• English
  • Business News
Friday, September 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Gwamnatinmu Za Ta Farfaɗo Da Harkar ilimi Da Walwalar Malamai – Atiku

by Sulaiman
3 years ago
in Siyasa
0
2023: Gwamnatinmu Za Ta Farfaɗo Da Harkar ilimi Da Walwalar Malamai – Atiku
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ɗan takarar shugaban ƙasa na PDP, Atiku Abubakar, Wazirin Adamawa ya yi alƙawarin cewa zai mayar da hankalin sa wajen farfaɗo da harkokin ilmi tare da inganta shi, ya na mai zargin cewa, “gwamnatin APC ta kashe harkar ilmi a ƙasar nan, ta hanyar bijiro da tsare-tsaren da kowa ya san ba za su inganta ci gaban ilmi ba.”

Atiku ya bayyana haka ne a yayin ƙaddamar da fara kamfen ɗin sa na shiyyar Kudu maso Yamma a Akure, babban birnin Jihar Ondo cikin makon nan.

  • Mijina Wayayyen Bafulatani Ne, Ba Bafulatanin Daji Ba Ne – Uwargidan Atiku

Daga nan ya ƙara jaddada irin alƙawarin da ya yi a Ilorin, wanda ya ce idan ya yi nasara, gwamnatin sa za ta ware dala biliyan 10 domin bunƙasa ƙanana da matsakaitan masana’antu, ta yadda matasa za su yunƙuro wajen samun aikin yi sosai, su ma mata rayuwar su za ta ƙara bunƙasa.

Da ya ke jawabi a wurin gangamin, wanda ya samu halartar ɗimbin magoya bayan PDP, Atiku ya ce Nijeriya ta yi asarar shekaru takwas da APC ta yi ta na mulki, wanda su ka jefa jama’a cikin mawuyacin halin da ba shi misaltuwa.

Atiku

Labarai Masu Nasaba

Arewa Ba Zata Ƙarɓi Mulki A 2027 Ba, Gwamna  Bago

Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)

Ya yi fatan cewa, “daga 2023, kada Allah ya sake jarabtar ‘yan Nijeriya da irin mulkin APC.”

Kafin ya fara jawabi, sai da uwargidan sa Titi Abubakar ta fara yi wa dandazon magoya bayan PDP jawabi tukunna.

Titi, wadda haifaffiyar Jihar Ondo ce, ta ce ta yi farin cikin ganin PDP ta fara kamfen ɗin shiyyar Kudu maso Yamma a jihar ta ta haihuwa.

“Ina gabatar da kai na a gare ku, a matsayi na na ‘yar ku. Idan ku ka zaɓi miji na, zai daƙile Boko Haram kuma zai inganta ilmi.

“Kada ku manta, miji na ne ya yi nasara a zaɓen 2019, amma aka yi masa maguɗi, aka murɗe zaɓen. To kada ku bari a sake yaudarar ku. Wannan lokacin ma ku fito ku sake zaɓen PDP.

“Idan Atiku ya yi nasara, wata dama ce da Jihar Ondo za ta samu cewa ‘yar su za ta zama uwargidan shugaban ƙasa. Dama kuma Bayarabiya ba ta taɓa zama uwargidan shugaban ƙasa a Najeriya ba.”

Atiku

Da ta ke yabon mijin ta, Titi ta ce ko lokacin da ya na mataimakin shugaban ƙasa ya yi rawar gani, domin shi ne ya janyo irin su Nasir El-Rufai da Ngozi Ikwenja-Ewela cikin gwamnati, “har da ma wasu fitattun haziƙan da su ka kawo ci gaba a ƙasar nan.

Mataimakin takarar Atiku, Gwamna Ifeanyi Okowa ya ce PDP za ta farfaɗo da fannin ilmi. Sannan ya nuna damuwar sa dangane da yadda ɗaliban jami’a su ka shafe watanni takwas a gida, ya na mai cewa ba za a samu irin haka a gwamnatin su ba.

Atiku

Shi ma Gwamna Udom Emmanuel ya roƙi al’ummar Jihar Ondo su zaɓi Atiku, wanda ya ce shi kaɗai a cikin sauran ‘yan takarar zai iya haɗa kan Najeriya.

Shugaban jam’iyya Iyorchia Ayu da Babban Daraktan Kamfen, wato Gwamna Aminu Tambuwal na Sokoto, duk sun yi wa taron jawabai masu nuna fifikon Atiku kan sauran ‘yan takara.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Dalilin Ci Gaba Da Fuskantar Karancin Mai A Fadin Nijeriya – Dillalai

Next Post

GORON JUMA’A

Related

Arewa Ba Zata Ƙarɓi Mulki A 2027 Ba, Gwamna  Bago
Siyasa

Arewa Ba Zata Ƙarɓi Mulki A 2027 Ba, Gwamna  Bago

4 days ago
Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)
Siyasa

Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)

4 days ago
APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC
Siyasa

APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC

5 days ago
PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya
Siyasa

PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya

6 days ago
INEC Ta Amince Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC
Manyan Labarai

INEC Ta Amince Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

1 week ago
APC Ce Ke Kai Mana Hari Saboda Siyasa – Malami
Manyan Labarai

APC Ce Ke Kai Mana Hari Saboda Siyasa – Malami

1 week ago
Next Post
GORON JUMA’A

GORON JUMA’A

LABARAI MASU NASABA

Atiku

2027: Su Wane Ne Ke Tsoron Guguwar Makinde A Jam’iyyar  PDP

September 19, 2025
Nan Ba Da Jimawa Ba Hauhawar Farashin Kayayyaki Za Ta Zama Tarihi —Fadar Shugaban

Nan Ba Da Jimawa Ba Hauhawar Farashin Kayayyaki Za Ta Zama Tarihi —Fadar Shugaban

September 19, 2025
Ce-ce-kuce Kan Shirin Ƙara Wa Ƴan Siyasa Masu Riƙe Da Madafun Iko Albashi

Ce-ce-kuce Kan Shirin Ƙara Wa Ƴan Siyasa Masu Riƙe Da Madafun Iko Albashi

September 19, 2025
An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

September 18, 2025
Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

September 18, 2025
Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

September 18, 2025
Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

September 18, 2025
Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

September 18, 2025
Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

September 18, 2025
An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

September 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.