Wasu ƴan bindiga da ake zaton ‘yan fashin daji ne sun kai hari ga mahaifiyar gwamnan jihar Taraba, Jumai Kefas, da ‘yar’uwarsa Atsi.
Lamarin ya faru ne a jiya Juma’a yayin da suke kan hanyar Wukari-Kente a ƙaramar hukumar Wukari. Shugaban ƙaramar hukumar Wukari ya tabbatar da harin a cikin hira da Weekend Trust, inda ya bayyana cewa wasu mutane a kan babura sun yi kokarin tsayar da motar da ke ɗauke da mahaifiyar gwamnan da ‘yar’uwarsa.
- ‘Yan Bindiga 3 Da Mai Yin Safarar Makamai Sun Shiga Hannu A Taraba
- Malaman Jami’ar Taraba Sun Sanya Sharuɗɗan Komawa Aji
Ɗaya daga cikin jami’an ‘yansanda ya yi harbi sama don tsoratar da maharan.
Bari Atsi Kefas ta samu raunin bindiga kuma an fara ba ta magani a Asibitin koyarwa na Taraba kafin daga bisani a tafi da ita Abuja don ci gaba da samun kulawa.
Matsalar tsaro dai har yanzu na ci gaba da zama babban ƙalubale a yankin Arewa, wanda ake buƙatar babban shiri daga gwamnati da kuma goyon baya daga al’umma.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp