yana da matuƙar muhimmanci. Amma domin samun wannan ’yanci, dole ne mu ɗauki nauyin da ke tare da shi. Ba za ka yi amfani da ’yancin ka wajen tauye haƙƙin wani ba.”

 

A nasa ɓangaren, Mista Nelson Papi Kolliesuah, Babban Manajan Ayyuka na Data-Pop Alliance, wato kamfanin da UNESCO ta ɗauka don tantance shirin da Nijeriya ke yi na kafa cibiyar, ya yaba da ƙoƙarin gwamnatin ƙasar.

 

Ya ce sun zo Nijeriya ne domin tabbatar da cewa an cika sharuɗɗan dukkan kayan aiki, ƙarfin aiki, da tsarin gudanarwa da ake buƙata domin kafa cibiyar.

 

Ya ƙara da cewa sun gamsu da shirye-shiryen da gwamnatin Nijeriya ta yi, inda ya ce cibiyar ta dace da muradun duniya, tsarin ilimi na Nijeriya, da kuma Muradun Cigaba Masu Ɗorewa na Majalisar Ɗinkin Duniya (MDGs).


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

An Wallafa Littafin Tunanin Xi Jinping A Kan Wayewar Kai Game Da Kiyaye Lafiyar Muhalli

Next Post

Binciken CGTN Ya Nuna Damuwa Daga Sassan Kasa Da Kasa Game Da Yawaitar Ficewar Amurka Daga Yarjeniyoyin Kasa Da Kasa

Related

Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

3 hours ago
An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano
Labarai

An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

4 hours ago
Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta
Labarai

Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta

6 hours ago
Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin

6 hours ago
EFCC Ta Gargaɗi Ƴan Nijeriya Kan Ɓullar Sabbin Hanyoyin Damfarar Kuɗi
Labarai

EFCC Ta Gargaɗi Ƴan Nijeriya Kan Ɓullar Sabbin Hanyoyin Damfarar Kuɗi

7 hours ago
Dangote Ya Yaba Wa Tinubu Kan Samar Da Ababen More Rayuwa A Nijeriya
Labarai

Dangote Ya Yaba Wa Tinubu Kan Samar Da Ababen More Rayuwa A Nijeriya

10 hours ago
Next Post
Binciken CGTN Ya Nuna Damuwa Daga Sassan Kasa Da Kasa Game Da Yawaitar Ficewar Amurka Daga Yarjeniyoyin Kasa Da Kasa

Binciken CGTN Ya Nuna Damuwa Daga Sassan Kasa Da Kasa Game Da Yawaitar Ficewar Amurka Daga Yarjeniyoyin Kasa Da Kasa

LABARAI MASU NASABA

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

July 10, 2025
Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

July 10, 2025
Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

July 10, 2025
Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

July 10, 2025
Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori

Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori

July 10, 2025
An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

July 10, 2025
Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adam

Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adam

July 10, 2025
Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta

Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta

July 10, 2025
An Bude Taron Ministoci Kan Wayewar Kai A Birnin Beijing

An Bude Taron Ministoci Kan Wayewar Kai A Birnin Beijing

July 10, 2025
Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin

Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin

July 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.