ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Ƴansanda Sun Kama Mutane 12 Bisa Zarginsu Da Laifuka Daban-Daban A Gombe

by Yunusa Isa
3 years ago
Yansanda

Rundunar Ƴansandan Jihar Gombe ta gabatar da wasu mutane 12 ga manema labarai, wadanda ake zargi da aikata laifuka daban-daban a jihar.

Da yake karin haske ga manema labaran a hedkwatar rundunar, Kwamishinan Ƴan Sandan Jihar, CP Okua Etim ta bakin Jami’in Hulda da Jama’a na Rundunar ASP Sa’ad Sharif, yace “Rundunar ƴan sanda a Gombe ta samu nasarori da dama a cikin wannan mako, ta kama wassu da ake zargi da laifukan fashi da makami, da fyade, da sojan gona, da sata, da ƴan kulla makirci, da fasa gida da kwacen wayar salula da dai sauransu”.

  • ‘Yan Awaren Biyafara 30 Sun Shiga Hannun ‘Yansanda A Jihar Enugu

Yace rundunar ta kama wani matashi mai suna Habu Muhammad Kabir, bisa zargin sa da yin sojan gona, inda ya je sansanin horas da mahajjata dake Kwalejin Horar da Malaman Arabiyya ta Gombe, ya kuma gabatar da kansa a matsayin ma’aikacin Hukumar Tattara Harajin Cikin Gida ta Jihar don ya damfari maniyyatan jihar da sunan karban kudin haraji.

ADVERTISEMENT

Wadda ake zargin ya amsa laifin buga jabun katin shaida da rasiti da kuma hatimin hukumar, inda ya karbi kudi Naira 30,000 daga hannun wassu maniyata biyu.

Sharif yace rundunar ta kuma kama wassu da dama wadanda ake zargi da laifukan fyade da fashi da makami, da fasa gida, da hadin baki da kuma sata.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Ya ce a yayin kamen, ƴan sandan sun samu wassu kayayyaki da makamai da suka hada da takardun bogi, da kwamfyuta tafi-da-gidanka, da injin dab’i (printer), da katin shaida na jabu, da tsabar kudi, da dan kamfai da kyalle, da adduna, da wukake, da tarin guraye da layu, da wayoyin hannu da dai sauransu.

Jami’in hulda da jama’an na rundunar ƴan sandan ya ce bayan kammala bincike, za a gurfanar da wadanda ake zargin a gaban kotu.

Da yake shawartar jama’a su rika baiwa jami’an tsaro bayanan da suka dace don gudanar da ayyukansu yadda ya kamata, jami’in ya ce rundunar ta himmatu wajen samar da zaman lafiya da tsaro ga al’ummar jihar.

Ya kara da cewa, rundunar ta samar da layukan waya na musamman don kai rahoton duk wata matsalar tsaro a jihar.

“Kuna iya kira a duk lokacin da kuka fuskanci aika-aika irin ta ƴan kalare ko wata matsala ta tsaro a gida ko a wurin aiki a faɗin Jihar Gombe, kar ku yi wata-wata, ku tuntubi lambobin mu na gaggawa 08150567771 ko kuma ku kira ƴan ‘Operation Hattara’ a kan 08035158691 ko kuma 09139962191”

Yayin zantawar su da manema labarai, wasu daga cikin wadanda ake zargin sun yi nadamar abin da suka aikata, suna masu bayyana hakan da cewa rudin shaidan ne.

Da suke rokon a yi musu sassauci, wadanda ake zargin sun bada tabbacin gyara halin su, tare da zamowa mutanen kwarai.

Yansanda
Yunusa Isa
+ postsBio
  • Yunusa Isa
    https://hausa.leadership.ng/author/yunusa-isa/
    Asalin Abin Da Ya Sa Barayi Suka Kashe Sheikh Albani Kuri
  • Yunusa Isa
    https://hausa.leadership.ng/author/yunusa-isa/
    Gwamnatin Gombe Za Ta Dauki Sababbin Ma’aikatan Lafiya 200
  • Yunusa Isa
    https://hausa.leadership.ng/author/yunusa-isa/
    Gwamnatin Gombe Ta Sha Alwashin Magance Rikicin Manoma Da Makiyaya
  • Yunusa Isa
    https://hausa.leadership.ng/author/yunusa-isa/
    Gwamnatin Gombe Ta Bukaci Jami’an Lafiya Da Su Kara Kwazo Wajen Yaki Da Cutar Sida

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
Ana Bin Jihar Kano Bashin Sama Da Naira Biliyan 240, Inji Abba Gida-gida 

Yanzu-yanzu: Gwamnan Jihar Kano Ya Sake Sanar Da Nadin Sabbin Mukamai

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.