• English
  • Business News
Tuesday, November 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ɗan Takarar Gwamnan Zamfara, Dauda Lawal Ya Halarci Taron Masu Ruwa Da Tsaki Da Atiku

by Bello Hamza
3 years ago
Zamfara

Ɗan takarar gwamnan Jihar Zamfara a ƙarƙashin inuwar jam’iyyar PDP, Dr. Dauda Lawal ya halarci taron masu ruwa da tsaki na yankin Arewa maso Yamma.

Taron wanda aka gudanar yau Talata a dakin taro na Bristol dake Kano, ya samu halartar gabaɗaya ‘yan takarar gwamna daga jihohi bakwai na yankin.

Yanzu-yanzu: Tinubu Ya Gana Da Jonathan, Ya Nemi Ya Mara Masa Baya

 

A yayin taron, wanda ɗan takarar shugaban ƙasa, Atiku Abubakar ya yi don gudanar da tattaunawa ta musamman da ‘yan takarar gwamna na jihohin Arewa maso Yamma da masu ruwa da tsaki na jam’iyyar PDP daga yankin. Tsohon mataimakin Shugaban Ƙasan kuma Wazirin Adamawa ya yi kira ga musamman ‘yan takarar gwamnan da su ci gaba da yin aiki don nasarar jam’iyyar.

LABARAI MASU NASABA

Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha

“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump

Ya bayyana cewa, idan har PDP ta lashe zaɓen shugaban ƙasa wanda shi ne za a fara gudanarwa, toh babu makawa jam’iyyar za ta lashe sauran kujeru, kama daga na gwamna, sanata, da sauransu.

Da farkon fara taron dai an gabatar da mataimakin shugaban jam’iyyar PDP na yankin Arewa maso Yamma, Alhaji Hayatu Gwarzo wanda ya yi maraba da baki tare da bayyana maƙasudin kiran wannan tattaunawa ta musamman.

Bayan nan an gabatar da ‘yan takarar gwamna daga jihohi bakwai na wannan yankin. Dakta Dauda Lawal daga Jihar Zamfara, Ashiru Isa Kudan daga Jihae Kaduna, Mustapha Sule Lamido daga Jihar Jigawa, Sadiƙ Walid aga Jihar Kano, Janar Aminu Bande daga Jihar Kebbi, Sa’idu Umar daga Jihar Sakkwato.

Ɗan takarar gwamna na Jihar Kaduna, Isa Ashiru Kudan ne ya yi jawabi a madadin ‘yan uwansa ‘yan takara daga waɗannan jihohin Arewa maso Yamma guda bakwai. Ya bayyana jin daɗinsu ga irin wannan muhimmin taro, wanda a cewarsa ya ƙara kusanto ‘yan takarar da ɗan takarar shugaban ƙasa, Atiku Abubakar.

Cikin jiga-jigai da suka halarci wannan taro akwai gwamnan Jihar Delta kuma ɗan takarar mataimakin shugaban ƙasa a PDP, Ifeanyi Okowa, gwamnan Jihar Sakkwato, Aminu Waziri Tambuwal, shugaban jam’iyyar PDP ta ƙasa, Sanata Iyochia Ayu, tsohon mataimakin Shugaban Ƙasa, Namadi Sambo, tsohon gwamnan Jihar Jigawa, Sule Lamido, tsohon gwamnan Jihar Katsina, Ibrahim Shehu Shema da dai sauransu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha
Siyasa

Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha

November 4, 2025
“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump
Labarai

“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump

November 3, 2025
Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna
Manyan Labarai

Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna

November 1, 2025
Next Post
Hadarin Kwale-kwale: Mutum Biyu Sun Rasu, An Ceto Bakwai A Jigawa

Hadarin Kwale-kwale: Mutum Biyu Sun Rasu, An Ceto Bakwai A Jigawa

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Jami’in Diflomasiyyar Nijar: Baje Kolin CIIE Muhimmin Dandali Ne Na Bunkasa Hadin Gwiwa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

Tsohon Jami’in Diflomasiyyar Nijar: Baje Kolin CIIE Muhimmin Dandali Ne Na Bunkasa Hadin Gwiwa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

November 4, 2025
Zulum Ya Raba Motocin Sintiri 63 Ga Hukumomin Tsaro A Borno

Zulum Ya Raba Motocin Sintiri 63 Ga Hukumomin Tsaro A Borno

November 4, 2025
Shugaban Xi Ya Gana Da Firaministan Rasha

Shugaban Xi Ya Gana Da Firaministan Rasha

November 4, 2025
China Ta Gargaɗi Amurka Kan Tsoma Baki A Harkokin Nijeriya

China Ta Gargaɗi Amurka Kan Tsoma Baki A Harkokin Nijeriya

November 4, 2025
2023: Me Ya Sa Ake Rububin Wike?

Atiku Ya Fice Daga PDP Saboda Na Ƙi Bari Ya Lalata Mana Jam’iyya – Wike

November 4, 2025
Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha

Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha

November 4, 2025
Kalaman Trump A Kan Nijeriya Abun Damuwa Ne – Peter Obi 

Kalaman Trump A Kan Nijeriya Abun Damuwa Ne – Peter Obi 

November 4, 2025
Jami’an Tsaro Sun Dawo Da Fasfo Ɗin Sanata Natasha Bayan Ƙwace Shi A Abuja

Natasha Ta Zargi Akpabio Da Sanya Jami’an Tsaro Su Ƙwace Mata Fasfo A Filin Jirgin Saman Abuja 

November 4, 2025
Masu Kashe Mutane A Kudu Maso Gabas Kiristoci Ne – Soludo

Masu Kashe Mutane A Kudu Maso Gabas Kiristoci Ne – Soludo

November 4, 2025
Ribadu Ya Gana Da Hafsoshin Tsaro Biyo Bayan Kalaman Trump 

Ribadu Ya Gana Da Hafsoshin Tsaro Biyo Bayan Kalaman Trump 

November 4, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.