• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Gwamnan Yobe Ya Hori ‘Yan Siyasa Su Nesanci Kalaman Ta Da Zaune Tsaye

by Muhammad Maitela
3 years ago
in Labarai
0
Takarar Tinubu Da Shettima Babbar Nasarar APC Ce – Buni
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan jihar Yobe, Hon. Mai Mala Buni ya bukaci yan siyasa a jihar Yobe su guji kalaman da za su jawo tada zaune tsaye a lokutan yakin neman zaben da yake gudana a fadin kasar nan; musamman a jihar Yobe.

Gwamnan ya bayyana hakan ta bakin Babban Mai Taimaka masa ta kafafin sadarwa na zamani, Mallam Yusuf Ali, inda ya ce a matsayin Gwamna Buni ma’abucin son zaman lafiya da sasanci, wanda hakan ya sanya ake masa lakabi da ‘Limamin-sulhu’, ya bukaci yan siyasa su zauna lafiya a lokacin da suke gudanar da yakin neman zaben mai zuwa na 2023.

  • Gwamna Buni Ya Tallafawa Marayu 200 Da N50,000 Kowanne

Yusuf Ali ya kara da cewa, “Hon. Mai Mala Buni mutum ne mai matukar kaunar wanzuwar zaman lafiya da yaduwar fahimtar juna daga kowane bangaren al’ummar (yan siyasa).

Musamman a daidai lokacin da ake tunkarar zaben 2023, wanda abubuwan da za su sa a samu nasarar gudanar da zaben shi ne zaman lafiya. Yada maganganun gaba ko kiyayya a tsakanin al’umma ba zai haifar mana da-mai-ido ba, domin ko shakka babu dukkanin mu ‘ya’yan jihar Yobe ne, babu dalilin da zai sa mu rura wutar gaba ko kyama a tsakaninmu.”

Mallam Yusuf ya kara da cewa, kowane lokaci Gwmnan ya kan nanata muhimmancin zaman lafiya da fahimtar juna, wanda ko a kwanan baya, a sa’ilin da yake kaddamar da kasafin kudin wannan shekara a gaban Majalisar Dokokin jihar Yobe ya jadda batun ‘yan siyasa’ su guji kalaman da zasu kawo tashin-tashina ko kiyayya da makamantan su.

Labarai Masu Nasaba

Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

Gwamna ya ce, “Ina so na tunatar da mu cewa, a yayin da muke tunkarar babban zaben 2023, ya dace ace dokokin zabe na kasa su ne za su ci gaba da yi mana jagoranci, tare da kokari wajen abubuwan da za su kawo ma na hadin kai da zaman lafiya, tare da yin watsi da kalaman kiyayya ko tunzura jama’a.

Sannan mu na iya kasancewa ma su bambancin ra’ayin siyasa, amma wannan ba zai sanya mu kasance makiyan juna ba. A matsayinmu na ‘yan jihar Yobe, bai dace ace mun jefa kanmu a cikin tashin hankali da juna ba, domin wata bukatar son zuciyarka.”Gwamna Buni ya ce, “ina tabbatar muku da cewa, wannan gwamnati za ta ci gaba da aiki don tabbatar da zaman lafiya mai dorewa da ci gaban wannan jihar da na al’ummarmu baki daya.

Don haka, ina rokon ku, ku ci gaba da yin addu’o’i na musamman domin samun zaman lafiya da ci gaban jihar Yobe da ma kasarmu Nijeriya baki daya.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda ‘Hackers’ Ke Amfani Da Hanyar Smishing Wajen Yin Kutse

Next Post

Yadda Za Ki Tallata Kaya Ta Intanet

Related

Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 
Labarai

Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

3 hours ago
Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto
Labarai

Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

5 hours ago
Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo
Labarai

Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

5 hours ago
Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa
Labarai

Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

6 hours ago
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100
Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

8 hours ago
Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki
Manyan Labarai

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

11 hours ago
Next Post
Yadda Za Ki Tallata Kaya Ta Intanet

Yadda Za Ki Tallata Kaya Ta Intanet

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

June 29, 2025
2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu

2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu

June 29, 2025
Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya

Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya

June 29, 2025
Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

June 29, 2025
Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila

Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila

June 29, 2025
Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

June 29, 2025
Gyaran Tsarin Mulki: Majalisa Ta Shirya Sauraron Jin Ra’ayoyin Jama’a A Wasu Sassan Nijeriya

Gyaran Tsarin Mulki: Majalisa Ta Shirya Sauraron Jin Ra’ayoyin Jama’a A Wasu Sassan Nijeriya

June 29, 2025
Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

June 29, 2025
Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

June 29, 2025
Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

June 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.