ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

by Sulaiman
6 months ago
Tinubu

Tun bayan da gwamnatin Tinubu ta karɓi ragamar mulkin Nijeriya, wani abu baƙo da ke shirin zama ruwan dare, kullum kamar ƙara yawaita yake yi, wannan abu ba komai ne fa ce mu ce “U-turn”, a turance, ma’ana “naɗa muƙamai da soke su”.

 

U-turn a cikin naɗe-naɗen gwamnati yana nufin lokacin da shugaban ƙasa ya fara sanar da naɗin muƙami sannan daga baya ya janye naɗin, ko ya maye gurbin wanda aka naɗa, ko soke naɗin gaba ɗaya.

ADVERTISEMENT

 

Duk da cewa, gwamnatin tana da mafakarta kan hakan, amma da yawa suna tambaya, meke hana a duba duka abubuwan da suka dace kafin sanar da naɗin ga jama’a?

LABARAI MASU NASABA

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

 

Amma kafin muji amsar wannan daga gwamnati, bari mu fara duba hasashen manyan dalilan da ka iya janyo gwamnati ta janye naɗin muƙami bayan ta sanar da naɗin a bainar jama’a.

 

1. Ƙorafin Jama’a da Siyasa

Sau da yawa akan janye naɗe-naɗe bayan suka mai ƙarfi daga jama’a, ko masu ruwa da tsaki, ko ƙungiyoyin siyasa. Misali, an janye naɗin wani matashi mai shekaru 24 a matsayin shugaban FERMA bayan suka da aka yi masa cewa ba shi da ƙwarewar da ake buƙata, wanda hakan ya sanya shugaban ƙasa ya janye naɗin.

Hakazalika, akwai wani jerin sunayen wasu manyan mutane da aka yi yunƙurin naɗawa a matsayin jakadu, bayan shan suka a kafafen sada zumunta, dole hakan ya haifar da matsin lamba ga gwamnati ta janye sunayen don sake duba lamarin.

 

2. Matsin lamba daga ‘ya’yan Jam’iyyar Cikin Gida (mai mulki) ko daga masu ruwa da tsaki

Wani lokaci, janye naɗin na zuwa ne bayan ƙorafe-ƙorafen cikin gida ko ƙorafe-ƙorafe masu tasiri daga masu ruwa da tsaki da suka buƙaci sauye-sauye – misali, tutsun ‘ya’yan jam’iyyar APC ko masu ruwa da tsaki na jiha kan waɗanda aka naɗa a muƙamai.

A cikin sake fasalin kwamitin Hukumar Neja-delta (NDDC), an canza waɗanda aka naɗa na asali bayan tutsun da magoya bayan jam’iyyar APC na yankin suka yi.

 

3 – Rashin Jituwa da Haɗin kai a tsakanin manyan ofisoshin gwamnati wajen yanke shawara

Masu sharhi kan al’amuran dake faruwa a ƙasa, sun bayyana rashin daidaiton haɗin kai a cikin fadar shugaban ƙasa a matsayin abin da ke haifar da hakan, inda ake fitar da sanarwar naɗin muƙami kafin a kammala duk wani bincike da bayanai, wanda ke haifar da jin kunya na yin amai a lashe a babbar Fada irin ta shugaban ƙasa.

Wannan yana nuna cewa, wani lokacin ana sanar da yanke shawara kafin a samu cikakken amincewa daga sauran ofisoshin gwamnati.

 

5. Dabarun Siyasa

Wasu sauye-sauyen na iya faruwa ne sakamakon dabarun siyasa, kamar daidaita muradun yanki, kwantar da hankalin masu suka, ko hana rarrabuwar kawuna a cikin jam’iyya mai mulki.

Wannan dambarwar na nuna cewa, ra’ayin jama’a da na masu ruwa da tsaki, da tsarin jam’iyya mai mulki, da kuma dabarun siyasa na taka muhimmiyar rawa wajen naɗe-naɗe da sauye-sauyen muƙamai ko da bayan an fitar da sanarwar ne.

Ga wasu daga cikin jerin naɗe-naɗe da sauye-sauyen muƙamai a gwamnatin Shugaba Tinubu.

