• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Gudummawar Da Ya kamata Jami’an Tsaro Su Bayar

by Leadership Hausa
3 years ago
in Manyan Labarai, Rahotonni
0
2023: Gudummawar Da Ya kamata Jami’an Tsaro Su Bayar
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwanakin baya Shugaba Muhammadu Buhari, a wani taro da ya halarta a Owerri na Jihar Imo, ya nemi rundunar ‘yansandan Nijeriya su samar da cikakken tsarin da zai kai ga samar da sahihin sakamakon zabe a 2023, ya kuma nemi su nisanta kansu daga harkokin siyasa su kuma tabbatar da tsayuwa wajen kare tsarin dimokradiyya.

Shugaba Buhari ya bude taron kwanaki uku ne na horas da manyan hafsoshin jami’an ‘yansanda, inda ya bukaci a sake nazarin yadda suke gudanar da ayyukansu musamman ganin bazanar tsaron da ake fuskanta a halin yanzu don haka yakamata su jajirce wajen ganin an gudanar da sahihin zabe a shekasrar 2023.

  • Ana Baje Kolin Shirye-Shiryen CMG A Taron Kafofin Watsa Labaran Kasa Da Kasa Karo Na Farko
  • 2023: Wike Zai Goyi Bayan Peter Obi Ya Yi Watsi Da Takarar Atiku

Shugaba Buhari ya kuma lura da cewa, sai fa in kuri’un al’umma sun yi tasiri a zabe kafin al’umma su samu kwanciyar hankali tare da rungumar gwamnatin da ta samu nasara.

Ya kuma kara da cewa, za a iya tabbatar da hakan ne ta hanyar samar da cikakken kwarraru jami’an ‘yansanda da suka san ayyukansu suka kuma gudanar da aikin naka ba tare da nuna son rai ba.

‘A kan haka ne, nike umartar Babban Sufeton ‘yansanda da ya samar da shugabanci nagari tare da ba kowa hakkin gudanar da harkokinsa na siyasa, ta haka al’umma za su rungumi duk wanda ya samu nasara don yana nuna abin da al’umma suka zaba ke nan,” in ji shi.

Labarai Masu Nasaba

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Tabbas nasara ko rashin nasarar zaben 2023 ya danganta ne da yadda jami’an tsaronmu suka gudanar da ayyyukansu musamman ma ‘yansanda.

Haka kuma a bayyana yake cewa, Hukumar Zabe INEC tana kokarin samar da sabbin hanyoyi na zaman don gudanar da harkokin zabe.

Muna sane da yadda INEC ta samar da na’urar ‘Card Reader’, ‘BBAS’ da kuma hanyoyin aikawa da sakamakon zabe ta na’ura, mai kwakwalwa. Wadanda sun taimaka wajen dakile ayyyukan ‘yan banga, satar akwatin zabe, da yadda a wasu lokutta ake samun mutane na kada kuri’a fiye da sau daya, wanda hakan ya yi matukar taimakawa wajen kara wa sakamakon zabukka mutunci.

Duk da cewa, wadannan na’u’roriun ba bai ba za a iya karkatar da sub a ne anmma sun taimaka kwarai da gaske wajen tabbatar da wadanda al’umma suka zaba ne suka kai ga samu nasara a zabukkan da aka gudanar a ‘yan shekarun nan.

Abin taikaici a nan shi ne duk da irin kokarin da INEC ta ke yi, ‘yansiyasa na nan suna neman wasu hanyoyin gudanar da ayuukjansu na magudi a lokuttan zabe.

Cikin manyan matsalolin da harkokin zabe ke fuskanta a kasar nan shi ne yadda ba a bari al’umma su zabi wanda suke so ya mulke a dukkan matakai don kuwa masu kudi ke kwace harkar zabe inda suke dankarawa mutanen da suke so a kan al’umma don su biya musu bukata yayin da suka kai ga kujerar mulkin a dukkan matakai.

