ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 26, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Binciken CGTN Ya Nuna Damuwa Daga Sassan Kasa Da Kasa Game Da Yawaitar Ficewar Amurka Daga Yarjeniyoyin Kasa Da Kasa

by CGTN Hausa and Sulaiman
1 year ago
Cgtn

Sabuwar gwamnatin Amurka, ta yi amfani da kwanakinta na farko a kan karaga wajen zartar da jerin umarnin shugaban kasa, inda ta sanar da ficewar Amurka daga yarjejeniyar sauyin yanayi ta Paris, da hukumar lafiya ta duniya WHO, wanda hakan ya haifar da damuwa tsakanin sassan kasa da kasa. 

Wani binciken jin ra’ayin jama’a da kafar CGTN ta kasar Sin ta gudanar, ya nuna cewa, manufar nan ta “Sanya Amurka gaban komai”, ba za ta kai kasar zuwa ga sabon “Lokacin cimma Nasarori” ba, kuma hakan zai iya kara haifar da koma baya ga tsarin gudanar da duniya.

  • Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Inganta Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa A Taron Davos
  • Kwangilar Tashar Wutar Mambila: Obasanjo Zai Bayar Da Shaida A Kotun Paris Yau

Alkaluman sun nuna cewa, kaso 68.5 bisa dari na masu bayyana ra’ayin na ganin janyewar da sabuwar gwamnatin Amurka ta sanar daga yarjejeniyar Paris, da ficewa daga hukumar kiwon lafiya ta duniya WHO, zai gurgunta hadin gwiwar kasa da kasa, a fannin shawo kan sauyin yanayi, da harkokin kula da lafiyar al’umma. Kaza lika, kaso 77.7 bisa dari na masu bayyana ra’ayoyinsu sun yi matukar damuwa, cewa akwai yiwuwar matakin ya haifar da wani mummunan misali tsakanin kasashen duniya.

ADVERTISEMENT

Alal hakika, har kullum Amurka na kallon hukumomin kasa da kasa, da cibiyoyi, da tsare-tsaren gudanar da harkokin duniya ta wata mahanga maras dacewa, da kuma idon kare moriyar kashin kai, tana kallon su a matsayin wasu abubuwa na cimma nasara, da tabbatar da manufarta ta danniya a duniya.

Karkashin manufar “Sanya Amurka gaban komai”, sabuwar gwamnatin kasar na kokarin matsawa hukumomin kasa da kasa lamba, ta yadda dole za su yi biyayya ga Amurka kan batutuwa irin su kafa dokoki, da yadda za a gudanar da cibiyoyi da jagorancin sauye-sauye, ta hanyar janyewa daga yarjeniyoyin kasa da kasa, da ma wasu hukumomin na kasa da kasa.

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Bankado Laifukan Miyagun Kwayoyi 12,000 A Watanni Biyar Na Farkon Bana

Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

Bugu da kari, binciken na jin ra’ayin jama’a ya nuna cewa, kaso 81.6 bisa dari na masu bayyana ra’ayoyinsu, na ganin Amurka na kokarin cimma burikan kashin kai ne, ko da kuwa sauran sassan kasa da kasa za su yi hasara, wanda hakan zai yi matukar illata tsarin gaskiya da adalci a fannin jagorancin harkokin duniya, da halastattun moriyar sauran kasashen duniya.

An dora damar bayyana ra’ayoyin ne kan dandalolin kafar CGTN na Turanci, da Faransanci, da Larabci da yaren Sifaniya da na Rasha, inda masu bayyana ra’ayi sama da 7,452 suka kada kuri’unsu cikin sa’o’i 24. (Saminu Alhassan)

Cgtn
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Bankado Laifukan Miyagun Kwayoyi 12,000 A Watanni Biyar Na Farkon Bana
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina
Cgtn
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Buƙatar Mayar Da Hankali Wajen Kawo Ƙarshen Ciwon Sikila A Nijeriya
  • Sulaiman
    Sin Ta Bankado Laifukan Miyagun Kwayoyi 12,000 A Watanni Biyar Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    Ƙa’idojin Gudanar Da Biyan Kuɗi Nan Take Domin Kare Kai Daga Zamba
  • Sulaiman
    Falalar Yawaita Tuba Ga Ubangiji (Istigfari)

MASU ALAKA

Sin Ta Bankado Laifukan Miyagun Kwayoyi 12,000 A Watanni Biyar Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Sin Ta Bankado Laifukan Miyagun Kwayoyi 12,000 A Watanni Biyar Na Farkon Bana

June 26, 2026
Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci
Daga Birnin Sin

Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

June 25, 2026
Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji
Daga Birnin Sin

Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

June 25, 2026
Next Post
Amurka Ta Manta Da Nauyin Dake Wuyanta Ganin Yadda Ta Janye Daga Yarjejeniyar Sauyin Yanayi Ta Paris

Amurka Ta Manta Da Nauyin Dake Wuyanta Ganin Yadda Ta Janye Daga Yarjejeniyar Sauyin Yanayi Ta Paris

LABARAI MASU NASABA

sikila

Buƙatar Mayar Da Hankali Wajen Kawo Ƙarshen Ciwon Sikila A Nijeriya

June 26, 2026
Sin Ta Bankado Laifukan Miyagun Kwayoyi 12,000 A Watanni Biyar Na Farkon Bana

Sin Ta Bankado Laifukan Miyagun Kwayoyi 12,000 A Watanni Biyar Na Farkon Bana

June 26, 2026
makarfi

Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi

June 26, 2026
Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni

An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027

June 26, 2026
Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji

Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji

June 26, 2026
Kotu Ta Soke Rajistar Jam’iyyar NDC A Matsayin Jam’iyyar Siyasa

Kotu Ta Soke Rajistar Jam’iyyar NDC A Matsayin Jam’iyyar Siyasa

June 26, 2026
An Kashe Mutane Da Dama Da Kone Gidajensu A Wani Hari Da Aka Kai Benuwai

Yadda Rikice-rikice Ke Ƙara Ta’azzara Talauci A Arewacin Nijeriya —Rahoto

June 26, 2026
Za A Sake Nazarin Mafi Ƙarancin Albashi A Nijeriya – Gbajabiamila

Za A Sake Nazarin Mafi Ƙarancin Albashi A Nijeriya – Gbajabiamila

June 26, 2026
Sowore Ya Sha Alwashin Ci Gaba Da Gwagwarmaya Duk Da Tsare Shi A Gidan Yarin Kuje

Jagoran Matasan AAC Kwamret Yahaya Soje Ya Nemi A Saki Sowore

June 26, 2026
Har Yanzu Ba Mu Karɓi Kuɗaɗen Da Aka Ware Mana Na Zaɓukan 2027 Ba – INEC

Har Yanzu Ba Mu Karɓi Kuɗaɗen Da Aka Ware Mana Na Zaɓukan 2027 Ba – INEC

June 26, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.