• English
  • Business News
Saturday, June 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ɗaukar Malamai 7, 325: Gamayyar Kungiyoyin Farar Hula Sun Jinjina wa Gwamna Dikko Raɗɗa

by El-Zaharadeen Umar
2 years ago
in Labarai
0
Ɗaukar Malamai 7, 325: Gamayyar Kungiyoyin Farar Hula Sun Jinjina wa Gwamna Dikko Raɗɗa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gamayyar kungiyoyin farar hula a jihar Katsina sun jinjinawa ƙoƙarin gwamna Dikko Umar Raɗɗa bisa amincewa da ɗaukar malaman firamare da sakandare kimanin 7,325.

Wannan yana kunshe ne a cikin wata sanarwar da shugaban gamayyar kungiyoyin farar hula da sakatarensa a jihar Katsina, Abdulrahaman Abdullahi Dutsinma da Tukur Suke Tama suka sanya wa hannu aka rabawa manema labarai a Katsina.

  • Har Yanzu Dokar Ababen Hawa Na Aiki A Katsina —Gwamnatin Jihar
  • Ba Zan yi Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ba, Cewar Dikko Radda

Sanarwar ta ce wannan abin a raba ne ganin yadda gwamnati ta ɗauki malaman wucin gadi na S-Power da kuma ‘yan sakai na makarantun sakandare a matsayin malamai na dindindin.

“Ya zama wajibi gare mu da mu jinjinawa gwamnatin jihar Katsina ƙarƙashin jagorancin Malam Dikko Raɗɗa saboda wannan yunkuri irin sa na farko a tarihin Katsina, wanda muke da tabbacin hakan zai sauya yanayi da tsarin koyo da koyarwa a jihar baƙi ɗaya” inji shi.

Haka kuma gamayyar kungiyoyin farar hula ta nuna godiyarsa ga kwamitin da ya shirya jarabawar ɗaukar Malaman ba tare da yin wani katsalandan ba, wanda hakan ya tabbatar da ingancin aikin da kwamitin ya yi tunda babu korafe-korafe

Labarai Masu Nasaba

Sarkakiyar Da Ke Tattare Da Zaben 2027 Da Yadda Za Ta Kaya

Nijeriya Na Kan Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arziki Da Dawo Da Martabar Ƙasa — Ministan Yaɗa Labarai

Kazalika sanarwar ta ce, wani abu mai matuƙar mahimmanci akan wannan lamari shi ne, yadda aka amince da duk shawarwarin da kwamitin ya bada ga gwamna Malam Dikko Umar Raɗɗa tare da neman amincewar nada horo ga duk sabbin malaman da aka ɗauka.

Daga ƙarshe dai gamayyar kungiyoyin farar hula ta yaba da wannan kokari tare da yin kira ga gwamna Dikko Raɗɗa ya duba halin da ma’aikatan wucin gadi da ke ɓangaren hukumomin kiwon lafiya a fadin jihar Katsina.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Dikko RaddaKatsina
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasar Sin Ce Kan Gaba Wajen Yawan Manyan Jiragen Ruwa A Duniya 

Next Post

An Fitar Da Jerin Manyan Kamfanoni Masu Zaman Kansu Na Sin Guda 500 Na 2023

Related

jam'iyyu
Rahotonni

Sarkakiyar Da Ke Tattare Da Zaben 2027 Da Yadda Za Ta Kaya

9 hours ago
Nijeriya Na Kan Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arziki Da Dawo Da Martabar Ƙasa — Ministan Yaɗa Labarai
Labarai

Nijeriya Na Kan Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arziki Da Dawo Da Martabar Ƙasa — Ministan Yaɗa Labarai

9 hours ago
Nijeriya Da Morocco Za Su Sanya Hannu Kan Kulla Yarjejeniyar Aikin Bututun Iskar Gas
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Himmatu Wajen Inganta Karfin Sashen Fetur Da Gas Na Cikin Gida

