Rundunar ’yansandan Nijeriya, ta gurfanar da wani dan kasar Indiya da wasu ’yan Nijeriya 12 a gaban Babbar Kotun Tarayya da ke Legas, bisa zargin su da hada baki wajen karkatar da danyen man dizal na kamfanin Dangote da aka kiyasta darajarsa ta kai naira biliyan huɗu.
Mai shari’a, Deinde Dipeolu ne ya karanatawa wanda ake zargin tuhume-tuhume 16 da suka shafi hada baki wajen aikata laifi, karkatar da danyen man dizel, da kuma karɓar kuɗi ta hanyar da ba ta dace ba daga harkokin man fetur.
- Guguwa Za Ta Sa Kasashen Sin Da Afirka Su Kara Rike Hannayen Juna
- Shugabannin Sin Da Kongo (Brazaville) Sun Aike Da Wasikun Taya Murna Ga Taron Ministocin Kula Da Aiwatar Da Sakamakon Taron FOCAC
Lauyan gwamnati, Mista M. Y. Bello, ya shaidawa kotu cewa, wadanda ake zargin ma’aikata ne na kamfanin Dangote da kuma wasu kamfanonin jigilar man fetur da suka hada da Arigen Integrated Limited, Obat Limited, Amaiden Energy Limited, Regal Gate Limited, Alkham Limited, Prestige Limited, da kuma Opetrus Global Limited.
Binciken ya nuna cewa, mutum biyu daga cikin wadanda ake zargin ma’aikatan Dangote ne kai tsaye, yayin da sauran ke aiki da kamfanonin da ke da alaka da safarar mai daga matatar Dangote zuwa wuraren ajiya na kamfanin da ke Ibese da Obajana.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp