ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Dan Takarar Gwamnan PDP Ya Kaddamar Da Kwamitin Kamfe A Kebbi

by Umar Faruk
4 years ago
PDP

Dan takarar gwamna na jam’iyyar PDP, Manjo-Janar Aminu Bande (mai ritaya), ya kaddamar da kwamitin kamfe dinsa a Birnin Kebbi, babban birnin Jihar Kebbi.

Janar Aminu Bande a cikin jawabinsa ya yi alkawarin gudanar da dunkulalliyar gwamnati idan aka zabe shi a zaben 2023 mai zuwa a matsayin gwamnan Jihar kebbi.

  • Ganduje Ya Kaddamar Da Manyan Motocin Sufuri 100 Da Kanana 50 A Kano
  • Wani Harin Bam Ya Yi Sanadin Kashe Aƙalla Mutum 100 A Somaliya

Bande ya ce, “Takararta ba don son rai ba ce, a’a, don ci gaban jihar cikin gaggawa ne.”

ADVERTISEMENT

Haka kuma ya yi alkawarin yin adalci ga kowace irin al’umma a fadin jihar ba tare da la’akari da addini, kabila da jam’iyya ba da nufin kai jihar ga wani babban mataki da kuma na ci gaba.

Dan takarar ya bukaci ’yan kwamiti yakin neman zaben da su dauki wani sabon salo na yakin neman zabe wanda kowane shugaba da kowane mamba zai kawo da rumfunansa ko rumfarsa na zabe a mazabar da ya ke jefa kuri’a, inda ya kara da cewa duk wanda bai iya kawo rumfar zabensa ba, to bai cancanci zama dan majalisar yakin neman zabensa ba ko yana da wani tasiri ga siyasa ba a yankinsu ko karamar hukumarsu.

LABARAI MASU NASABA

2027: ADC Ta Fara Sulhunta Mambobinta Da Ba Su Gamsu Da Zaɓen Fidda Gwani Ba A Kaduna

A Ƙarshe Jamilu Gwamna Ya Samu Babbar Dama Ta Yin Takara

Kazalika, ya shaida wa taron cewa, “Idan masu rike da madafun iko suka kawo musu kudi su karba, domin naku ne, amma ku tabbatar kun zabe Jam’iyyar PDP domin samun zaman lafiya, ci gaba da kawo canji a jihar Kebbi da Nijeriya baki daya.”

A nasa jawabin shugaban Majalisar yakin neman zaben Gwamnan Jihar Kebbi, Alhaji Abubakar Shehu-Geda ya yi kira ga ’yan kwamiti da su jajirce da kuma nuna kwazo wajen ganin Jam’iyyar PDP ta lashe dukkan mukamai na zaben 2023 mai zuwa a Jihar kebbi da na shugaban kasa.

Ya bayyana jin dadin yadda dukkan jiga-jigan siyasa a jihar Kebbi sun hallara, don haka ya tabbatar da cewa PDP ta riga ta lashe zabe a Jihar ta Kebbi da yardar Allah.

Kazalika, Shehu-Geda ya nemi goyon baya da hadin kan kowa da kowa domin samun nasarar zabe a fadin jihar.

Alhaji Bala tsohon shugaban jam’iyyar APC a jihar ya ce: “Yanzu na gamsu cewa PDP ta riga ta lashe dukkan mukaman zabe duba da irin manyan da na gani a nan.

“Duk da haka, ina so in roki dukkan ku da ku koma gida ku shawo kan jama’ar ku don su zabi jam’iyyarmu ta PDP a dukkan mukamai na zaben 2023.”

A nasa bangaren kwamishinan hukumar kula da tasrin gurabun daukar aikin gwamnati na tarayya mai wakiltar jihar Kebbi, Alhaji Abubakar Atiku-Bubu ya bukaci sauran jam’iyyun siyasa da su gudanar da yakin neman zabensu cikin tsafta da kuma limana da kwanciyar hankali batare da wata fitina ba.

Ya ce sun yanke shawarar kafa tanti da PDP ganin yadda tsohon Janar din ya kasance a jam’iyyar ne domin ya kawo hayyaci da kuma canjin da ake so a jihar Kebbi.

PDP
Umar Faruk
+ postsBio
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk-2/
    Nijeriya Da Jamhuriyar Benin Za Su Sassauta Tsanantawa A Kan Iyakokinsu Ga ‘Yan Kasuwa
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk-2/
    Hajjin Bana: Shettima Zai Kaddamar Da Jirgin Farko Na Maniyyata 430 A Kebbi
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk-2/
    Jami’an Tsaro sun Ceto Mata Biyu da aka Yi Garkuwa da Su A Kebbi
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk-2/
    Majalisar Dokokin Kebbi Ta Dakatar Da Dan Majalisa Mai Wakiltar Birnin Kebbi Ta Arewa

MASU ALAKA

ADC Ta Fara Sayar Da Fom Din Takara Kafin Babban Taron Jam’iyya
Siyasa

2027: ADC Ta Fara Sulhunta Mambobinta Da Ba Su Gamsu Da Zaɓen Fidda Gwani Ba A Kaduna

June 9, 2026
A Ƙarshe Jamilu Gwamna Ya Samu Babbar Dama Ta Yin Takara
Siyasa

A Ƙarshe Jamilu Gwamna Ya Samu Babbar Dama Ta Yin Takara

June 8, 2026
Shugabannin NDC Na Arewa Maso Yamma Sun Zargi Kwankwaso Da Ƙoƙarin Babakere
Siyasa

Shugabannin NDC Na Arewa Maso Yamma Sun Zargi Kwankwaso Da Ƙoƙarin Babakere

June 8, 2026
Next Post
Gwamnan Kebbi Ya Umarci A Biya Biliyan 2 Kudin Hutun Ma’aikata 

Gwamnan Kebbi Ya Umarci A Biya Biliyan 2 Kudin Hutun Ma'aikata 

LABARAI MASU NASABA

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

June 13, 2026
Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.