• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: A Shirye Muke Mu Bude Kofar Kulla Kawance Da Sauran Jam’iyyu Kafin Zabe –NNPP

jam’iyyar NNPP ba ta kyamar tattaunawa don gina kasa.

byMuhammad
3 years ago
2023

Shugaban jam’iyyar NNPP na kasa, Rufa’i Alkali, a ranar Larabar, ya bayyana cewa jam’iyyar a shirye take ta hada kai da wasu Jam’iyyun siyasa kafin zaben 2023 mai zuwa.

Mista Alkali, mai baiwa tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan shawara ne kan harkokin siyasa, ya bayyana hakan a Legas a wani taron manema labarai.

  • Rikicin NNPP: Kwankwaso Ya Ci Amanarmu – Shekarau
  • Dalilin Da Yasa Ban Halarci Taron NBA Ba – Kwankwaso 

A cewarsa, jam’iyyar ba ta kyamar tattaunawa don gina kasa.

“Jam’iyyun da ke son tattaunawa da jam’iyyar NNPP ba aibu ba ne su yi hakan a don samar da tafiya daya mai karfi, kuma dole ne mu bayyana ra’ayoyinmu kan makomar kasar nan.

“Dukkan jam’iyyu daidai suke a gaban doka.

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Yi Watsi Da Ƙarar Da Aka Shigar Da Tinubu Kan Sanya Dokar Ta-Ɓaci A Ribas

Jam’iyyar PDP Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni A Kwara

“Muna magana ne game da makomar Nijeriya,” in ji Mista Alkali, tsohon sakataren yada labaran jam’iyyar PDP na kasa.

Ya kuma yi tir da yadda ake tafiyar da harkokin siyasa a Nijeriya, yana mai cewa bai kamata mutane su zo a tattauna a fitar da dan takara daya tilo.

Tattaunawar kawance tsakanin jam’iyyun NNPP da Labour ta tsawon makonni ta gaza haifar da sakamako, shi ya sa ‘yan takarar shugaban kasa na jam’iyyun biyu – Mista Kwankwaso da Peter Obi – suka bayyana a matsayin ‘yan takara.

Alkali ya ce idan wata jam’iyya ta zauna don tattaunawa, dole ne su fara kokarin fahimtar kansu: mene ne suke da alaka da su – akida, hangen nesa, buri da kuma manufofin yin aiki tare.

Ya kara da cewa ya kamata jam’iyyu su amince da matakin kawance ko dai a majalisar wakilai, wakilai, dattijai, gwamna ko shugaban kasa.

“A siyasa muna magana ne game da kwazon aiki.”

Shugaban, ya ce Nijeriya ba za ta iya yin kuskure a 2023 ba, yana mai cewa jam’iyyar NNPP za ta bullo da sabbin dabarun gina tattalin arzikin kasa idan aka zabe shi.

Ya kara da cewa “NNPP tana wa Nijeriya shiri kuma za su kawo sauyi ga al’amuran siyasar kasar.”

Ya kara da cewa jam’iyyar NNPP ta kasance jam’iyyar siyasa mafi girma a Nijeriya kuma nan ba da dadewa ba za ta samu goyon bayan mafi yawan ‘yan Nijeriya a fadin kasar.

Ya ce jam’iyyar NNPP za ta ci gaba da bin ka’idojinta na inganta rayuwar talakawan Nijeriya.

“Abin da Nijeriya ke bukata shi ne shugabancin da mutane za su amince da su kuma za su samar,” in ji Alkali, farfesa a fannin kimiyyar siyasa da tattalin arziki.

Akan tikitin takarar musulmi da musulmi, shugaban ya ce hakkin dan takara ne ya zabi abokin takararsa, yana mai cewa abin da ya kamata ya fi dacewa shi ne tunkarar kalubalen Nijeriya.

Ya kara da cewa: “Idan muna son kasar nan ta canza dole ne mu wuce batun maganar yankin yanki da tattaunawa kan addini.

“Mun wuce matakin sabani na yanki da ra’ayin addini.” (NAN)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kotu Ta Yi Watsi Da Ƙarar Da Aka Shigar Da Tinubu Kan Sanya Dokar Ta-Ɓaci A Ribas
Labarai

Kotu Ta Yi Watsi Da Ƙarar Da Aka Shigar Da Tinubu Kan Sanya Dokar Ta-Ɓaci A Ribas

October 2, 2025
Jam’iyyar PDP Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni A Kwara
Siyasa

Jam’iyyar PDP Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni A Kwara

September 28, 2025
Tinubu Zai Gana Da Manyan Ƴan Kasuwa, Zai Ƙaddamar Da Muhimman Aiyuka A Legas
Siyasa

Tinubu Zai Gana Da Manyan Ƴan Kasuwa, Zai Ƙaddamar Da Muhimman Aiyuka A Legas

September 27, 2025
Next Post
Rikicin PDP: Bayan Ganawar Tinubu Da Wike A Landan, Ba Shiri Atiku Ya Garzaya Birtaniya

Rikicin PDP: Bayan Ganawar Tinubu Da Wike A Landan, Ba Shiri Atiku Ya Garzaya Birtaniya

LABARAI MASU NASABA

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version