• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Ƴansanda Sun Kama Mutane 12 Bisa Zarginsu Da Laifuka Daban-Daban A Gombe

by Yunusa Isa
2 years ago
Yansanda

Rundunar Ƴansandan Jihar Gombe ta gabatar da wasu mutane 12 ga manema labarai, wadanda ake zargi da aikata laifuka daban-daban a jihar.

Da yake karin haske ga manema labaran a hedkwatar rundunar, Kwamishinan Ƴan Sandan Jihar, CP Okua Etim ta bakin Jami’in Hulda da Jama’a na Rundunar ASP Sa’ad Sharif, yace “Rundunar ƴan sanda a Gombe ta samu nasarori da dama a cikin wannan mako, ta kama wassu da ake zargi da laifukan fashi da makami, da fyade, da sojan gona, da sata, da ƴan kulla makirci, da fasa gida da kwacen wayar salula da dai sauransu”.

  • ‘Yan Awaren Biyafara 30 Sun Shiga Hannun ‘Yansanda A Jihar Enugu

Yace rundunar ta kama wani matashi mai suna Habu Muhammad Kabir, bisa zargin sa da yin sojan gona, inda ya je sansanin horas da mahajjata dake Kwalejin Horar da Malaman Arabiyya ta Gombe, ya kuma gabatar da kansa a matsayin ma’aikacin Hukumar Tattara Harajin Cikin Gida ta Jihar don ya damfari maniyyatan jihar da sunan karban kudin haraji.

Wadda ake zargin ya amsa laifin buga jabun katin shaida da rasiti da kuma hatimin hukumar, inda ya karbi kudi Naira 30,000 daga hannun wassu maniyata biyu.

Sharif yace rundunar ta kuma kama wassu da dama wadanda ake zargi da laifukan fyade da fashi da makami, da fasa gida, da hadin baki da kuma sata.

LABARAI MASU NASABA

SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

Ya ce a yayin kamen, ƴan sandan sun samu wassu kayayyaki da makamai da suka hada da takardun bogi, da kwamfyuta tafi-da-gidanka, da injin dab’i (printer), da katin shaida na jabu, da tsabar kudi, da dan kamfai da kyalle, da adduna, da wukake, da tarin guraye da layu, da wayoyin hannu da dai sauransu.

Jami’in hulda da jama’an na rundunar ƴan sandan ya ce bayan kammala bincike, za a gurfanar da wadanda ake zargin a gaban kotu.

Da yake shawartar jama’a su rika baiwa jami’an tsaro bayanan da suka dace don gudanar da ayyukansu yadda ya kamata, jami’in ya ce rundunar ta himmatu wajen samar da zaman lafiya da tsaro ga al’ummar jihar.

Ya kara da cewa, rundunar ta samar da layukan waya na musamman don kai rahoton duk wata matsalar tsaro a jihar.

“Kuna iya kira a duk lokacin da kuka fuskanci aika-aika irin ta ƴan kalare ko wata matsala ta tsaro a gida ko a wurin aiki a faɗin Jihar Gombe, kar ku yi wata-wata, ku tuntubi lambobin mu na gaggawa 08150567771 ko kuma ku kira ƴan ‘Operation Hattara’ a kan 08035158691 ko kuma 09139962191”

Yayin zantawar su da manema labarai, wasu daga cikin wadanda ake zargin sun yi nadamar abin da suka aikata, suna masu bayyana hakan da cewa rudin shaidan ne.

Da suke rokon a yi musu sassauci, wadanda ake zargin sun bada tabbacin gyara halin su, tare da zamowa mutanen kwarai.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati
Labarai

SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

October 9, 2025
An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba
Labarai

An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

October 9, 2025
Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta
Manyan Labarai

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

October 9, 2025
Next Post
Ana Bin Jihar Kano Bashin Sama Da Naira Biliyan 240, Inji Abba Gida-gida 

Yanzu-yanzu: Gwamnan Jihar Kano Ya Sake Sanar Da Nadin Sabbin Mukamai

LABARAI MASU NASABA

SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

October 9, 2025
An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

October 9, 2025
Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

October 9, 2025
Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

October 9, 2025
Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

October 9, 2025
Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.