• English
  • Business News
Tuesday, September 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Gwamnan Yobe Ya Hori ‘Yan Siyasa Su Nesanci Kalaman Ta Da Zaune Tsaye

by Muhammad Maitela
3 years ago
in Labarai
0
Takarar Tinubu Da Shettima Babbar Nasarar APC Ce – Buni
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan jihar Yobe, Hon. Mai Mala Buni ya bukaci yan siyasa a jihar Yobe su guji kalaman da za su jawo tada zaune tsaye a lokutan yakin neman zaben da yake gudana a fadin kasar nan; musamman a jihar Yobe.

Gwamnan ya bayyana hakan ta bakin Babban Mai Taimaka masa ta kafafin sadarwa na zamani, Mallam Yusuf Ali, inda ya ce a matsayin Gwamna Buni ma’abucin son zaman lafiya da sasanci, wanda hakan ya sanya ake masa lakabi da ‘Limamin-sulhu’, ya bukaci yan siyasa su zauna lafiya a lokacin da suke gudanar da yakin neman zaben mai zuwa na 2023.

  • Gwamna Buni Ya Tallafawa Marayu 200 Da N50,000 Kowanne

Yusuf Ali ya kara da cewa, “Hon. Mai Mala Buni mutum ne mai matukar kaunar wanzuwar zaman lafiya da yaduwar fahimtar juna daga kowane bangaren al’ummar (yan siyasa).

Musamman a daidai lokacin da ake tunkarar zaben 2023, wanda abubuwan da za su sa a samu nasarar gudanar da zaben shi ne zaman lafiya. Yada maganganun gaba ko kiyayya a tsakanin al’umma ba zai haifar mana da-mai-ido ba, domin ko shakka babu dukkanin mu ‘ya’yan jihar Yobe ne, babu dalilin da zai sa mu rura wutar gaba ko kyama a tsakaninmu.”

Mallam Yusuf ya kara da cewa, kowane lokaci Gwmnan ya kan nanata muhimmancin zaman lafiya da fahimtar juna, wanda ko a kwanan baya, a sa’ilin da yake kaddamar da kasafin kudin wannan shekara a gaban Majalisar Dokokin jihar Yobe ya jadda batun ‘yan siyasa’ su guji kalaman da zasu kawo tashin-tashina ko kiyayya da makamantan su.

Labarai Masu Nasaba

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Yanke Hutu, Zai Dawo Abuja Gobe Talata

Gwamna ya ce, “Ina so na tunatar da mu cewa, a yayin da muke tunkarar babban zaben 2023, ya dace ace dokokin zabe na kasa su ne za su ci gaba da yi mana jagoranci, tare da kokari wajen abubuwan da za su kawo ma na hadin kai da zaman lafiya, tare da yin watsi da kalaman kiyayya ko tunzura jama’a.

Sannan mu na iya kasancewa ma su bambancin ra’ayin siyasa, amma wannan ba zai sanya mu kasance makiyan juna ba. A matsayinmu na ‘yan jihar Yobe, bai dace ace mun jefa kanmu a cikin tashin hankali da juna ba, domin wata bukatar son zuciyarka.”Gwamna Buni ya ce, “ina tabbatar muku da cewa, wannan gwamnati za ta ci gaba da aiki don tabbatar da zaman lafiya mai dorewa da ci gaban wannan jihar da na al’ummarmu baki daya.

Don haka, ina rokon ku, ku ci gaba da yin addu’o’i na musamman domin samun zaman lafiya da ci gaban jihar Yobe da ma kasarmu Nijeriya baki daya.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda ‘Hackers’ Ke Amfani Da Hanyar Smishing Wajen Yin Kutse

Next Post

Yadda Za Ki Tallata Kaya Ta Intanet

Related

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 
Manyan Labarai

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

8 hours ago
Tinubu
Labarai

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Yanke Hutu, Zai Dawo Abuja Gobe Talata

9 hours ago
Sanata Natasha Za Ta Fuskanci Hukunci Daga Kwamitin Ɗa’a Na Majalisa
Labarai

Majalisar Dattawa Ce Kawai Za Ta Iya Dawo Da Sanata Natasha – Magatakardar Majalisa

10 hours ago
Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 
Labarai

Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 

11 hours ago
Neja
Labarai

Gwamnatin Neja Ta Musanta Rahoton Hana Da’awa A Jihar

12 hours ago
An Karrama Farfesa Adamu Gwarzo Kan Gudummawarsa Ga Bunƙasa Ilimin Jami’a A Nijeriya
Labarai

An Karrama Farfesa Adamu Gwarzo Kan Gudummawarsa Ga Bunƙasa Ilimin Jami’a A Nijeriya

12 hours ago
Next Post
Yadda Za Ki Tallata Kaya Ta Intanet

Yadda Za Ki Tallata Kaya Ta Intanet

LABARAI MASU NASABA

Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

September 15, 2025
Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

September 15, 2025
Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu

Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu

September 15, 2025
Tinubu

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Yanke Hutu, Zai Dawo Abuja Gobe Talata

September 15, 2025
Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”

Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”

September 15, 2025
Sanata Natasha Za Ta Fuskanci Hukunci Daga Kwamitin Ɗa’a Na Majalisa

Majalisar Dattawa Ce Kawai Za Ta Iya Dawo Da Sanata Natasha – Magatakardar Majalisa

September 15, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Shuka Kiyayya Da Tashin-Tashina A Tekun Kudancin Sin

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Shuka Kiyayya Da Tashin-Tashina A Tekun Kudancin Sin

September 15, 2025
Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 

Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 

September 15, 2025
Mujallar Qiushi Za Ta Wallafa Sharhin Xi Jinping Mai Taken “Zurfafa Dunkulewar Kasuwannin Kasa Ta Bai Daya”

Mujallar Qiushi Za Ta Wallafa Sharhin Xi Jinping Mai Taken “Zurfafa Dunkulewar Kasuwannin Kasa Ta Bai Daya”

September 15, 2025
Neja

Gwamnatin Neja Ta Musanta Rahoton Hana Da’awa A Jihar

September 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.