Wannan halayyar ta haifar da shugabanin da basu iya gudanar da mulki ba, basa kuma sa al’amarin al’umma a gaban su. Dole Nijeriya ta kauce ma wannan hanyar don babu wani cigaba da za a samu tare da bin wannan tsarin gaba daya.

Abin dadada rai anan shi ne yadda Shugaban Kasa Muhammdu Buhari ya yi alkawarin tabbatar da ya bar tarihin gudanar da sahihin zabe ba tare da cutar da wani bangare ba kamar yadda aka gudanar da zabukkan jihohin Ekiti, Osun, da Anambra, hakan kuma ya sanya wa ‘yan Nijeriya da dama sun fara gaskata Shugaba Buhari a kan wannan alkawari nasa.

Amma wani abin da aka lura da shi a zabukkan jihohin Ekiti da Osun shi ne batun nan na sayen kuri’a, wannan kuma yana neman ya karya daraja da mutuncin zabukkan da aka gudanar a ‘yan tsakanin nan.

Ra’ayin wannan jarifar shi ne, tabbas lamarin sayen kuri’a ya matukar karuwa hakan kuma na faruwa ne saboda yadda jami’an tsaro suka kasa kamawa tare da hukunta masu wannan mummunan sana’a, dole a kawo karshen wannan lamarin a nan take. Dole ne ‘yansnanda su yi aikinsu a kan masu saye da sayar da kuri’ar koda kuwa wane ne.

Tabbas, al’umma da dama kan yi tunanin cewa, ‘yansanda kan goyi bayan gwamnati a dukkan zabukkan da ake yi ne, wannan kuma yana faruwa ne saboda haka lamarin yake a zabukkan da aka gudanar a shekarun baya. Ba haka lamarin ya kamata ya kasance ba. Sukan kawar da fuskokinsu su yayin da jami’an gwamnati ke harkar sayen kuri’u a lokacin zabe. Cikin manyan dalilin haka shi ne don gwamantin tarayyar ke tanadar wa jami’an tsaron kudin gudanar da ayyuykansu.

Muna iyan tunawa da cewa, Babban Sufeton ‘Yansanda, Alkali Usman Baba, ya tabbatar wa da shugaban Nijeriya cewa, rundunar za ta yi amfani da sakamakon taron wajen samar da cikakken tsarin tsaron da jami’anta za su yi amfani da su don samar da sahihin zabe, ta haka za a tabbatar da tsarin mulkin dimokradiyya da kasar nan ta doru a kai.

Ya yi alkawarin cewa, tsarin da za su fito da shi zai karfafa tsarin zaben kasa ta yadda al’umma za su karbi sakamakoin zaben 2023 ba tare da wata matsala ba.

Ra’ayin wannan jaridar na tare da shugaban kasa inda ya nemi cewa, ya kamata sakamakon zabukkan 2023 ya zama abin da al’umma suka zaba ne, dole a gudanar da sahihin zabe da zai samu karbuwa ga dukkan al’umma. Wannan shi ne sirrin dimokradiyya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: gudunmawaJami'an Tsaro. 2023. Buhari
ShareTweetSendShare
Previous Post

Da Dumi-Duminsa: Buhari Ya Tsige Fadah A Matsayin Darakta Janar Na NYSC

Next Post

Oramah, Marwa, Amusan Sun Yi Nasarar Zama Gwarazan Kamfanin LEADERSHIP A 2022

Related

Jami'an Tsaro
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

5 hours ago
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

9 hours ago
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano
Manyan Labarai

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

1 day ago
Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci
Rahotonni

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

1 day ago
Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

1 day ago
Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi
Manyan Labarai

Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi

1 day ago
Next Post
Jami'an Tsaro

Oramah, Marwa, Amusan Sun Yi Nasarar Zama Gwarazan Kamfanin LEADERSHIP A 2022

LABARAI MASU NASABA

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

June 7, 2025
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

June 7, 2025
Jami'an Tsaro

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

June 7, 2025
Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.