• English
  • Business News
Saturday, June 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ɗan Takarar Gwamnan Zamfara, Dauda Lawal Ya Halarci Taron Masu Ruwa Da Tsaki Da Atiku

by Bello Hamza
3 years ago
in Siyasa
0
Ɗan Takarar Gwamnan Zamfara, Dauda Lawal Ya Halarci Taron Masu Ruwa Da Tsaki Da Atiku
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ɗan takarar gwamnan Jihar Zamfara a ƙarƙashin inuwar jam’iyyar PDP, Dr. Dauda Lawal ya halarci taron masu ruwa da tsaki na yankin Arewa maso Yamma.

Taron wanda aka gudanar yau Talata a dakin taro na Bristol dake Kano, ya samu halartar gabaɗaya ‘yan takarar gwamna daga jihohi bakwai na yankin.

Yanzu-yanzu: Tinubu Ya Gana Da Jonathan, Ya Nemi Ya Mara Masa Baya

 

A yayin taron, wanda ɗan takarar shugaban ƙasa, Atiku Abubakar ya yi don gudanar da tattaunawa ta musamman da ‘yan takarar gwamna na jihohin Arewa maso Yamma da masu ruwa da tsaki na jam’iyyar PDP daga yankin. Tsohon mataimakin Shugaban Ƙasan kuma Wazirin Adamawa ya yi kira ga musamman ‘yan takarar gwamnan da su ci gaba da yin aiki don nasarar jam’iyyar.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Kano Ta Ƙaryata Karɓo Bashin Dala Miliyan 6.6

Zamfara: APC Za Ta Maka PDP A Kotu Kan Zargin Matawalle Da Hannu A Satar Mutane

Ya bayyana cewa, idan har PDP ta lashe zaɓen shugaban ƙasa wanda shi ne za a fara gudanarwa, toh babu makawa jam’iyyar za ta lashe sauran kujeru, kama daga na gwamna, sanata, da sauransu.

Da farkon fara taron dai an gabatar da mataimakin shugaban jam’iyyar PDP na yankin Arewa maso Yamma, Alhaji Hayatu Gwarzo wanda ya yi maraba da baki tare da bayyana maƙasudin kiran wannan tattaunawa ta musamman.

Bayan nan an gabatar da ‘yan takarar gwamna daga jihohi bakwai na wannan yankin. Dakta Dauda Lawal daga Jihar Zamfara, Ashiru Isa Kudan daga Jihae Kaduna, Mustapha Sule Lamido daga Jihar Jigawa, Sadiƙ Walid aga Jihar Kano, Janar Aminu Bande daga Jihar Kebbi, Sa’idu Umar daga Jihar Sakkwato.

Ɗan takarar gwamna na Jihar Kaduna, Isa Ashiru Kudan ne ya yi jawabi a madadin ‘yan uwansa ‘yan takara daga waɗannan jihohin Arewa maso Yamma guda bakwai. Ya bayyana jin daɗinsu ga irin wannan muhimmin taro, wanda a cewarsa ya ƙara kusanto ‘yan takarar da ɗan takarar shugaban ƙasa, Atiku Abubakar.

Cikin jiga-jigai da suka halarci wannan taro akwai gwamnan Jihar Delta kuma ɗan takarar mataimakin shugaban ƙasa a PDP, Ifeanyi Okowa, gwamnan Jihar Sakkwato, Aminu Waziri Tambuwal, shugaban jam’iyyar PDP ta ƙasa, Sanata Iyochia Ayu, tsohon mataimakin Shugaban Ƙasa, Namadi Sambo, tsohon gwamnan Jihar Jigawa, Sule Lamido, tsohon gwamnan Jihar Katsina, Ibrahim Shehu Shema da dai sauransu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Yanzu-yanzu: Tinubu Ya Gana Da Jonathan, Ya Nemi Ya Mara Masa Baya

Next Post

Hadarin Kwale-kwale: Mutum Biyu Sun Rasu, An Ceto Bakwai A Jigawa

Related

Gwamnatin Kano Ta Ƙaryata Karɓo Bashin Dala Miliyan 6.6
Labarai

Gwamnatin Kano Ta Ƙaryata Karɓo Bashin Dala Miliyan 6.6

16 hours ago
Zamfara: APC Za Ta Maka PDP A Kotu Kan Zargin Matawalle Da Hannu A Satar Mutane
Manyan Labarai

