• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ɗan Takarar Gwamnan Zamfara, Dauda Lawal Ya Halarci Taron Masu Ruwa Da Tsaki Da Atiku

by Bello Hamza
3 years ago
Zamfara

Ɗan takarar gwamnan Jihar Zamfara a ƙarƙashin inuwar jam’iyyar PDP, Dr. Dauda Lawal ya halarci taron masu ruwa da tsaki na yankin Arewa maso Yamma.

Taron wanda aka gudanar yau Talata a dakin taro na Bristol dake Kano, ya samu halartar gabaɗaya ‘yan takarar gwamna daga jihohi bakwai na yankin.

Yanzu-yanzu: Tinubu Ya Gana Da Jonathan, Ya Nemi Ya Mara Masa Baya

 

A yayin taron, wanda ɗan takarar shugaban ƙasa, Atiku Abubakar ya yi don gudanar da tattaunawa ta musamman da ‘yan takarar gwamna na jihohin Arewa maso Yamma da masu ruwa da tsaki na jam’iyyar PDP daga yankin. Tsohon mataimakin Shugaban Ƙasan kuma Wazirin Adamawa ya yi kira ga musamman ‘yan takarar gwamnan da su ci gaba da yin aiki don nasarar jam’iyyar.

LABARAI MASU NASABA

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

Kotu Ta Yi Watsi Da Ƙarar Da Aka Shigar Da Tinubu Kan Sanya Dokar Ta-Ɓaci A Ribas

Ya bayyana cewa, idan har PDP ta lashe zaɓen shugaban ƙasa wanda shi ne za a fara gudanarwa, toh babu makawa jam’iyyar za ta lashe sauran kujeru, kama daga na gwamna, sanata, da sauransu.

Da farkon fara taron dai an gabatar da mataimakin shugaban jam’iyyar PDP na yankin Arewa maso Yamma, Alhaji Hayatu Gwarzo wanda ya yi maraba da baki tare da bayyana maƙasudin kiran wannan tattaunawa ta musamman.

Bayan nan an gabatar da ‘yan takarar gwamna daga jihohi bakwai na wannan yankin. Dakta Dauda Lawal daga Jihar Zamfara, Ashiru Isa Kudan daga Jihae Kaduna, Mustapha Sule Lamido daga Jihar Jigawa, Sadiƙ Walid aga Jihar Kano, Janar Aminu Bande daga Jihar Kebbi, Sa’idu Umar daga Jihar Sakkwato.

Ɗan takarar gwamna na Jihar Kaduna, Isa Ashiru Kudan ne ya yi jawabi a madadin ‘yan uwansa ‘yan takara daga waɗannan jihohin Arewa maso Yamma guda bakwai. Ya bayyana jin daɗinsu ga irin wannan muhimmin taro, wanda a cewarsa ya ƙara kusanto ‘yan takarar da ɗan takarar shugaban ƙasa, Atiku Abubakar.

Cikin jiga-jigai da suka halarci wannan taro akwai gwamnan Jihar Delta kuma ɗan takarar mataimakin shugaban ƙasa a PDP, Ifeanyi Okowa, gwamnan Jihar Sakkwato, Aminu Waziri Tambuwal, shugaban jam’iyyar PDP ta ƙasa, Sanata Iyochia Ayu, tsohon mataimakin Shugaban Ƙasa, Namadi Sambo, tsohon gwamnan Jihar Jigawa, Sule Lamido, tsohon gwamnan Jihar Katsina, Ibrahim Shehu Shema da dai sauransu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu
Siyasa

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
Kotu Ta Yi Watsi Da Ƙarar Da Aka Shigar Da Tinubu Kan Sanya Dokar Ta-Ɓaci A Ribas
Labarai

Kotu Ta Yi Watsi Da Ƙarar Da Aka Shigar Da Tinubu Kan Sanya Dokar Ta-Ɓaci A Ribas

October 2, 2025
Jam’iyyar PDP Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni A Kwara
Siyasa

Jam’iyyar PDP Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni A Kwara

September 28, 2025
Next Post
Hadarin Kwale-kwale: Mutum Biyu Sun Rasu, An Ceto Bakwai A Jigawa

Hadarin Kwale-kwale: Mutum Biyu Sun Rasu, An Ceto Bakwai A Jigawa

LABARAI MASU NASABA

An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

October 9, 2025
Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

October 9, 2025
Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

October 9, 2025
Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

October 9, 2025
Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.