ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, July 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: A Shirye Muke Mu Bude Kofar Kulla Kawance Da Sauran Jam’iyyu Kafin Zabe –NNPP

jam’iyyar NNPP ba ta kyamar tattaunawa don gina kasa.

by Muhammad
4 years ago
2023

Shugaban jam’iyyar NNPP na kasa, Rufa’i Alkali, a ranar Larabar, ya bayyana cewa jam’iyyar a shirye take ta hada kai da wasu Jam’iyyun siyasa kafin zaben 2023 mai zuwa.

Mista Alkali, mai baiwa tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan shawara ne kan harkokin siyasa, ya bayyana hakan a Legas a wani taron manema labarai.

  • Rikicin NNPP: Kwankwaso Ya Ci Amanarmu – Shekarau
  • Dalilin Da Yasa Ban Halarci Taron NBA Ba – Kwankwaso 

A cewarsa, jam’iyyar ba ta kyamar tattaunawa don gina kasa.

ADVERTISEMENT

“Jam’iyyun da ke son tattaunawa da jam’iyyar NNPP ba aibu ba ne su yi hakan a don samar da tafiya daya mai karfi, kuma dole ne mu bayyana ra’ayoyinmu kan makomar kasar nan.

“Dukkan jam’iyyu daidai suke a gaban doka.

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ya Naɗa Kenneth Okonkwo A Matsayin Kakakin Yaƙin Neman Zaɓensa

‘Yan Adawa Sun Mayar Da Matsalar Tsaro Siyasa – Yusuf Gagdi

“Muna magana ne game da makomar Nijeriya,” in ji Mista Alkali, tsohon sakataren yada labaran jam’iyyar PDP na kasa.

Ya kuma yi tir da yadda ake tafiyar da harkokin siyasa a Nijeriya, yana mai cewa bai kamata mutane su zo a tattauna a fitar da dan takara daya tilo.

Tattaunawar kawance tsakanin jam’iyyun NNPP da Labour ta tsawon makonni ta gaza haifar da sakamako, shi ya sa ‘yan takarar shugaban kasa na jam’iyyun biyu – Mista Kwankwaso da Peter Obi – suka bayyana a matsayin ‘yan takara.

Alkali ya ce idan wata jam’iyya ta zauna don tattaunawa, dole ne su fara kokarin fahimtar kansu: mene ne suke da alaka da su – akida, hangen nesa, buri da kuma manufofin yin aiki tare.

Ya kara da cewa ya kamata jam’iyyu su amince da matakin kawance ko dai a majalisar wakilai, wakilai, dattijai, gwamna ko shugaban kasa.

“A siyasa muna magana ne game da kwazon aiki.”

Shugaban, ya ce Nijeriya ba za ta iya yin kuskure a 2023 ba, yana mai cewa jam’iyyar NNPP za ta bullo da sabbin dabarun gina tattalin arzikin kasa idan aka zabe shi.

Ya kara da cewa “NNPP tana wa Nijeriya shiri kuma za su kawo sauyi ga al’amuran siyasar kasar.”

Ya kara da cewa jam’iyyar NNPP ta kasance jam’iyyar siyasa mafi girma a Nijeriya kuma nan ba da dadewa ba za ta samu goyon bayan mafi yawan ‘yan Nijeriya a fadin kasar.

Ya ce jam’iyyar NNPP za ta ci gaba da bin ka’idojinta na inganta rayuwar talakawan Nijeriya.

“Abin da Nijeriya ke bukata shi ne shugabancin da mutane za su amince da su kuma za su samar,” in ji Alkali, farfesa a fannin kimiyyar siyasa da tattalin arziki.

Akan tikitin takarar musulmi da musulmi, shugaban ya ce hakkin dan takara ne ya zabi abokin takararsa, yana mai cewa abin da ya kamata ya fi dacewa shi ne tunkarar kalubalen Nijeriya.

Ya kara da cewa: “Idan muna son kasar nan ta canza dole ne mu wuce batun maganar yankin yanki da tattaunawa kan addini.

