ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Gwamnan Yobe Ya Hori ‘Yan Siyasa Su Nesanci Kalaman Ta Da Zaune Tsaye

by Muhammad Maitela
4 years ago
Yobe

Gwamnan jihar Yobe, Hon. Mai Mala Buni ya bukaci yan siyasa a jihar Yobe su guji kalaman da za su jawo tada zaune tsaye a lokutan yakin neman zaben da yake gudana a fadin kasar nan; musamman a jihar Yobe.

Gwamnan ya bayyana hakan ta bakin Babban Mai Taimaka masa ta kafafin sadarwa na zamani, Mallam Yusuf Ali, inda ya ce a matsayin Gwamna Buni ma’abucin son zaman lafiya da sasanci, wanda hakan ya sanya ake masa lakabi da ‘Limamin-sulhu’, ya bukaci yan siyasa su zauna lafiya a lokacin da suke gudanar da yakin neman zaben mai zuwa na 2023.

  • Gwamna Buni Ya Tallafawa Marayu 200 Da N50,000 Kowanne

Yusuf Ali ya kara da cewa, “Hon. Mai Mala Buni mutum ne mai matukar kaunar wanzuwar zaman lafiya da yaduwar fahimtar juna daga kowane bangaren al’ummar (yan siyasa).

ADVERTISEMENT

Musamman a daidai lokacin da ake tunkarar zaben 2023, wanda abubuwan da za su sa a samu nasarar gudanar da zaben shi ne zaman lafiya. Yada maganganun gaba ko kiyayya a tsakanin al’umma ba zai haifar mana da-mai-ido ba, domin ko shakka babu dukkanin mu ‘ya’yan jihar Yobe ne, babu dalilin da zai sa mu rura wutar gaba ko kyama a tsakaninmu.”

Mallam Yusuf ya kara da cewa, kowane lokaci Gwmnan ya kan nanata muhimmancin zaman lafiya da fahimtar juna, wanda ko a kwanan baya, a sa’ilin da yake kaddamar da kasafin kudin wannan shekara a gaban Majalisar Dokokin jihar Yobe ya jadda batun ‘yan siyasa’ su guji kalaman da zasu kawo tashin-tashina ko kiyayya da makamantan su.

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

Gwamna ya ce, “Ina so na tunatar da mu cewa, a yayin da muke tunkarar babban zaben 2023, ya dace ace dokokin zabe na kasa su ne za su ci gaba da yi mana jagoranci, tare da kokari wajen abubuwan da za su kawo ma na hadin kai da zaman lafiya, tare da yin watsi da kalaman kiyayya ko tunzura jama’a.

Sannan mu na iya kasancewa ma su bambancin ra’ayin siyasa, amma wannan ba zai sanya mu kasance makiyan juna ba. A matsayinmu na ‘yan jihar Yobe, bai dace ace mun jefa kanmu a cikin tashin hankali da juna ba, domin wata bukatar son zuciyarka.”Gwamna Buni ya ce, “ina tabbatar muku da cewa, wannan gwamnati za ta ci gaba da aiki don tabbatar da zaman lafiya mai dorewa da ci gaban wannan jihar da na al’ummarmu baki daya.

Don haka, ina rokon ku, ku ci gaba da yin addu’o’i na musamman domin samun zaman lafiya da ci gaban jihar Yobe da ma kasarmu Nijeriya baki daya.”

Yobe
Muhammad Maitela
+ postsBio
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    29 Ga Mayu: Gwamna Buni Zai Yi Tattaunawar Kai Tsaye Ta Farko Da Al’umma
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    Wakilin VOA Haruna Dauda Ya Rasu A Maiduguri
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    PDP Ta Sake Zaɓar Amb. El-Gash A Yobe

MASU ALAKA

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
Labarai

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Sabbin Ministoci
Labarai

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 
Labarai

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Next Post
Yadda Za Ki Tallata Kaya Ta Intanet

Yadda Za Ki Tallata Kaya Ta Intanet

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.