• English
  • Business News
Wednesday, May 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Gudummawar Da Ya kamata Jami’an Tsaro Su Bayar

by Leadership Hausa
2 years ago
in Manyan Labarai, Rahotonni
0
2023: Gudummawar Da Ya kamata Jami’an Tsaro Su Bayar
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwanakin baya Shugaba Muhammadu Buhari, a wani taro da ya halarta a Owerri na Jihar Imo, ya nemi rundunar ‘yansandan Nijeriya su samar da cikakken tsarin da zai kai ga samar da sahihin sakamakon zabe a 2023, ya kuma nemi su nisanta kansu daga harkokin siyasa su kuma tabbatar da tsayuwa wajen kare tsarin dimokradiyya.

Shugaba Buhari ya bude taron kwanaki uku ne na horas da manyan hafsoshin jami’an ‘yansanda, inda ya bukaci a sake nazarin yadda suke gudanar da ayyukansu musamman ganin bazanar tsaron da ake fuskanta a halin yanzu don haka yakamata su jajirce wajen ganin an gudanar da sahihin zabe a shekasrar 2023.

  • Ana Baje Kolin Shirye-Shiryen CMG A Taron Kafofin Watsa Labaran Kasa Da Kasa Karo Na Farko
  • 2023: Wike Zai Goyi Bayan Peter Obi Ya Yi Watsi Da Takarar Atiku

Shugaba Buhari ya kuma lura da cewa, sai fa in kuri’un al’umma sun yi tasiri a zabe kafin al’umma su samu kwanciyar hankali tare da rungumar gwamnatin da ta samu nasara.

Ya kuma kara da cewa, za a iya tabbatar da hakan ne ta hanyar samar da cikakken kwarraru jami’an ‘yansanda da suka san ayyukansu suka kuma gudanar da aikin naka ba tare da nuna son rai ba.

‘A kan haka ne, nike umartar Babban Sufeton ‘yansanda da ya samar da shugabanci nagari tare da ba kowa hakkin gudanar da harkokinsa na siyasa, ta haka al’umma za su rungumi duk wanda ya samu nasara don yana nuna abin da al’umma suka zaba ke nan,” in ji shi.

Labarai Masu Nasaba

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

Tabbas nasara ko rashin nasarar zaben 2023 ya danganta ne da yadda jami’an tsaronmu suka gudanar da ayyyukansu musamman ma ‘yansanda.

Haka kuma a bayyana yake cewa, Hukumar Zabe INEC tana kokarin samar da sabbin hanyoyi na zaman don gudanar da harkokin zabe.

Muna sane da yadda INEC ta samar da na’urar ‘Card Reader’, ‘BBAS’ da kuma hanyoyin aikawa da sakamakon zabe ta na’ura, mai kwakwalwa. Wadanda sun taimaka wajen dakile ayyyukan ‘yan banga, satar akwatin zabe, da yadda a wasu lokutta ake samun mutane na kada kuri’a fiye da sau daya, wanda hakan ya yi matukar taimakawa wajen kara wa sakamakon zabukka mutunci.

Duk da cewa, wadannan na’u’roriun ba bai ba za a iya karkatar da sub a ne anmma sun taimaka kwarai da gaske wajen tabbatar da wadanda al’umma suka zaba ne suka kai ga samu nasara a zabukkan da aka gudanar a ‘yan shekarun nan.

Abin taikaici a nan shi ne duk da irin kokarin da INEC ta ke yi, ‘yansiyasa na nan suna neman wasu hanyoyin gudanar da ayuukjansu na magudi a lokuttan zabe.

Cikin manyan matsalolin da harkokin zabe ke fuskanta a kasar nan shi ne yadda ba a bari al’umma su zabi wanda suke so ya mulke a dukkan matakai don kuwa masu kudi ke kwace harkar zabe inda suke dankarawa mutanen da suke so a kan al’umma don su biya musu bukata yayin da suka kai ga kujerar mulkin a dukkan matakai.

Wannan halayyar ta haifar da shugabanin da basu iya gudanar da mulki ba, basa kuma sa al’amarin al’umma a gaban su. Dole Nijeriya ta kauce ma wannan hanyar don babu wani cigaba da za a samu tare da bin wannan tsarin gaba daya.

