• English
  • Business News
Monday, June 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ƙoƙarin Ƙungiyoyin Afrika A Gasar Kofin Duniya

by Abba Ibrahim Wada
2 days ago
in Wasanni
0
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gasar cin Kofin Duniya ta kungiyoyi ko kuma FIFA Club World Cup da a yanzu ake gudanarwa a kasar Amurka za ta bai wa tawagogin Afirka hudu da za su buga gasar karin damar bajakolin ‘yan wasan Afirka da kuma irin yadda kasashen na Afirka suke kokarin ganin sun fara goga kafada da kafada da manyan kungiyoyi a nahiyar Turai da kuma kudancin Amurka.

Kungiyar Al Ahly ta Masar da ta lashe kofin Champions League na Afirka sau 12, da Mamelodi Sundowns ta Afirka ta Kudu, da Wydad Casablanca ta Morocco, da Esperance ta Tunisia, su ne za su nemi murkushe takwarorinsu na Turai da sauran nahiyoyin duniya da a yanzu suke fafatawa a gasar da hukumar kwallon kafa ta duniya FIFA ta shirya a karon farko.

  • Su Waye ‘Yan Afirka Da Suka Canja Kungiya A Turai?
  • Anya Nahiyar Afirka Fili Ne Na Gudanar Da Takara?

Babu wata kungiya daga Afirka da ta taba lashe kofin gasar ta Club World Cup a tarihi, inda biyu ne kawai suka taba kai wa wasan karshe a karo 20 na gasar. Amma yanzu akwai ladan da za a samu – jimillar abin da za a bayar ya kai Dala biliyan daya, inda aka ware Dala miliyan 475 don bai wa wadanda suka fi kokari. Duk da cewa FIFA ta kara yawan wasannin da aka saba bugawa duk da yawan wasannin da ke gaban kungiyoyi, kocin Esperance Maher Kanzari ya ce “dama ce” ga ‘yanwasa su bayyana kansu.

Duka kungiyoyin Afirka da za su buga gasar ta Kofin Duniya za su samu ladan akalla Dala miliyan 9.55 – irin wadannan wakilai daga Asiya da Arewacin Amurka da Amurka ta Tsakiya za su samu. Wannan adadi ya ninka Dala miliyan hudu da Palmiras ta samu bayan lashe kofin zakarun nahiyar Afirka.

Duk da haka, ladan da kungiyoyin Afirka za su samu shi ne mafi kankanta. Wakilan Kudancin Amurka shida za su samu ladan Dala miliyan 15.21, yayin da kungiyoyin Turai 12 za su samu kudi daga Dala miliyan 12.81 zuwa 38.19.

Labarai Masu Nasaba

An Sauya Sunan Makarantar Wasanni Don Girmama Ƴan Kano Da Suka Yi Hatsari

Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

Nasarar da kungiya ta samu a matakin rukuni za a ba ta Dala miliyan biyu, canjaras kuma miliyan daya, wadda ta cinye kofin kuma za ta samu ladan Dala miliyan 40. Ganin yadda kungiyoyin Turai suka mamaye gasar, Afirka na fatan samun karin dama a nan gaba, ma’ana a Karara nahiyar Afirka yawan kungiyoyin da za su dinga wakiltar ta.

Wasu na fatan kungiyoyin Afirka da ke cikin gasar za su ja hankalin duniya zuwa nahiyar ko da kuwa gasarta ta zakaru ba ta iya yin hakan ba, da kuma kawo musu kudi idan aka kwatanta da takwarorinsu.

Sabuwar gasar African Footbal League da hukumar CAF ta kaddamar a 2023 ba a sake yin ta ba, duk da irin rigingimun da aka yi lokacin da aka fara ta, mai tawaga hudu wadda kungiyar Sundowns ta lashe.

Kungiyar Pretoria da shugaban hukumar kwallon kafa ta Afirka CAF, Patrice Motsepe ya mallaka, ta kafa kanta a matsayin jagora a harkar kwallon kafar Afirka – ita ta lashe kofunan gasar Afirka ta Kudu tara na baya-bayan nan.

Sundowns za su kara da Ulsan HD da Borussia Dortmund da Fluminense a Rukunin F, abin da wani magoyi kwallon kafa ya ce zai taimaka wajen nasararta a gasar ta Club World Cup.

Lokacin gudanar da gasar Club World Cup ya shafi harkokin wasa a Afirka, ta yadda sai da aka matsar da lokacin gudanar da gasar Kofin kasashen Afirka wato AFCON 2025 daga watannin Yuni da Yuli zuwa karshen shekarar ta 2025. Tuni kungiyar kwararrun ‘yankwallo ta duniya ta shigar da kara a shekarar da ta gabata kan abin da suka kira “nuna karfin iko” da FIFA ta yi wajen fadada gasar, amma kuma duk da haka ba a dakata ba.

Danwasan Nijeriya na AC Milan Samuel Chikwueze ya ce kungiyarsa ba za ta buga gasar ba, amma duk da haka yawan wasannin da za su buga sun yi yawa. ‘Yan wasan dai sun yi korafin cewa lokaci daya da ‘yanwasa za su huta shi ne daidai lokacin da suka saka gasar. ‘Yan wasan sun bayyana cewa abu ne mai wahala buga wasanni masu yawa domin mutum zai gajiyar da kafufuwansa da tunaninsa ta yadda ma ba zai ji dadin buga wasan ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AfrikaDuniyaƘwallon Ƙafa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

Next Post

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

Related

An Sauya Sunan Makarantar Wasanni Don Girmama Ƴan Kano Da Suka Yi Hatsari
Wasanni

An Sauya Sunan Makarantar Wasanni Don Girmama Ƴan Kano Da Suka Yi Hatsari

9 hours ago
Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa
Wasanni

Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

14 hours ago
Wace Nahiya Ce Ta Fi Iya Ƙwallon Ƙafa Tsakanin Turai Da Kudancin Amurka?
Wasanni

Wace Nahiya Ce Ta Fi Iya Ƙwallon Ƙafa Tsakanin Turai Da Kudancin Amurka?

2 days ago
Cristiano Ronaldo Na Shirin Tsawaita Kwantiraginsa A Kungiyar Al-Nassr
Wasanni

Cristiano Ronaldo Na Shirin Tsawaita Kwantiraginsa A Kungiyar Al-Nassr

4 days ago
Manchester United Da Everton Na Zawarcin Wilfred Ndidi
Wasanni

Manchester United Da Everton Na Zawarcin Wilfred Ndidi

5 days ago
Manchester United Za Ta Biya Fam Miliyan 60 Don Ɗaukar Mbeumo Daga Brentford
Wasanni

Manchester United Za Ta Biya Fam Miliyan 60 Don Ɗaukar Mbeumo Daga Brentford

6 days ago
Next Post
Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya -  Shugaban ƘasaTinubu

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

June 29, 2025
Sharrin Ƴan Adawa Ne, Gwamnati Ta Ƙaryata Labarin Cire SGF Akume 

Sharrin Ƴan Adawa Ne, Gwamnati Ta Ƙaryata Labarin Cire SGF Akume 

June 29, 2025
An Sauya Sunan Makarantar Wasanni Don Girmama Ƴan Kano Da Suka Yi Hatsari

An Sauya Sunan Makarantar Wasanni Don Girmama Ƴan Kano Da Suka Yi Hatsari

June 29, 2025
Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

June 29, 2025
Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar

Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar

June 29, 2025
Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

June 29, 2025
2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu

2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu

June 29, 2025
Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya

Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya

June 29, 2025
Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

June 29, 2025
Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila

Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila

June 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.