• English
  • Business News
Tuesday, October 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ƙungiyar Fulani Makiyaya Ta Nuna Damuwarta Na Ɓacewar Mataimakin Shugabanta

by Shehu Yahaya
5 months ago
Fulani

Ƙungiyar Fulani Makiyaya ta kasa (MACBAN) ta nuna nuna damuwarta dangane rashin sanin halin da mataimakin shugaban kungiyar na kasa, Injiniya Mannir Atiku Lamido, tsawon shekaru biyu babu labarinsa.

A wani taron manema labarai a Kaduna, wanda sakataren kungiyar Alhaji Bello Aliyu Gotomo, ya yi ya bayyana rashin gamsuwarsu da irin matakin da jami’an tsaro suke dauka wajen gano halin da mataimakin shugaban nasu yake ciki duk da cewa suna ikirarin yin bakin kokarinsu.

  • Lokaci Ya Yi Da Za A Kawo Karshen Musguna Wa Fulani – Dakta Awwal 
  • Kungiyar Fulani Ta MACBAN Ta Nesanta Kanta Daga Zanga-zangar Matasa

Haka zalika, ya bayyana danuwarsu dangane da yadda matsalar rashin tsaro take kara ta’azzara a jihohin Arewacin kasar nan, musamman jihohin Adamawa da Borno da Nija da Katsina da dai sauransu, inda ya ce akwai bukatar hukumomin tsaro su kara zage damtse wajen kawo saukin lamarin.

Ya ci gaba da cewa, “Jami’an tsaro sun shaida mana cewa suna bakin kokarinsu wajen gano halin da Injiya Manir Atiku yake ciki, amma abin da ya ba mu tsoro da shakku shi ne, sun ce sun yi kokarin bibiyar lambar wayarsa domin gano inda yake amma abin da bai yiwuba saboda a cewarsu, an goge komai a wayarsa wanda babu wata hanya da za a iya gano inda yake ta hanyar bibiyar wayarsa. Sun ce a yanzu babu wani bayani da za a iya samu dangane da batar nasa.

“Muna kira ga gwamnatin tarayya da hukumomin tsaro da su taimaka mana su gano halin da dan uwanmu yake ciki, yau shekaru biyu kenan babu labarinsa.”

LABARAI MASU NASABA

Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Kasar Sin Na Saurin Bunkasa

Mutane 3,433 Sun Rasu a Hatsarin Mota 6,858 Cikin Wata 9 A Nijeriya – FRSC

Mataimakin shugaban kungiyar MACBAN ta kasa ya bace ne a ranar 20 ga watan Yuni na shekarar 2023 a garin Zariya, inda aka tsinci motarsa a bakin hanya a bude, lamarin da haifar da fargaba da jimami, wanda har yanzu babu wani bayani dangane da halin da yake ciki.

Sai dai sakataran ya bayyana jin dadinsu bisa samar da ma’aikatar bunkasa harkokin Fulani da Shugaban kasa Bola Tinubu ya yi.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Kasar Sin Na Saurin Bunkasa
Ra'ayi Riga

Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Kasar Sin Na Saurin Bunkasa

October 21, 2025
Mutane 3,433 Sun Rasu a Hatsarin Mota 6,858 Cikin Wata 9 A Nijeriya – FRSC
Labarai

Mutane 3,433 Sun Rasu a Hatsarin Mota 6,858 Cikin Wata 9 A Nijeriya – FRSC

October 21, 2025
NLC Ta Bai Wa Gwamnatin Tarayya Wa’adin Mako 4 Don Biyan Buƙatun ASUU Da Sauran Ƙungiyoyi 
Manyan Labarai

NLC Ta Bai Wa Gwamnatin Tarayya Wa’adin Mako 4 Don Biyan Buƙatun ASUU Da Sauran Ƙungiyoyi 

October 21, 2025
Next Post
Dalilin Ƴansandan Kano Na Tsare Wasu Awaki

Dalilin Ƴansandan Kano Na Tsare Wasu Awaki

LABARAI MASU NASABA

Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Kasar Sin Na Saurin Bunkasa

Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Kasar Sin Na Saurin Bunkasa

October 21, 2025
Mutane 3,433 Sun Rasu a Hatsarin Mota 6,858 Cikin Wata 9 A Nijeriya – FRSC

Mutane 3,433 Sun Rasu a Hatsarin Mota 6,858 Cikin Wata 9 A Nijeriya – FRSC

October 21, 2025
NLC Ta Bai Wa Gwamnatin Tarayya Wa’adin Mako 4 Don Biyan Buƙatun ASUU Da Sauran Ƙungiyoyi 

NLC Ta Bai Wa Gwamnatin Tarayya Wa’adin Mako 4 Don Biyan Buƙatun ASUU Da Sauran Ƙungiyoyi 

October 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Ɗan Fashi Sanye Da Kayan NYSC A Enugu

October 21, 2025
Gwamnatin Gombe Ta Ceto Yara 59 Da Aka Yi Safararsu

Gwamnatin Gombe Ta Ceto Yara 59 Da Aka Yi Safararsu

October 21, 2025
Matsayar Kasar Sin A Bayyane Take Dangane Da Batutuwan Cinikayya Da Tsagin Amurka

Matsayar Kasar Sin A Bayyane Take Dangane Da Batutuwan Cinikayya Da Tsagin Amurka

October 20, 2025
An Shiga Ruɗani A Borno Bayan Budurwa Ta Kashe Kanta Saboda Auren Dole

An Shiga Ruɗani A Borno Bayan Budurwa Ta Kashe Kanta Saboda Auren Dole

October 20, 2025
Sin Ta Kara Wasu Wurare 22 Cikin Yankunan Dausayi Masu Matukar Muhimmanci A Kasar

Sin Ta Kara Wasu Wurare 22 Cikin Yankunan Dausayi Masu Matukar Muhimmanci A Kasar

October 20, 2025
Tinubu Ya Taya Kwankwaso Murnar Ranar Haihuwa, Ya Jaddada Abotarsu

Tinubu Ya Taya Kwankwaso Murnar Ranar Haihuwa, Ya Jaddada Abotarsu

October 20, 2025
Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Tsagaita Bude Wuta Tsakanin Pakistan Da Afghanistan

Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Tsagaita Bude Wuta Tsakanin Pakistan Da Afghanistan

October 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.