Abin dadada rai anan shi ne yadda Shugaban Kasa Muhammdu Buhari ya yi alkawarin tabbatar da ya bar tarihin gudanar da sahihin zabe ba tare da cutar da wani bangare ba kamar yadda aka gudanar da zabukkan jihohin Ekiti, Osun, da Anambra, hakan kuma ya sanya wa ‘yan Nijeriya da dama sun fara gaskata Shugaba Buhari a kan wannan alkawari nasa.

Amma wani abin da aka lura da shi a zabukkan jihohin Ekiti da Osun shi ne batun nan na sayen kuri’a, wannan kuma yana neman ya karya daraja da mutuncin zabukkan da aka gudanar a ‘yan tsakanin nan.

Ra’ayin wannan jarifar shi ne, tabbas lamarin sayen kuri’a ya matukar karuwa hakan kuma na faruwa ne saboda yadda jami’an tsaro suka kasa kamawa tare da hukunta masu wannan mummunan sana’a, dole a kawo karshen wannan lamarin a nan take. Dole ne ‘yansnanda su yi aikinsu a kan masu saye da sayar da kuri’ar koda kuwa wane ne.

Tabbas, al’umma da dama kan yi tunanin cewa, ‘yansanda kan goyi bayan gwamnati a dukkan zabukkan da ake yi ne, wannan kuma yana faruwa ne saboda haka lamarin yake a zabukkan da aka gudanar a shekarun baya. Ba haka lamarin ya kamata ya kasance ba. Sukan kawar da fuskokinsu su yayin da jami’an gwamnati ke harkar sayen kuri’u a lokacin zabe. Cikin manyan dalilin haka shi ne don gwamantin tarayyar ke tanadar wa jami’an tsaron kudin gudanar da ayyuykansu.

Muna iyan tunawa da cewa, Babban Sufeton ‘Yansanda, Alkali Usman Baba, ya tabbatar wa da shugaban Nijeriya cewa, rundunar za ta yi amfani da sakamakon taron wajen samar da cikakken tsarin tsaron da jami’anta za su yi amfani da su don samar da sahihin zabe, ta haka za a tabbatar da tsarin mulkin dimokradiyya da kasar nan ta doru a kai.

Ya yi alkawarin cewa, tsarin da za su fito da shi zai karfafa tsarin zaben kasa ta yadda al’umma za su karbi sakamakoin zaben 2023 ba tare da wata matsala ba.

Ra’ayin wannan jaridar na tare da shugaban kasa inda ya nemi cewa, ya kamata sakamakon zabukkan 2023 ya zama abin da al’umma suka zaba ne, dole a gudanar da sahihin zabe da zai samu karbuwa ga dukkan al’umma. Wannan shi ne sirrin dimokradiyya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: gudunmawaJami'an Tsaro. 2023. Buhari
ShareTweetSendShare
Previous Post

Da Dumi-Duminsa: Buhari Ya Tsige Fadah A Matsayin Darakta Janar Na NYSC

Next Post

Oramah, Marwa, Amusan Sun Yi Nasarar Zama Gwarazan Kamfanin LEADERSHIP A 2022

Related

JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu
Manyan Labarai

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

17 minutes ago
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya
Manyan Labarai

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

5 hours ago
Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte
Manyan Labarai

Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

9 hours ago
Ko Kanawa Za Su Yafe Wa Ganduje?
Manyan Labarai

Kotu Ta Ce Za A Ci Gaba Da Shari’ar Ganduje Kan Zargin Aikata Rashawa A Kano

10 hours ago
Gwamnan Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar
Manyan Labarai

Gwamnan Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar

1 day ago
Wata Mata Ta Kashe Dan Hayar Da Ke Gidanta A Ondo
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban APC A Ondo, Sun Nemi N100m

1 day ago
Next Post
Jami'an Tsaro

Oramah, Marwa, Amusan Sun Yi Nasarar Zama Gwarazan Kamfanin LEADERSHIP A 2022

LABARAI MASU NASABA

JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

May 14, 2025
Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata

Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata

May 14, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

May 14, 2025
Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

May 14, 2025
Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

May 14, 2025
Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

May 14, 2025
‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 239, Sun Ƙwato Makamai Da Alburusai A Kogi

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 239, Sun Ƙwato Makamai Da Alburusai A Kogi

May 14, 2025
Dakarun Soji Sun Daƙile Wani Sabon Harin ISWAP A Dikwa

Dakarun Soji Sun Daƙile Wani Sabon Harin ISWAP A Dikwa

May 14, 2025
Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.