ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Ƴansanda Sun Kama Mutane 12 Bisa Zarginsu Da Laifuka Daban-Daban A Gombe

by Yunusa Isa
3 years ago
Yansanda

Rundunar Ƴansandan Jihar Gombe ta gabatar da wasu mutane 12 ga manema labarai, wadanda ake zargi da aikata laifuka daban-daban a jihar.

Da yake karin haske ga manema labaran a hedkwatar rundunar, Kwamishinan Ƴan Sandan Jihar, CP Okua Etim ta bakin Jami’in Hulda da Jama’a na Rundunar ASP Sa’ad Sharif, yace “Rundunar ƴan sanda a Gombe ta samu nasarori da dama a cikin wannan mako, ta kama wassu da ake zargi da laifukan fashi da makami, da fyade, da sojan gona, da sata, da ƴan kulla makirci, da fasa gida da kwacen wayar salula da dai sauransu”.

  • ‘Yan Awaren Biyafara 30 Sun Shiga Hannun ‘Yansanda A Jihar Enugu

Yace rundunar ta kama wani matashi mai suna Habu Muhammad Kabir, bisa zargin sa da yin sojan gona, inda ya je sansanin horas da mahajjata dake Kwalejin Horar da Malaman Arabiyya ta Gombe, ya kuma gabatar da kansa a matsayin ma’aikacin Hukumar Tattara Harajin Cikin Gida ta Jihar don ya damfari maniyyatan jihar da sunan karban kudin haraji.

ADVERTISEMENT

Wadda ake zargin ya amsa laifin buga jabun katin shaida da rasiti da kuma hatimin hukumar, inda ya karbi kudi Naira 30,000 daga hannun wassu maniyata biyu.

Sharif yace rundunar ta kuma kama wassu da dama wadanda ake zargi da laifukan fyade da fashi da makami, da fasa gida, da hadin baki da kuma sata.

LABARAI MASU NASABA

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Ya ce a yayin kamen, ƴan sandan sun samu wassu kayayyaki da makamai da suka hada da takardun bogi, da kwamfyuta tafi-da-gidanka, da injin dab’i (printer), da katin shaida na jabu, da tsabar kudi, da dan kamfai da kyalle, da adduna, da wukake, da tarin guraye da layu, da wayoyin hannu da dai sauransu.

Jami’in hulda da jama’an na rundunar ƴan sandan ya ce bayan kammala bincike, za a gurfanar da wadanda ake zargin a gaban kotu.

Da yake shawartar jama’a su rika baiwa jami’an tsaro bayanan da suka dace don gudanar da ayyukansu yadda ya kamata, jami’in ya ce rundunar ta himmatu wajen samar da zaman lafiya da tsaro ga al’ummar jihar.

Ya kara da cewa, rundunar ta samar da layukan waya na musamman don kai rahoton duk wata matsalar tsaro a jihar.

“Kuna iya kira a duk lokacin da kuka fuskanci aika-aika irin ta ƴan kalare ko wata matsala ta tsaro a gida ko a wurin aiki a faɗin Jihar Gombe, kar ku yi wata-wata, ku tuntubi lambobin mu na gaggawa 08150567771 ko kuma ku kira ƴan ‘Operation Hattara’ a kan 08035158691 ko kuma 09139962191”

Yayin zantawar su da manema labarai, wasu daga cikin wadanda ake zargin sun yi nadamar abin da suka aikata, suna masu bayyana hakan da cewa rudin shaidan ne.

Da suke rokon a yi musu sassauci, wadanda ake zargin sun bada tabbacin gyara halin su, tare da zamowa mutanen kwarai.

Yansanda
Yunusa Isa
+ postsBio
  • Yunusa Isa
    https://hausa.leadership.ng/author/yunusa-isa/
    Asalin Abin Da Ya Sa Barayi Suka Kashe Sheikh Albani Kuri
  • Yunusa Isa
    https://hausa.leadership.ng/author/yunusa-isa/
    Gwamnatin Gombe Za Ta Dauki Sababbin Ma’aikatan Lafiya 200
  • Yunusa Isa
    https://hausa.leadership.ng/author/yunusa-isa/
    Gwamnatin Gombe Ta Sha Alwashin Magance Rikicin Manoma Da Makiyaya
  • Yunusa Isa
    https://hausa.leadership.ng/author/yunusa-isa/
    Gwamnatin Gombe Ta Bukaci Jami’an Lafiya Da Su Kara Kwazo Wajen Yaki Da Cutar Sida

MASU ALAKA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
Labarai

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Next Post
Ana Bin Jihar Kano Bashin Sama Da Naira Biliyan 240, Inji Abba Gida-gida 

Yanzu-yanzu: Gwamnan Jihar Kano Ya Sake Sanar Da Nadin Sabbin Mukamai

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.