Zamfara: APC Za Ta Maka PDP A Kotu Kan Zargin Matawalle Da Hannu A Satar Mutane

2 days ago
A Bai Wa Kudu Tikitin Takara A 2027 Ko PDP Ta Ruguje – Wani Jigo A PDP
Siyasa

A Bai Wa Kudu Tikitin Takara A 2027 Ko PDP Ta Ruguje – Wani Jigo A PDP

3 days ago
Shehu Sani Ya Buƙaci Shugabannin Arewa Su Mara Wa Tinubu Baya Ya Yi Shekaru 8 A Kan Mulki
Manyan Labarai

Shehu Sani Ya Buƙaci Shugabannin Arewa Su Mara Wa Tinubu Baya Ya Yi Shekaru 8 A Kan Mulki

2 weeks ago
Babu Wanda Zai Iya Kora Ta Daga PDP —  Wike
Siyasa

Babu Wanda Zai Iya Kora Ta Daga PDP —  Wike

2 weeks ago
Sulhun PDP Ya Haɗu Da Cikas, Wike Ya Janye Daga Duk Wata Yarjejeniya
Siyasa

Sulhun PDP Ya Haɗu Da Cikas, Wike Ya Janye Daga Duk Wata Yarjejeniya

2 weeks ago
Next Post
Hadarin Kwale-kwale: Mutum Biyu Sun Rasu, An Ceto Bakwai A Jigawa

Hadarin Kwale-kwale: Mutum Biyu Sun Rasu, An Ceto Bakwai A Jigawa

LABARAI MASU NASABA

Taron Koli Na Sin Da Kasashen Yankin Tsakiyar Asiya Karo Na Biyu Zai Ingiza Manufar Kara Dunkulewar Sassan Yankin

Taron Koli Na Sin Da Kasashen Yankin Tsakiyar Asiya Karo Na Biyu Zai Ingiza Manufar Kara Dunkulewar Sassan Yankin

June 13, 2025
jam'iyyu

Sarkakiyar Da Ke Tattare Da Zaben 2027 Da Yadda Za Ta Kaya

June 13, 2025
Nijeriya Na Kan Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arziki Da Dawo Da Martabar Ƙasa — Ministan Yaɗa Labarai

Nijeriya Na Kan Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arziki Da Dawo Da Martabar Ƙasa — Ministan Yaɗa Labarai

June 13, 2025
Babban Jami’in Diflomasiyyar Kasar Sin Ya Yi Kiran Karfafa Alaka Da Afirka

Babban Jami’in Diflomasiyyar Kasar Sin Ya Yi Kiran Karfafa Alaka Da Afirka

June 13, 2025
Xi Ya Yi Kira Da A Kara Azamar Gina Kasa A Gabar Da Ake Bikin Cika Shekaru 120 Da Haihuwar Dan Mazan Jiya Chen Yun

Xi Ya Yi Kira Da A Kara Azamar Gina Kasa A Gabar Da Ake Bikin Cika Shekaru 120 Da Haihuwar Dan Mazan Jiya Chen Yun

June 13, 2025
Pogba Na Shirin Komawa Monaco Bayan Dakatar Da Shi

Pogba Na Shirin Komawa Monaco Bayan Dakatar Da Shi

June 13, 2025
Nijeriya Da Morocco Za Su Sanya Hannu Kan Kulla Yarjejeniyar Aikin Bututun Iskar Gas

Gwamnatin Tarayya Ta Himmatu Wajen Inganta Karfin Sashen Fetur Da Gas Na Cikin Gida

June 13, 2025
Bin Hanya Daya Da Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Muhimmin Mataki Ne Na Ba Da Tabbaci Ga Huldar Ciniki Da Tattalin Arzikin Sin Da Amurka

Bin Hanya Daya Da Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Muhimmin Mataki Ne Na Ba Da Tabbaci Ga Huldar Ciniki Da Tattalin Arzikin Sin Da Amurka

June 13, 2025
Sin Ta Bayyana Adawa Da Keta Hurumin ‘Yanci Tsaro Da Ikon Mulkin Yankunan Iran

Sin Ta Bayyana Adawa Da Keta Hurumin ‘Yanci Tsaro Da Ikon Mulkin Yankunan Iran

June 13, 2025
Gwamnati Ta Yi Karin Haske Kan Biyan Tallafin Rage Radadi Da Mafi Karancin Albashi

Gwamnati Ta Yi Karin Haske Kan Biyan Tallafin Rage Radadi Da Mafi Karancin Albashi

June 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.