• English
  • Business News
Wednesday, July 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnati Ta Nemi Zuba Jari A Fasahar Na’urar Hoto Da Ke Tashoshin Jiragen Ruwa

by Khalid Idris Doya
1 year ago
in Kimiyya Da Fasahar Sadarwa
0
Gwamnati Ta Nemi Zuba Jari A Fasahar Na’urar Hoto Da Ke Tashoshin Jiragen Ruwa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin tarayya ta bukaci kamfanoni masu zaman kansu da su zuba jari a bangaren fasahar na’urar daukar hoto ta (Scanning) a tashoshin jiragen ruwan Nijeriya domin dorewar amfani da ita da kuma bunkasa amfani da zamani a harkokin safarar jiragen ruwa a kasar nan.

Wannan bukatar ta fito ne a wajen ganawar bullo da dabarun hanyoyin da za a inganta jiragen ruwa da samar da tsarin kara samar da kudaden shiga da aka  yi a gudana a Abuja, wanda ya samu halartar ministan kula da teku da albarkatun cikin teko Gboyega Oyetola; ministan sufuri, Said Ahmed Alkali; kwanturola-janar na hukumar hana fasa kwabri wato Kwastam, Bashir Adewale Adeniyi da kuma darakta janar na hukumar kula da layukan dogo na Nijeriya (NRC), Fidet Okhiria.

  • Kasashen Afirka 10 Da Za Su Samu Bunkasar Tattalin Arziki A 2024
  • Bukatar Samar Da Tsaftatacciyar Adawa A Nijeriya

A wani mataki na inganta ayyukan jiragen ruwa a tashoshin jiragen ruwa da kuma ganin sun yi gogayya da takwarorinsu, ministoci da shugaban kwastam din sun amince kan cewar dole ne a samar da matakin duba jiragen ruwa na zahiri a filayen jiragen ruwa da samar da hadin guiwa da saukaka aiki domin kyautata kasuwanci.

Kudurin na kunshe ta cikin sanar hadin guiwa da kakakin ministan da kula da albarkatun tekuna, Ismail Omipidan da na kwastam spokesman, Abdullahi Maiwada.

Ministocin sun bayyana muhimmancin amfanin na’urar kimiyya ta dubawa da tantancewa wato (NIIT) wajen rage cinkoso a filayen jirage, kuma bai wa shugaban kwastam ikon tantancewa kayan da jirgin ruwa ya dauko cikin sauki da hanzari ta hanyar daukan hoton scanning cikin ‘yan mintuna sabanin hanyar da ake amfani da shi na dube-duben zahiri wanda hakan ne dauka tsowon lokaci kuma wasu lokutan ba a samun biyan bukata yadda ake so.

Labarai Masu Nasaba

Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)

Kariya Daga Soyayyar ‘Online’ Da Shagalta A Intanet

Don haka ne suka ce, amfani da fasahar daukan hoton zai kawo sauki sosai kuma zai taimaka wajen kyautata tsaro da rage matsatsin aiki hadi da taimaka wa kasar na sosai.

Don haka ne suka nemi masu hannu da shuni da su zuba hannun jarinsu wajen kawo na’urar daukan hotuna a filayen jiragen ruwa domin kwalliya ta biya kudin sabulu.

Sun kuma cimma matsayar cewa za a sake gina sabuwar layin dogo a gefen na’urar daukan hoto da ke filin jirgin ruwan Apapa domin tabbatar da rage cinkso da bada damar saukaka aikin daukan hoton cikin sauki da hanzari.

 Sun kuma cimma matsayar sake kwaskwarima da tabbatar da ana amfani da naurorin daukan hotuna da ake da su a halin yanzu a wasu jiragen jiragen ruwa kamar su na Apapa, Tincan Island, Onne, da PTML domin tabbatar da amfaninsu da cin gajiyarsu, kuma na’urar salula na daukan hotona su ma za a tabbatar da zuba su a muhumman filayen jiragen ruwa domin saukaka aikin duba jiragen ruwa da kayan da suka kwaso.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ƙungiyar Masu Sana’ar POS Za Ta Fara Aikin Taftace Sana’ar A Faɗin Kasar Nan

Next Post

Dabarun Kiwon Zomo A Saukake

Related

Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)

2 months ago
Kariya Daga Soyayyar ‘Online’ Da Shagalta A Intanet
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Kariya Daga Soyayyar ‘Online’ Da Shagalta A Intanet

4 months ago
Hanyoyin Kare Kanka Daga Damfara Ta Intanet
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Hanyoyin Kare Kanka Daga Damfara Ta Intanet

4 months ago
Yadda Za A Kare Yara Daga Barazanar Intanet
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Yadda Za A Kare Yara Daga Barazanar Intanet

4 months ago
Mantuwa Na Matukar Taimakon Rayuwar Mutane – Masani
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Mantuwa Na Matukar Taimakon Rayuwar Mutane – Masani

9 months ago
Yadda Na Kirkiro ‘Brain-chip’ Da Ke Dawo Wa Wadanda Aka Haifa Da Makanta Ganinsu – Elon Musk
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Yadda Na Kirkiro ‘Brain-chip’ Da Ke Dawo Wa Wadanda Aka Haifa Da Makanta Ganinsu – Elon Musk

9 months ago
Next Post
Dabarun Kiwon Zomo A Saukake

Dabarun Kiwon Zomo A Saukake

LABARAI MASU NASABA

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

July 1, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

July 1, 2025
An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

July 1, 2025
Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma

Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma

July 1, 2025
Kayan Aro Baya Rufe Katara

Kayan Aro Baya Rufe Katara

July 1, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

Askarawan Zamfara Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga, Kacalla Ɗanbokolo Ubangidan Turji

July 1, 2025
Tawagar Likitoci Ta Sin Ta Ba Da Horon Fasahar Likitancin Gargajiya Ta Sin A Nijar

Tawagar Likitoci Ta Sin Ta Ba Da Horon Fasahar Likitancin Gargajiya Ta Sin A Nijar

July 1, 2025
Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano

Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano

July 1, 2025
Fahimtar Sabon Tunani: Yadda Sin Ta Samu Bunkasa A Tarihi Ta Hanyar Juyin Juya Halin Da Take Yi Wa Kanta 

Fahimtar Sabon Tunani: Yadda Sin Ta Samu Bunkasa A Tarihi Ta Hanyar Juyin Juya Halin Da Take Yi Wa Kanta 

July 1, 2025
An Yi Bikin Kade-Kade Don Taya Murnar Cika Shekaru 104 Da Kafuwar JKS

An Yi Bikin Kade-Kade Don Taya Murnar Cika Shekaru 104 Da Kafuwar JKS

July 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.