• English
  • Business News
Wednesday, October 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Dan Takarar Gwamnan PDP Ya Kaddamar Da Kwamitin Kamfe A Kebbi

by Umar Faruk
3 years ago
PDP

Dan takarar gwamna na jam’iyyar PDP, Manjo-Janar Aminu Bande (mai ritaya), ya kaddamar da kwamitin kamfe dinsa a Birnin Kebbi, babban birnin Jihar Kebbi.

Janar Aminu Bande a cikin jawabinsa ya yi alkawarin gudanar da dunkulalliyar gwamnati idan aka zabe shi a zaben 2023 mai zuwa a matsayin gwamnan Jihar kebbi.

  • Ganduje Ya Kaddamar Da Manyan Motocin Sufuri 100 Da Kanana 50 A Kano
  • Wani Harin Bam Ya Yi Sanadin Kashe Aƙalla Mutum 100 A Somaliya

Bande ya ce, “Takararta ba don son rai ba ce, a’a, don ci gaban jihar cikin gaggawa ne.”

Haka kuma ya yi alkawarin yin adalci ga kowace irin al’umma a fadin jihar ba tare da la’akari da addini, kabila da jam’iyya ba da nufin kai jihar ga wani babban mataki da kuma na ci gaba.

Dan takarar ya bukaci ’yan kwamiti yakin neman zaben da su dauki wani sabon salo na yakin neman zabe wanda kowane shugaba da kowane mamba zai kawo da rumfunansa ko rumfarsa na zabe a mazabar da ya ke jefa kuri’a, inda ya kara da cewa duk wanda bai iya kawo rumfar zabensa ba, to bai cancanci zama dan majalisar yakin neman zabensa ba ko yana da wani tasiri ga siyasa ba a yankinsu ko karamar hukumarsu.

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Diri Da ’Yan Majalisa 23 Na Bayelsa Sun Fice Daga PDP

2027: Babu Ɗan Siyasar Da Zai Iya Ƙalubalantar Tinubu — Fadar Shugaban Ƙasa

Kazalika, ya shaida wa taron cewa, “Idan masu rike da madafun iko suka kawo musu kudi su karba, domin naku ne, amma ku tabbatar kun zabe Jam’iyyar PDP domin samun zaman lafiya, ci gaba da kawo canji a jihar Kebbi da Nijeriya baki daya.”

A nasa jawabin shugaban Majalisar yakin neman zaben Gwamnan Jihar Kebbi, Alhaji Abubakar Shehu-Geda ya yi kira ga ’yan kwamiti da su jajirce da kuma nuna kwazo wajen ganin Jam’iyyar PDP ta lashe dukkan mukamai na zaben 2023 mai zuwa a Jihar kebbi da na shugaban kasa.

Ya bayyana jin dadin yadda dukkan jiga-jigan siyasa a jihar Kebbi sun hallara, don haka ya tabbatar da cewa PDP ta riga ta lashe zabe a Jihar ta Kebbi da yardar Allah.

Kazalika, Shehu-Geda ya nemi goyon baya da hadin kan kowa da kowa domin samun nasarar zabe a fadin jihar.

Alhaji Bala tsohon shugaban jam’iyyar APC a jihar ya ce: “Yanzu na gamsu cewa PDP ta riga ta lashe dukkan mukaman zabe duba da irin manyan da na gani a nan.

“Duk da haka, ina so in roki dukkan ku da ku koma gida ku shawo kan jama’ar ku don su zabi jam’iyyarmu ta PDP a dukkan mukamai na zaben 2023.”

A nasa bangaren kwamishinan hukumar kula da tasrin gurabun daukar aikin gwamnati na tarayya mai wakiltar jihar Kebbi, Alhaji Abubakar Atiku-Bubu ya bukaci sauran jam’iyyun siyasa da su gudanar da yakin neman zabensu cikin tsafta da kuma limana da kwanciyar hankali batare da wata fitina ba.

Ya ce sun yanke shawarar kafa tanti da PDP ganin yadda tsohon Janar din ya kasance a jam’iyyar ne domin ya kawo hayyaci da kuma canjin da ake so a jihar Kebbi.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwamna Diri Da ’Yan Majalisa 23 Na Bayelsa Sun Fice Daga PDP
Da ɗumi-ɗuminsa

Gwamna Diri Da ’Yan Majalisa 23 Na Bayelsa Sun Fice Daga PDP

October 15, 2025
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Manyan Labarai

2027: Babu Ɗan Siyasar Da Zai Iya Ƙalubalantar Tinubu — Fadar Shugaban Ƙasa

October 15, 2025
Dalilin Da Ya Sa Mutane Ke Dawowa Jam’iyyar APC — Shettima
Manyan Labarai

Dalilin Da Ya Sa Mutane Ke Dawowa Jam’iyyar APC — Shettima

October 15, 2025
Next Post
Gwamnan Kebbi Ya Umarci A Biya Biliyan 2 Kudin Hutun Ma’aikata 

Gwamnan Kebbi Ya Umarci A Biya Biliyan 2 Kudin Hutun Ma'aikata 

LABARAI MASU NASABA

Yajin Aikin: Ɗalibai Sun Bai Wa ASUU Da Gwamnatin Tarayya Wa’adin Kwana 7 Su Warware Rikicinsu

Yajin Aikin: Ɗalibai Sun Bai Wa ASUU Da Gwamnatin Tarayya Wa’adin Kwana 7 Su Warware Rikicinsu

October 15, 2025
Gwamna Diri Da ’Yan Majalisa 23 Na Bayelsa Sun Fice Daga PDP

Gwamna Diri Da ’Yan Majalisa 23 Na Bayelsa Sun Fice Daga PDP

October 15, 2025
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

2027: Babu Ɗan Siyasar Da Zai Iya Ƙalubalantar Tinubu — Fadar Shugaban Ƙasa

October 15, 2025
Tinubu Ya Nemi Jihohi Su Dakatar Da Karbar Haraji A Kan Masu Safarar Kayan Abinci

Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba Barazana Ce Ga Tsaro A Yammacin Afirka – Tinubu

October 15, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Hana Manoma Girbi A Zamfara, Al’umma Na Neman Taimako

October 15, 2025
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

‘Yansanda Sun Kama Mutum 105, Sun Ƙwato Ƙwayoyi Sama Da 5,000 A Jigawa

October 15, 2025
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

Sojoji Sun Ceto Mutum 9 Da Aka Sace A Kwara

October 15, 2025
Dalilin Da Ya Sa Mutane Ke Dawowa Jam’iyyar APC — Shettima

Dalilin Da Ya Sa Mutane Ke Dawowa Jam’iyyar APC — Shettima

October 15, 2025
Ma’aikatar Kasuwancin Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Shiga Tattaunawar Cinikayya Da Sahihiyar Zuciya

Ma’aikatar Kasuwancin Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Shiga Tattaunawar Cinikayya Da Sahihiyar Zuciya

October 14, 2025
Uwar Gidan Shugaban Sin Ta Ziyarci Wajen Nune-nunen Karfafawa Mata Gwiwa A Bangaren Fasahohin Zamani

Uwar Gidan Shugaban Sin Ta Ziyarci Wajen Nune-nunen Karfafawa Mata Gwiwa A Bangaren Fasahohin Zamani

October 14, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.