ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: A Shirye Muke Mu Bude Kofar Kulla Kawance Da Sauran Jam’iyyu Kafin Zabe –NNPP

jam’iyyar NNPP ba ta kyamar tattaunawa don gina kasa.

by Muhammad
4 years ago
2023

Shugaban jam’iyyar NNPP na kasa, Rufa’i Alkali, a ranar Larabar, ya bayyana cewa jam’iyyar a shirye take ta hada kai da wasu Jam’iyyun siyasa kafin zaben 2023 mai zuwa.

Mista Alkali, mai baiwa tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan shawara ne kan harkokin siyasa, ya bayyana hakan a Legas a wani taron manema labarai.

  • Rikicin NNPP: Kwankwaso Ya Ci Amanarmu – Shekarau
  • Dalilin Da Yasa Ban Halarci Taron NBA Ba – Kwankwaso 

A cewarsa, jam’iyyar ba ta kyamar tattaunawa don gina kasa.

ADVERTISEMENT

“Jam’iyyun da ke son tattaunawa da jam’iyyar NNPP ba aibu ba ne su yi hakan a don samar da tafiya daya mai karfi, kuma dole ne mu bayyana ra’ayoyinmu kan makomar kasar nan.

“Dukkan jam’iyyu daidai suke a gaban doka.

LABARAI MASU NASABA

2027: Magoya Bayan Tinubu Sun Yi Watsi Da Sukar Takarar Musulmi-Musulmi Da Kwankwaso Ya Yi

Kabiru Gaya Ya Amince Zai Sauya Sheƙa Zuwa APC

“Muna magana ne game da makomar Nijeriya,” in ji Mista Alkali, tsohon sakataren yada labaran jam’iyyar PDP na kasa.

Ya kuma yi tir da yadda ake tafiyar da harkokin siyasa a Nijeriya, yana mai cewa bai kamata mutane su zo a tattauna a fitar da dan takara daya tilo.

Tattaunawar kawance tsakanin jam’iyyun NNPP da Labour ta tsawon makonni ta gaza haifar da sakamako, shi ya sa ‘yan takarar shugaban kasa na jam’iyyun biyu – Mista Kwankwaso da Peter Obi – suka bayyana a matsayin ‘yan takara.

Alkali ya ce idan wata jam’iyya ta zauna don tattaunawa, dole ne su fara kokarin fahimtar kansu: mene ne suke da alaka da su – akida, hangen nesa, buri da kuma manufofin yin aiki tare.

Ya kara da cewa ya kamata jam’iyyu su amince da matakin kawance ko dai a majalisar wakilai, wakilai, dattijai, gwamna ko shugaban kasa.

“A siyasa muna magana ne game da kwazon aiki.”

Shugaban, ya ce Nijeriya ba za ta iya yin kuskure a 2023 ba, yana mai cewa jam’iyyar NNPP za ta bullo da sabbin dabarun gina tattalin arzikin kasa idan aka zabe shi.

Ya kara da cewa “NNPP tana wa Nijeriya shiri kuma za su kawo sauyi ga al’amuran siyasar kasar.”

Ya kara da cewa jam’iyyar NNPP ta kasance jam’iyyar siyasa mafi girma a Nijeriya kuma nan ba da dadewa ba za ta samu goyon bayan mafi yawan ‘yan Nijeriya a fadin kasar.

Ya ce jam’iyyar NNPP za ta ci gaba da bin ka’idojinta na inganta rayuwar talakawan Nijeriya.

“Abin da Nijeriya ke bukata shi ne shugabancin da mutane za su amince da su kuma za su samar,” in ji Alkali, farfesa a fannin kimiyyar siyasa da tattalin arziki.

Akan tikitin takarar musulmi da musulmi, shugaban ya ce hakkin dan takara ne ya zabi abokin takararsa, yana mai cewa abin da ya kamata ya fi dacewa shi ne tunkarar kalubalen Nijeriya.

Ya kara da cewa: “Idan muna son kasar nan ta canza dole ne mu wuce batun maganar yankin yanki da tattaunawa kan addini.