 

Shugaban NERC – Abdullahi Ramat

Shugaba Tinubu ya soke naɗin Abdullahi Ramat a matsayin Shugaban NERC inda ya maye gurbinsa da Oseni.

 

Zaɓaɓɓun Ministoci – Tsohon Gwamnan Kaduna, Malam Nasir elrufa’i da Maryam Shetty 

Duka su biyun an aika da sunan su don tantancewa a Majalisar Dattawa a matsayin waɗanda aka zaɓo a matsayin ministoci amma an janye sunansu inda kuma aka maye gurbinsu da wasu.

 

Karamin Ministan Ma’aikatar Gidaje da Raya Birane – Abdullahi Tijjani Muhammmad Gwarzo 

Bayan majalisar dattawa ta tantance Gwarzo a matsayin karamin Minista da zai yi aiki tare da Babban Minista Ahmed Musa Dangiwa amma watan Agustan 2023 amma a watan Oktoban 2024 aka sauke shi daga muƙaminsa.

 

Shugabannin NTA

Shugaba Tinubu ya naɗa sabbin shugabanin gudanarwar gidan Talabijin na Nijeriya (NTA) – ciki har da Rotimi Pedro a matsayin DG da sauran manyan jami’ai, amma daga baya aka soke sabbin naɗin, inda ya mayar da Salihu Abdullahi Dembos a matsayin DG da Ayo Adewuyi a matsayin Babban Daraktan Labarai.

 

Shugaban Hukumar UBEC — Idris Olorunnimbe

An naɗa Olorunnimbe a matsayin Shugaban Hukumar Ilimi Ta Bai-ɗaya (UBEC) amma daga baya aka soke naɗin, aka maye gurbinsa da Tanko Umaru Al-Makura.

 

Taƙaddamar Naɗin Jakadu. 

Bayan bayyanar sunayen wasu fitattun mutane a cikin jerin sunayen jakadun da aka yi yunƙurin naɗawa, taƙaddama ta kaure inda ta haifar da janye sunayen wasu daga ciki.

 

Muheeba Dankaka — Hukumar Halayyar Tarayya (FCC).

An sake naɗa ta a wa’adi na biyu na shekaru biyar-biyar a matsayin Shugabar FCC amma an janye naɗin bayan sa’o’i kaɗan, an maye gurbinta da Ayo Omidiran.

 

Zaɓaɓɓun Kwamishinonin Zaɓe na INEC (REC)

An sauya zaɓen Mohammed Ngoshe (Borno) da Owede Kosioma Eli (Bayelsa), inda aka maye gurbinsu da wasu.

 

Shugaban FERMA — Kashim Imam

An sanar da Kashim Imam a matsayin Shugaban Hukumar Kula da Hanyoyin Tarayya (FERMA) amma an janye naɗin cikin ‘yan kwanaki saboda cece-kuce game da ƙwarewa da shekarunsa.

 

Ruby Onwudiwe — kwamitin gudanarwar Daraktocin CBN

An zaɓe ta a matsayin mamba na kwamitin gudanarwa na Babban Bankin Nijeriya (CBN). An janye zaɓen bayan takaddamar siyasa game da jam’iyyarta.

 

Hukumar Raya Yankin Neja Delta, (NDDC)

An naɗa Asi Okang (Kuros Riba) da Victor Akinjo (Ondo) da farko a kwamitin NDDC amma an maye gurbinsu duka cikin sa’o’i 24 bayan tutsun da ‘ya’yan Jam’iyyar APC na yankin suka yi.

A irin wannan halin, ba a jima ba, fadar shugaban kasa, ta yi afuwa ga Maryam Sanda wacce ta kashe Mijinta, kuma kotu ta yanke mata hukuncin kisa amma da jama’a suka fara ƙorafi sai aka janye afuwar.

Tinubu
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana
  • Sulaiman
    Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili
  • Sulaiman
    Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa
  • Sulaiman
    Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

MASU ALAKA

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar
Manyan Labarai

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya
Rahotonni

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle
Manyan Labarai

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026
Next Post
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

LABARAI MASU NASABA

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026
Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.