11 hours ago
Gwamnati Ta Yi Karin Haske Kan Biyan Tallafin Rage Radadi Da Mafi Karancin Albashi
Labarai

Gwamnati Ta Yi Karin Haske Kan Biyan Tallafin Rage Radadi Da Mafi Karancin Albashi

13 hours ago
Dawanau
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Dukufa Wajen Karya Farashin Kayan Abinci – Minista

14 hours ago
Ƴansanda Sun Kama Shahararren Ɗan Damfarar Yanar Gizo A Bauchi
Labarai

Ƴansanda Sun Kama Shahararren Ɗan Damfarar Yanar Gizo A Bauchi

15 hours ago
Next Post
Kamfanoni

An Fitar Da Jerin Manyan Kamfanoni Masu Zaman Kansu Na Sin Guda 500 Na 2023

LABARAI MASU NASABA

Taron Koli Na Sin Da Kasashen Yankin Tsakiyar Asiya Karo Na Biyu Zai Ingiza Manufar Kara Dunkulewar Sassan Yankin

Taron Koli Na Sin Da Kasashen Yankin Tsakiyar Asiya Karo Na Biyu Zai Ingiza Manufar Kara Dunkulewar Sassan Yankin

June 13, 2025
jam'iyyu

Sarkakiyar Da Ke Tattare Da Zaben 2027 Da Yadda Za Ta Kaya

June 13, 2025
Nijeriya Na Kan Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arziki Da Dawo Da Martabar Ƙasa — Ministan Yaɗa Labarai

Nijeriya Na Kan Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arziki Da Dawo Da Martabar Ƙasa — Ministan Yaɗa Labarai

June 13, 2025
Babban Jami’in Diflomasiyyar Kasar Sin Ya Yi Kiran Karfafa Alaka Da Afirka

Babban Jami’in Diflomasiyyar Kasar Sin Ya Yi Kiran Karfafa Alaka Da Afirka

June 13, 2025
Xi Ya Yi Kira Da A Kara Azamar Gina Kasa A Gabar Da Ake Bikin Cika Shekaru 120 Da Haihuwar Dan Mazan Jiya Chen Yun

Xi Ya Yi Kira Da A Kara Azamar Gina Kasa A Gabar Da Ake Bikin Cika Shekaru 120 Da Haihuwar Dan Mazan Jiya Chen Yun

June 13, 2025
Pogba Na Shirin Komawa Monaco Bayan Dakatar Da Shi

Pogba Na Shirin Komawa Monaco Bayan Dakatar Da Shi

June 13, 2025
Nijeriya Da Morocco Za Su Sanya Hannu Kan Kulla Yarjejeniyar Aikin Bututun Iskar Gas

Gwamnatin Tarayya Ta Himmatu Wajen Inganta Karfin Sashen Fetur Da Gas Na Cikin Gida

June 13, 2025
Bin Hanya Daya Da Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Muhimmin Mataki Ne Na Ba Da Tabbaci Ga Huldar Ciniki Da Tattalin Arzikin Sin Da Amurka

Bin Hanya Daya Da Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Muhimmin Mataki Ne Na Ba Da Tabbaci Ga Huldar Ciniki Da Tattalin Arzikin Sin Da Amurka

June 13, 2025
Sin Ta Bayyana Adawa Da Keta Hurumin ‘Yanci Tsaro Da Ikon Mulkin Yankunan Iran

Sin Ta Bayyana Adawa Da Keta Hurumin ‘Yanci Tsaro Da Ikon Mulkin Yankunan Iran

June 13, 2025
Gwamnati Ta Yi Karin Haske Kan Biyan Tallafin Rage Radadi Da Mafi Karancin Albashi

Gwamnati Ta Yi Karin Haske Kan Biyan Tallafin Rage Radadi Da Mafi Karancin Albashi

June 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.