ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yansanda Sun Kai Samame Maboyar ‘Yan Ta’adda, Sun Kwato Miyagun Kwayoyi A Gombe

by Sulaiman and Rabi'u Ali Indabawa
8 months ago
Yansanda

Rundunar ‘Yansandan Jihar Gombe ta bayyana cewa ta kwato tarin miyagun kwayoyi bayan wata nasarar samame da ta kai a maboyar ‘yan ta’adda da ake zargi, da ke bayan wani katafaren kanti na ‘Gombe Local Government Shopping Complex’.

 

Wannan bayani ya fito a cikin wata sanarwa da Jami’in Hulda da Jama’a na ‘yansanda, DSP Buhari Abdullahi, ya sanya hannu a kai.

ADVERTISEMENT
  • Gwamnatin Jihar Taraba Ta Ayyana Yi Wa Kasuwannin Sayar Da Dabbobi 9 Garanbawul
  • JIBWIS FCT Ta Yi Taron Yaye Iyaye Mata Da Suka Kammala Koyon Sana’o’i

Abdullahi ya ce an gudanar da samamen ne ta hannun jami’an ‘yansanda na sashen Gombe yayin wani aikin yau da kullum na fatattakar wuraren da aka tabbatar da ayyukan laifi a yankin.

 

LABARAI MASU NASABA

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2, Sun Yi Garkuwa Da 30 A Kogi

NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano

Ya bayyana cewa a ‘yan watannin da suka gabata, rundunar ta kara kaimi wajen kai samame a wuraren da ake zargin yin laifuka a fadin jihar, a wani bangare na kokarinta na rage yawan shan miyagun kwayoyi da laifukan da suka shafi hakan, wadanda hukumomi ke cewa sau da dama su kan zama sanadin tashin hankali da aikata laifuka musamman tsakanin matasa.

 

“Lokacin da barayin suka hango tawagar sintiri na kusantowa, sai suka tsere, suka bar tarin miyagun kwayoyi da wasu haramtattun abubuwa a wurin,” in ji Abdullahi.

 

Mai magana da yawun rundunar ya lissafa abubuwan da aka kwato da suka hada da kwayoyin “Suck and Die,” Tramadol da Diazepam, inda ya ce an kwashe su gaba daya zuwa ofishin ‘yansanda domin ci gaba da bincike da daukar matakan da suka dace.

 

“Dukkan shaidun da aka kwato an tafi da su ofishin ‘yansanda, kuma bincike na ci gaba domin gano da kama wadanda suka tsere,” in ji shi.

 

Kwamishinan ‘yansanda, CP Bello Yahaya, ya yaba wa jami’an da suka gudanar da samamen bisa gaggawa da kwarewa, tare da tabbatar da cewa rundunar za ta ci gaba da jajircewa wajen yaki da laifuka da shan miyagun kwayoyi a Jihar Gombe.

 

“Rundunar ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen tabbatar da cewa Gombe ta kasance jiha marar laifi da kuma marar miyagun kwayoyi,” in ji shi.

 

“Muna aikawa da gargadi mai karfi ga duk masu aikata laifuka da su daina duk wani nau’i na aikata laifi ko kuma su fuskanci fushin doka,” in ji CP Yahaya.

 

Ya kuma roki jama’a da su ci gaba da bin doka da oda tare da taimaka wa ‘yansanda da sahihan bayanai da za su taimaka wajen tabbatar da zaman lafiya da tsaro.

 

“Muna kira ga al’umma da su rika sanar da ofishin ‘yansanda mafi kusa idan sun ga wani motsi ko aiki da suke shakka domin a dauki mataki cikin gaggawa,” in ji sanarwar.

 

A watan Afrilu, Rundunar ‘Yansandan Jihar Ogun ta gudanar da aikin tsaro na tsawon sa’o’i biyu a Sagamu Interchange bayan samun rahoton wani harin ‘yan fashi da ya yi sanadiyyar mutuwar mutum a kan hanyar Lagos–Ibadan Expressway.

 

A cewar rundunar, kwamishinan ‘yan sanda Lanre Ogunlowo ne ya jagoranci duba wurin, inda aka gano haramtattun kasuwanin, ‘yan daba da kuma maboyar ‘yan ta’adda a cikin dazukan da ke kusa da wurin.

 

A lokacin aikin tsaron, an kama mutum uku da ake zargi, sannan kuma an kara tsaurara sintiri a yankin domin hana sake kai irin wannan hari a nan gaba.

Yansanda
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • Sulaiman
    Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
  • Sulaiman
    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
Yansanda
Rabi'u Ali Indabawa
+ posts Bio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƴansanda Su Ƙi Karɓar Cin Hancin Naira Miliyan 500 Daga Hannun Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya

MASU ALAKA

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2, Sun Yi Garkuwa Da 30 A Kogi
Tsaro

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2, Sun Yi Garkuwa Da 30 A Kogi

June 1, 2026
NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano
Tsaro

NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano

May 31, 2026
Yadda Muka Kashe Masu Garkuwa 4 Da Suke Shirin Kai Hari Kan Attajirai A Legas —CP
Tsaro

Yadda Muka Kashe Masu Garkuwa 4 Da Suke Shirin Kai Hari Kan Attajirai A Legas —CP

May 31, 2026
Next Post
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya

DHQ Ta Ƙaryata Rahoton Yunƙurin Yi Wa Tinubu Juyin Mulki

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.