“Mun wuce matakin sabani na yanki da ra’ayin addini.” (NAN)

2023
Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Cikin Shekaru 28, Kudiri Ƙasa Da 10 Sanatocin Zamfara Ta Arewa Suka Gabatar A Majalisa – Shinkafi
  • Muhammad
    2027: NNPP Ta Yi Wa Korarrun Mambobinta Afuwa, Ta Yi Alƙawarin Basu Tikitin Kai-tsaye
  • Muhammad
    Musulunci Na Fuskantar Barazana A Karƙashin Mulkin Tinubu — Datti Baba-Ahmed
  • Muhammad
    Kwankwaso Tamkar Tsuntsu Ne A Siyasa Da Yake Sauya Sheƙa Daga Nan Zuwa Can – Ganduje

MASU ALAKA

Atiku
Siyasa

Atiku Ya Naɗa Kenneth Okonkwo A Matsayin Kakakin Yaƙin Neman Zaɓensa

July 2, 2026
‘Yan Adawa Sun Mayar Da Matsalar Tsaro Siyasa – Yusuf Gagdi
Manyan Labarai

‘Yan Adawa Sun Mayar Da Matsalar Tsaro Siyasa – Yusuf Gagdi

July 1, 2026
Majalisa Na Binciken Kwangilar Titin Naira Biliyan 1.46 Da Aka Yi Watsi Da Shi A Kaduna
Siyasa

Tinubu Ya Shimfiɗa Wa Arewacin Nijeriya Ayyuka Sama Da Kowane Shugaban Ƙasa – Uba Sani

July 1, 2026
Next Post
Rikicin PDP: Bayan Ganawar Tinubu Da Wike A Landan, Ba Shiri Atiku Ya Garzaya Birtaniya

Rikicin PDP: Bayan Ganawar Tinubu Da Wike A Landan, Ba Shiri Atiku Ya Garzaya Birtaniya

LABARAI MASU NASABA

Dakarun Tsaron Teku Na Sin Na Ci Gaba Da Sintirin Wanzar Da Doka A Yankunan Ruwa Na Gabashin Tsibirin Taiwan

Dakarun Tsaron Teku Na Sin Na Ci Gaba Da Sintirin Wanzar Da Doka A Yankunan Ruwa Na Gabashin Tsibirin Taiwan

July 4, 2026
Wasu Matasa Amurkawa Sun Ziyarci Sin Don Kara Fahimtar Kasar

Wasu Matasa Amurkawa Sun Ziyarci Sin Don Kara Fahimtar Kasar

July 4, 2026
Wakilin CMG Ya Zanta Da Mataimakin Shugaban Kasar Afirka Ta Kudu

Wakilin CMG Ya Zanta Da Mataimakin Shugaban Kasar Afirka Ta Kudu

July 4, 2026
CAF Ta Gayyaci Ƙasashen Afirka Su Nemi Ɗaukar Nauyin Gasar AFCON Ta 2028, 2032 da 2036

CAF Ta Gayyaci Ƙasashen Afirka Su Nemi Ɗaukar Nauyin Gasar AFCON Ta 2028, 2032 da 2036

July 4, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Jinjina Wa Shugaban NAHCON Kan Nasarar Aikin Hajjin 2026

Gwamnatin Zamfara Ta Jinjina Wa Shugaban NAHCON Kan Nasarar Aikin Hajjin 2026

July 4, 2026
Tawaga Ta Biyu Ta Kwararrun Kasar Sin Ta Sauka A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo Domin Karfafa Yaki Da Cutar Ebola

Tawaga Ta Biyu Ta Kwararrun Kasar Sin Ta Sauka A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo Domin Karfafa Yaki Da Cutar Ebola

July 4, 2026
Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina

Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina

July 4, 2026
Babban Dan Majalissar Dokokin Kasar Sin Ya Halarci Jana’izar Marigayi Jagoran Addini Na Iran

Babban Dan Majalissar Dokokin Kasar Sin Ya Halarci Jana’izar Marigayi Jagoran Addini Na Iran

July 4, 2026
Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

July 4, 2026
Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

July 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.