ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnati Ta Nemi Zuba Jari A Fasahar Na’urar Hoto Da Ke Tashoshin Jiragen Ruwa

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Ruwa

Gwamnatin tarayya ta bukaci kamfanoni masu zaman kansu da su zuba jari a bangaren fasahar na’urar daukar hoto ta (Scanning) a tashoshin jiragen ruwan Nijeriya domin dorewar amfani da ita da kuma bunkasa amfani da zamani a harkokin safarar jiragen ruwa a kasar nan.

Wannan bukatar ta fito ne a wajen ganawar bullo da dabarun hanyoyin da za a inganta jiragen ruwa da samar da tsarin kara samar da kudaden shiga da aka  yi a gudana a Abuja, wanda ya samu halartar ministan kula da teku da albarkatun cikin teko Gboyega Oyetola; ministan sufuri, Said Ahmed Alkali; kwanturola-janar na hukumar hana fasa kwabri wato Kwastam, Bashir Adewale Adeniyi da kuma darakta janar na hukumar kula da layukan dogo na Nijeriya (NRC), Fidet Okhiria.

  • Kasashen Afirka 10 Da Za Su Samu Bunkasar Tattalin Arziki A 2024
  • Bukatar Samar Da Tsaftatacciyar Adawa A Nijeriya

A wani mataki na inganta ayyukan jiragen ruwa a tashoshin jiragen ruwa da kuma ganin sun yi gogayya da takwarorinsu, ministoci da shugaban kwastam din sun amince kan cewar dole ne a samar da matakin duba jiragen ruwa na zahiri a filayen jiragen ruwa da samar da hadin guiwa da saukaka aiki domin kyautata kasuwanci.

ADVERTISEMENT

Kudurin na kunshe ta cikin sanar hadin guiwa da kakakin ministan da kula da albarkatun tekuna, Ismail Omipidan da na kwastam spokesman, Abdullahi Maiwada.

Ministocin sun bayyana muhimmancin amfanin na’urar kimiyya ta dubawa da tantancewa wato (NIIT) wajen rage cinkoso a filayen jirage, kuma bai wa shugaban kwastam ikon tantancewa kayan da jirgin ruwa ya dauko cikin sauki da hanzari ta hanyar daukan hoton scanning cikin ‘yan mintuna sabanin hanyar da ake amfani da shi na dube-duben zahiri wanda hakan ne dauka tsowon lokaci kuma wasu lokutan ba a samun biyan bukata yadda ake so.

LABARAI MASU NASABA

Zarewa Ta Ƙirƙiro Na’urar Gano Tsatsa Bayan Lashe Kyautar ‘Carbon Neutrality’ Ta Duniya

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

Don haka ne suka ce, amfani da fasahar daukan hoton zai kawo sauki sosai kuma zai taimaka wajen kyautata tsaro da rage matsatsin aiki hadi da taimaka wa kasar na sosai.

Don haka ne suka nemi masu hannu da shuni da su zuba hannun jarinsu wajen kawo na’urar daukan hotuna a filayen jiragen ruwa domin kwalliya ta biya kudin sabulu.

Sun kuma cimma matsayar cewa za a sake gina sabuwar layin dogo a gefen na’urar daukan hoto da ke filin jirgin ruwan Apapa domin tabbatar da rage cinkso da bada damar saukaka aikin daukan hoton cikin sauki da hanzari.

 Sun kuma cimma matsayar sake kwaskwarima da tabbatar da ana amfani da naurorin daukan hotuna da ake da su a halin yanzu a wasu jiragen jiragen ruwa kamar su na Apapa, Tincan Island, Onne, da PTML domin tabbatar da amfaninsu da cin gajiyarsu, kuma na’urar salula na daukan hotona su ma za a tabbatar da zuba su a muhumman filayen jiragen ruwa domin saukaka aikin duba jiragen ruwa da kayan da suka kwaso.

Ruwa
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Yaro Ya Harbe Kansa Har Lahira Bayan Mafarauci Ya Yi Sakaci Da Bindigarsa A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    An Kama Mutane 5 Da Sassan Jikin Ɗan’Adam Za Su Yi Tsafi A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mai Neman Takarar Gwamnan Bauchi, Bala Jibrin, Ya Fice Daga APC Kan Zargin Ɗoki-ɗora

MASU ALAKA

Zarewa Ta Ƙirƙiro Na’urar Gano Tsatsa Bayan Lashe Kyautar ‘Carbon Neutrality’ Ta Duniya
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Zarewa Ta Ƙirƙiro Na’urar Gano Tsatsa Bayan Lashe Kyautar ‘Carbon Neutrality’ Ta Duniya

February 21, 2026
Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai
Da ɗumi-ɗuminsa

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

September 5, 2025
Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)

April 19, 2025
Next Post
Dabarun Kiwon Zomo A Saukake

Dabarun Kiwon Zomo A Saukake

LABARAI MASU NASABA

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.