• English
  • Business News
Sunday, October 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ƙungiyar Masu Sana’ar POS Za Ta Fara Aikin Taftace Sana’ar A Faɗin Kasar Nan

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
POS

Kungiyar masu aiwatar da sana’ar sanyawa da cire kudi ta kasa POS wato Association Of Point Of Sales Users In Nijeriya, za ta fara aiki gadan-gadan a cikin wannan shekara da muke ciki domin tabbatar da ganin ta inganta sana’ar wajen tsaftacewa da hana duk wani abu da iya hana ruwa gudu ga masu sana’ar.

Mai magana da yawun kungiyar nan a kasa Alhaji Maina Abdullahi ne ya sanar da haka cikin wata ganawarsu da wakilin LEADERSHIP Hausa, inda ya ce, kungiya ce da dade tana shirya ayyuka a fadin kasar nan baki daya, a cewarsa kungiya ce da aka kafa ta domin samawa matasa aiki, kuma a halin yanzu hakar kungiya ya cimma ruwa duba da irin dinbin matasa da turuwa wajen shiga sana’ar ta POS, inda a cewarsa kwalliya tana biyan kudin sabulu, don haka a shirye suke da su fara aikin tsaftace sana’ar a wannan wata da za mu shiga, duba da irin korafe-korafen da ake samu na yawan cutar mutane da wasu bata gari ke yi a sana’ar.

  • Ministan Harkokin Wajen Kasar Sin Zai Tattauna Da Mashawarcin Shugaban Amurka Kan Tsaro Yayin Ziyararsa A Thailand
  • ‘Yan Bindiga Sanye Da Hijabi Sun Kashe ‘Yan Sanda 2 A Katsina

“Kungiya ce da aka kafa ta don ta kare hakkin masu sana’ar POS tare da kwato musu hakkokin nasu da kuma tsare musu dukiyoyinsu daga masu aikata laifuka na amundahana ko abin da ya yi kama da haka idan bukatar hakan ta taso, ta yadda zai zama ana gudanar da sana’ar ba tar da an cutar da wani ba,”in ji shi.

Ya ce, a halin yanzu kungiyar na ofisoshi 811 a fadin kasar nan, tare da abokan aiki 9,360.

“Kungiyarmu ta hana kai da manyan ofisoshi na gwamnati, da suka hada da jami’an tsaro da ofisoshin hada-hadar kudi domin ganin ta kare hakkin ‘ya’yanta,” a karshe ya yi kira ga dukkan masu sana’a POS da su ci gaba rike gaskiya da amana domin taimaka wa kungiyar wajen cimma nasarar gudanar da ayyukanta.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Raba Wa Masu Ƙananan Sana’o’i Biliyan 75 Domin Bunƙasa Kasuwancinsu

Ɗan Majalisa Ya Ce Ba Zai Sake Takara Ba, Ya Sadaukar Da Ita Ga Matasa

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Raba Wa Masu Ƙananan Sana’o’i Biliyan 75 Domin Bunƙasa Kasuwancinsu

October 26, 2025
Ɗan Majalisa Ya Ce Ba Zai Sake Takara Ba, Ya Sadaukar Da Ita Ga Matasa
Labarai

Ɗan Majalisa Ya Ce Ba Zai Sake Takara Ba, Ya Sadaukar Da Ita Ga Matasa

October 26, 2025
Abin Da Ya Sa Aka Yi Watsi Da Tashar Jiragen Ruwa Ta Kan Tudu Da Ke Jihar Kaduna
Labarai

Abin Da Ya Sa Aka Yi Watsi Da Tashar Jiragen Ruwa Ta Kan Tudu Da Ke Jihar Kaduna

October 26, 2025
Next Post
Gwamnati Ta Nemi Zuba Jari A Fasahar Na’urar Hoto Da Ke Tashoshin Jiragen Ruwa

Gwamnati Ta Nemi Zuba Jari A Fasahar Na'urar Hoto Da Ke Tashoshin Jiragen Ruwa

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Raba Wa Masu Ƙananan Sana’o’i Biliyan 75 Domin Bunƙasa Kasuwancinsu

October 26, 2025
Ɗan Majalisa Ya Ce Ba Zai Sake Takara Ba, Ya Sadaukar Da Ita Ga Matasa

Ɗan Majalisa Ya Ce Ba Zai Sake Takara Ba, Ya Sadaukar Da Ita Ga Matasa

October 26, 2025
Abin Da Ya Sa Aka Yi Watsi Da Tashar Jiragen Ruwa Ta Kan Tudu Da Ke Jihar Kaduna

Abin Da Ya Sa Aka Yi Watsi Da Tashar Jiragen Ruwa Ta Kan Tudu Da Ke Jihar Kaduna

October 26, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

‘Yansanda Sun Kama Wasu Mutum Biyu Da Ake Zargi Da Haɗa Baki Da ‘Yan Bindiga A Kano

October 26, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwamnatin Kaduna Tare Da  AUDA–NEPAD Sun Tallafa Wa Manoma 400 Da Kayan Noma

October 26, 2025
Tornadoes Ta Doke Pillars A Wasan Farko Na Babaganaru

Tornadoes Ta Doke Pillars A Wasan Farko Na Babaganaru

October 26, 2025
Gwarzon Kamfanin Samar Da Kayayyakin Gida Na Mai Da Gas Na Shekarar 2025 Kamfanin GEIL

Gwarzon Kamfanin Samar Da Kayayyakin Gida Na Mai Da Gas Na Shekarar 2025 Kamfanin GEIL

October 26, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwarzon Ɗan Majalisa Na Shekarar 2025: Benjamin Okezie Kalu

October 26, 2025
An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

October 25, 2025

Nafisa Abdullahi Aminu: Yarinyar Da Ta Ɗaukaka Darajar Nijeriya A Idon Duniya

October 25, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.