• English
  • Business News
Tuesday, August 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Gwamnan Yobe Ya Hori ‘Yan Siyasa Su Nesanci Kalaman Ta Da Zaune Tsaye

by Muhammad Maitela
3 years ago
in Labarai
0
Takarar Tinubu Da Shettima Babbar Nasarar APC Ce – Buni
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan jihar Yobe, Hon. Mai Mala Buni ya bukaci yan siyasa a jihar Yobe su guji kalaman da za su jawo tada zaune tsaye a lokutan yakin neman zaben da yake gudana a fadin kasar nan; musamman a jihar Yobe.

Gwamnan ya bayyana hakan ta bakin Babban Mai Taimaka masa ta kafafin sadarwa na zamani, Mallam Yusuf Ali, inda ya ce a matsayin Gwamna Buni ma’abucin son zaman lafiya da sasanci, wanda hakan ya sanya ake masa lakabi da ‘Limamin-sulhu’, ya bukaci yan siyasa su zauna lafiya a lokacin da suke gudanar da yakin neman zaben mai zuwa na 2023.

  • Gwamna Buni Ya Tallafawa Marayu 200 Da N50,000 Kowanne

Yusuf Ali ya kara da cewa, “Hon. Mai Mala Buni mutum ne mai matukar kaunar wanzuwar zaman lafiya da yaduwar fahimtar juna daga kowane bangaren al’ummar (yan siyasa).

Musamman a daidai lokacin da ake tunkarar zaben 2023, wanda abubuwan da za su sa a samu nasarar gudanar da zaben shi ne zaman lafiya. Yada maganganun gaba ko kiyayya a tsakanin al’umma ba zai haifar mana da-mai-ido ba, domin ko shakka babu dukkanin mu ‘ya’yan jihar Yobe ne, babu dalilin da zai sa mu rura wutar gaba ko kyama a tsakaninmu.”

Mallam Yusuf ya kara da cewa, kowane lokaci Gwmnan ya kan nanata muhimmancin zaman lafiya da fahimtar juna, wanda ko a kwanan baya, a sa’ilin da yake kaddamar da kasafin kudin wannan shekara a gaban Majalisar Dokokin jihar Yobe ya jadda batun ‘yan siyasa’ su guji kalaman da zasu kawo tashin-tashina ko kiyayya da makamantan su.

Labarai Masu Nasaba

‘Yan Kasuwa Na Neman Diyya Bayan Rushe Kasuwar Alaba Rago A Legas

ASUU Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Rashin Cika Mata Alƙawura

Gwamna ya ce, “Ina so na tunatar da mu cewa, a yayin da muke tunkarar babban zaben 2023, ya dace ace dokokin zabe na kasa su ne za su ci gaba da yi mana jagoranci, tare da kokari wajen abubuwan da za su kawo ma na hadin kai da zaman lafiya, tare da yin watsi da kalaman kiyayya ko tunzura jama’a.

Sannan mu na iya kasancewa ma su bambancin ra’ayin siyasa, amma wannan ba zai sanya mu kasance makiyan juna ba. A matsayinmu na ‘yan jihar Yobe, bai dace ace mun jefa kanmu a cikin tashin hankali da juna ba, domin wata bukatar son zuciyarka.”Gwamna Buni ya ce, “ina tabbatar muku da cewa, wannan gwamnati za ta ci gaba da aiki don tabbatar da zaman lafiya mai dorewa da ci gaban wannan jihar da na al’ummarmu baki daya.

Don haka, ina rokon ku, ku ci gaba da yin addu’o’i na musamman domin samun zaman lafiya da ci gaban jihar Yobe da ma kasarmu Nijeriya baki daya.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda ‘Hackers’ Ke Amfani Da Hanyar Smishing Wajen Yin Kutse

Next Post

Yadda Za Ki Tallata Kaya Ta Intanet

Related

‘Yan Kasuwa Na Neman Diyya Bayan Rushe Kasuwar Alaba Rago A Legas
Manyan Labarai

‘Yan Kasuwa Na Neman Diyya Bayan Rushe Kasuwar Alaba Rago A Legas

2 hours ago
Yajin Aikin ASUU Na Barazana Ga Ci Gaban Kasa
Labarai

ASUU Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Rashin Cika Mata Alƙawura

4 hours ago
Ranar Hausa Ta Duniya: Ba Ka Iyawa Duk Dagewarka Kuma Ba A Yaba Maka
Ra'ayi Riga

Ranar Hausa Ta Duniya: Ba Ka Iyawa Duk Dagewarka Kuma Ba A Yaba Maka

4 hours ago
Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya
Rahotonni

Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya

7 hours ago
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

16 hours ago
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna
Labarai

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

17 hours ago
Next Post
Yadda Za Ki Tallata Kaya Ta Intanet

Yadda Za Ki Tallata Kaya Ta Intanet

LABARAI MASU NASABA

Saka Zai Yi Jinyar Makonni 4 Sakamakon Rauni Da Ya Samu A Wasan Leeds

Saka Zai Yi Jinyar Makonni 4 Sakamakon Rauni Da Ya Samu A Wasan Leeds

August 26, 2025
‘Yan Kasuwa Na Neman Diyya Bayan Rushe Kasuwar Alaba Rago A Legas

‘Yan Kasuwa Na Neman Diyya Bayan Rushe Kasuwar Alaba Rago A Legas

August 26, 2025
Ɗaruruwan ‘Yan APC Sun Koma ADC A Sakkwato Saboda Rashin Tsaro Da Talauci

Ɗaruruwan ‘Yan APC Sun Koma ADC A Sakkwato Saboda Rashin Tsaro Da Talauci

August 26, 2025
Yajin Aikin ASUU Na Barazana Ga Ci Gaban Kasa

ASUU Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Rashin Cika Mata Alƙawura

August 26, 2025
Ranar Hausa Ta Duniya: Ba Ka Iyawa Duk Dagewarka Kuma Ba A Yaba Maka

Ranar Hausa Ta Duniya: Ba Ka Iyawa Duk Dagewarka Kuma Ba A Yaba Maka

August 26, 2025
Ɗan Nijeriya Ya Lashe Lambar Azurfa A Gasar Ninkaya Ta Duniya

Ɗan Nijeriya Ya Lashe Lambar Azurfa A Gasar Ninkaya Ta Duniya

August 26, 2025
Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya

Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya

August 26, 2025
An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

August 25, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

August 25, 2025
CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

August 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.