• English
  • Business News
Monday, November 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ƴan Bindiga Sun Ƙone Gidaje Da Motoci, Sun Sace Mutane 50 A Katsina

by El-Zaharadeen Umar
1 year ago
Bindiga

Rahotanni daga garin Maidabino a ƙaramar hukumar Ɗanmusa da ke jihar Katsina sun bayyana cewa ‘yan bindiga sun kai mummunan harin wuce gona da iri tare da kashe mutum tara.

A daren jiya Asabar ne dai ‘yan bindiga ɗauke da muggan makamai suka dira ƙauyen Maidabino da misalin karfe 7:00 na dare har zuwa 2:30 suna barna da ta’asa.

  • Atiku Ya Ziyarci Buhari Da Sarkin Daura Da Kuma Sarkin Katsina
  • Tsaro: Gwamnoni Arewa Maso Yamma Za Su Yi Taro Domin Neman Mafita A Katsina

Kazalika maharan sun ƙone motoci guda 9 da gidaje guda huɗu sannan sun ɗauke mutane fiye da hamsin duk a cikin daren.

Majiyar Leadership Hausa ta tabbatar da cewa an ƙone fiye da shaguna 15 ciki harda shagon sayar da magunguna a cikin garin Maidabino a yayin kai wannan hari na ƙare dangi.

Ado Gambo Maidabino na ɗaya daga cikin waɗanda aka konewa shagon sayar da magunguna wato ƙyamis a garin kuma ya bayyana takaicinsa gane da wannan hari.

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kai Samame Maboyar ‘Yan Ta’adda, Sun Kwato Miyagun Kwayoyi A Gombe

Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Yana mai roko Allah ya kawo ƙarshen wannan bala’i tare da fatan Allah ya maida masu da abin da suka rasa.

Wani daga cikin ta'asar da ƴan bindigar suka yi.
Wani daga cikin ta’asar da ƴan bindigar suka yi.

Ɗan majalisa mai wakiltar ƙaramar hukumar Ɗan Musa a majalisar dokokin jihar Katsina Aminu Sai Baba ya tabbatar da faruwar wannan lamari tare da yin Allah dai da kuma kira ga gwamnati ta kawo ɗauki na gaggawa.

Ya kuma ƙara da cewa tuni gwamanti ta amsa kiran su inda yanzu haka an riga an kai jami’an tsaro wannan yanki domin dawowa da zaman lafiya.

Idan za a iya tunawa yankin Ɗan Musa na ɗaya daga cikin ƙananan hukumomin da ke fuskantar hare-haren ‘yan bindiga ba dare ba rana.

A gobe litanin ne shugaban ƙasa Bola Ahmad Tunibu zai buɗe wani taro akan harkar tsaro da gwamnonin arewa maso yamma da hukumar UNDP suka shirya a Katsina domin shawo kan matsalar tsaro a yankin.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas
Tsaro

‘Yansanda Sun Kai Samame Maboyar ‘Yan Ta’adda, Sun Kwato Miyagun Kwayoyi A Gombe

October 18, 2025
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja
Tsaro

Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

October 18, 2025
Sojoji Sun Kashe Kwamandan IPOB ‘Alhaji’, Da Wasu 26, Sun Kama 22
Tsaro

Sojoji Sun Kashe Kwamandan IPOB ‘Alhaji’, Da Wasu 26, Sun Kama 22

October 12, 2025
Next Post
Sin Da EU Sun Amince Da Tattaunawa Kan Yadda EU Take Binciken Kin Ba Da Tallafi Kan EVs Na Kasar Sin

Sin Da EU Sun Amince Da Tattaunawa Kan Yadda EU Take Binciken Kin Ba Da Tallafi Kan EVs Na Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Da Dumi-duminsa: ‘Yan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Basarake A Ondo

Wani Sabon Hari Kan Al’ummar Da Ke Iyaka Da Katsina A Kano Ya Rutsa Da Mata 5

November 10, 2025
Matatun mai

Yadda Sojoji Suka Tarwatsa Haramtattun Matatun Mai 14 A Yankin Neja Delta 

November 10, 2025
Jibrin Kofa

Ɗan Majalisar Wakilai, Jibrin Ƙofa Ya Sauya Sheƙa Daga NNPP Zuwa APC

November 10, 2025
Boko haram

Sojoji Sun Fatattaki Boko Haram, Sun Ceto Mutane 86 Da Aka Sace A Borno

November 10, 2025
Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Ci Gaba Da Zama Muhimmin Ginshiki Ga Ci Gaban Nahiyar 

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Ci Gaba Da Zama Muhimmin Ginshiki Ga Ci Gaban Nahiyar 

November 9, 2025
An Rufe Taron Kolin Wuzhen Na Ayyukan Yanar Gizo Na Duniya Na Shekarar 2025

An Rufe Taron Kolin Wuzhen Na Ayyukan Yanar Gizo Na Duniya Na Shekarar 2025

November 9, 2025
Katsina United Ta Shiga Komar Hukuncin Hukumar NPFL

Katsina United Ta Shiga Komar Hukuncin Hukumar NPFL

November 9, 2025
Xi Ya Gana Da Shugabar IOC Tare Da Shugaban IOC Na Karramawa

Xi Ya Gana Da Shugabar IOC Tare Da Shugaban IOC Na Karramawa

November 9, 2025
CMG Ya Cimma Yarjejeniyar Samun Iznin Watsa Shirye-shiryen Wasannin Olympics Daga Shekarar 2026 Zuwa 2032

CMG Ya Cimma Yarjejeniyar Samun Iznin Watsa Shirye-shiryen Wasannin Olympics Daga Shekarar 2026 Zuwa 2032

November 9, 2025
Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Na Gwaji

Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Na Gwaji

November 9, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.