ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnati Ta Nemi Zuba Jari A Fasahar Na’urar Hoto Da Ke Tashoshin Jiragen Ruwa

by Khalid Idris Doya
2 years ago
Ruwa

Gwamnatin tarayya ta bukaci kamfanoni masu zaman kansu da su zuba jari a bangaren fasahar na’urar daukar hoto ta (Scanning) a tashoshin jiragen ruwan Nijeriya domin dorewar amfani da ita da kuma bunkasa amfani da zamani a harkokin safarar jiragen ruwa a kasar nan.

Wannan bukatar ta fito ne a wajen ganawar bullo da dabarun hanyoyin da za a inganta jiragen ruwa da samar da tsarin kara samar da kudaden shiga da aka  yi a gudana a Abuja, wanda ya samu halartar ministan kula da teku da albarkatun cikin teko Gboyega Oyetola; ministan sufuri, Said Ahmed Alkali; kwanturola-janar na hukumar hana fasa kwabri wato Kwastam, Bashir Adewale Adeniyi da kuma darakta janar na hukumar kula da layukan dogo na Nijeriya (NRC), Fidet Okhiria.

  • Kasashen Afirka 10 Da Za Su Samu Bunkasar Tattalin Arziki A 2024
  • Bukatar Samar Da Tsaftatacciyar Adawa A Nijeriya

A wani mataki na inganta ayyukan jiragen ruwa a tashoshin jiragen ruwa da kuma ganin sun yi gogayya da takwarorinsu, ministoci da shugaban kwastam din sun amince kan cewar dole ne a samar da matakin duba jiragen ruwa na zahiri a filayen jiragen ruwa da samar da hadin guiwa da saukaka aiki domin kyautata kasuwanci.

ADVERTISEMENT

Kudurin na kunshe ta cikin sanar hadin guiwa da kakakin ministan da kula da albarkatun tekuna, Ismail Omipidan da na kwastam spokesman, Abdullahi Maiwada.

Ministocin sun bayyana muhimmancin amfanin na’urar kimiyya ta dubawa da tantancewa wato (NIIT) wajen rage cinkoso a filayen jirage, kuma bai wa shugaban kwastam ikon tantancewa kayan da jirgin ruwa ya dauko cikin sauki da hanzari ta hanyar daukan hoton scanning cikin ‘yan mintuna sabanin hanyar da ake amfani da shi na dube-duben zahiri wanda hakan ne dauka tsowon lokaci kuma wasu lokutan ba a samun biyan bukata yadda ake so.

LABARAI MASU NASABA

Zarewa Ta Ƙirƙiro Na’urar Gano Tsatsa Bayan Lashe Kyautar ‘Carbon Neutrality’ Ta Duniya

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

Don haka ne suka ce, amfani da fasahar daukan hoton zai kawo sauki sosai kuma zai taimaka wajen kyautata tsaro da rage matsatsin aiki hadi da taimaka wa kasar na sosai.

Don haka ne suka nemi masu hannu da shuni da su zuba hannun jarinsu wajen kawo na’urar daukan hotuna a filayen jiragen ruwa domin kwalliya ta biya kudin sabulu.

Sun kuma cimma matsayar cewa za a sake gina sabuwar layin dogo a gefen na’urar daukan hoto da ke filin jirgin ruwan Apapa domin tabbatar da rage cinkso da bada damar saukaka aikin daukan hoton cikin sauki da hanzari.

 Sun kuma cimma matsayar sake kwaskwarima da tabbatar da ana amfani da naurorin daukan hotuna da ake da su a halin yanzu a wasu jiragen jiragen ruwa kamar su na Apapa, Tincan Island, Onne, da PTML domin tabbatar da amfaninsu da cin gajiyarsu, kuma na’urar salula na daukan hotona su ma za a tabbatar da zuba su a muhumman filayen jiragen ruwa domin saukaka aikin duba jiragen ruwa da kayan da suka kwaso.

Ruwa
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ATBU Ta Janye Filin Ginin Masallaci Da Ta Bai wa TIMSAN, Ta Amince Kowa Ya Yi Addininsa Yadda Ya Fahimta
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi

MASU ALAKA

Zarewa Ta Ƙirƙiro Na’urar Gano Tsatsa Bayan Lashe Kyautar ‘Carbon Neutrality’ Ta Duniya
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Zarewa Ta Ƙirƙiro Na’urar Gano Tsatsa Bayan Lashe Kyautar ‘Carbon Neutrality’ Ta Duniya

February 21, 2026
Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai
Da ɗumi-ɗuminsa

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

September 5, 2025
Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)

April 19, 2025
Next Post
Dabarun Kiwon Zomo A Saukake

Dabarun Kiwon Zomo A Saukake

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.