“Mun wuce matakin sabani na yanki da ra’ayin addini.” (NAN)

2023
Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100
  • Muhammad
    ‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan
  • Muhammad
    Cikin Shekaru 28, Kudiri Ƙasa Da 10 Sanatocin Zamfara Ta Arewa Suka Gabatar A Majalisa – Shinkafi
  • Muhammad
    2027: NNPP Ta Yi Wa Korarrun Mambobinta Afuwa, Ta Yi Alƙawarin Basu Tikitin Kai-tsaye

MASU ALAKA

Kwankwaso Zai Koma ADC Ranar Litinin
Manyan Labarai

2027: Magoya Bayan Tinubu Sun Yi Watsi Da Sukar Takarar Musulmi-Musulmi Da Kwankwaso Ya Yi

July 22, 2026
Kabiru Gaya Ya Amince Zai Sauya Sheƙa Zuwa APC
Labarai

Kabiru Gaya Ya Amince Zai Sauya Sheƙa Zuwa APC

July 21, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai
Siyasa

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

July 16, 2026
Next Post
Rikicin PDP: Bayan Ganawar Tinubu Da Wike A Landan, Ba Shiri Atiku Ya Garzaya Birtaniya

Rikicin PDP: Bayan Ganawar Tinubu Da Wike A Landan, Ba Shiri Atiku Ya Garzaya Birtaniya

LABARAI MASU NASABA

Idan Aka Cire Bangaren Man Fetur Kannywood Ce Ta Fi Samar Da Aikin Yi Ga Matasa —Hamisu Iyantama

Idan Aka Cire Bangaren Man Fetur Kannywood Ce Ta Fi Samar Da Aikin Yi Ga Matasa —Hamisu Iyantama

July 25, 2026
Kogin Kumadugu Ya Yi Ambaliya Karon Farko Cikin Shekara 100 A Yobe

Jihohi 28 Da Abuja Na Fuskantar Hadarin Ambaliyar Ruwa —Rahoto

July 25, 2026
2023

Ƴan Bindiga Sun Sace Shugaban Ƙaramar Hukumar Bungudu

July 25, 2026
Yadda Jami’an Tsaro Suka Fatattaki ’Yan Ta’adda A Wasu Jihohin Nijeriya, Sun Kama ‘Yan Kasar Pakistan Bakwai

Yadda Jami’an Tsaro Suka Fatattaki ’Yan Ta’adda A Wasu Jihohin Nijeriya, Sun Kama ‘Yan Kasar Pakistan Bakwai

July 25, 2026
2023

Obasanjo Da Atiku Sun Sake Musayar Zafafan Kalaman Zargin Juna

July 25, 2026
Manufofin Tattalin Arzikin Gwamnatin Tinubu Sun Lalata Rayukan Al’ummar Nijeriya —ADC

Manufofin Tattalin Arzikin Gwamnatin Tinubu Sun Lalata Rayukan Al’ummar Nijeriya —ADC

July 25, 2026
An Karrama Masana Ilimin Lissafi Na Kasar Sin Da Lambobin Yabo Na Fields Medal

An Karrama Masana Ilimin Lissafi Na Kasar Sin Da Lambobin Yabo Na Fields Medal

July 24, 2026
Ta Da Zaune Tsaye Da Philippines Ta Yi A Teku Ba Zai Lalata Dangantakar Hadin Gwiwar Sin Da ASEAN Ba

Ta Da Zaune Tsaye Da Philippines Ta Yi A Teku Ba Zai Lalata Dangantakar Hadin Gwiwar Sin Da ASEAN Ba

July 24, 2026
Jadawalin INEC:Kotun Daukaka Kara Ta Kassara Fatan Jam’iyyu Da ‘Yan Siyasa

Jadawalin INEC:Kotun Daukaka Kara Ta Kassara Fatan Jam’iyyu Da ‘Yan Siyasa

July 24, 2026
An Zartas Da Sanarwar Chengdu A Taron Ministocin Kungiyar APEC Kan Harkar Raya Fasahohin Dijital Da AI

An Zartas Da Sanarwar Chengdu A Taron Ministocin Kungiyar APEC Kan Harkar Raya Fasahohin Dijital Da AI

July 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.