• English
  • Business News
Monday, June 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: INEC Za Ta Dauki Ma’aikata Miliyan 1.4 Domin Horar Da Su Fasahar BVAS – Okoye

by Sulaiman
2 years ago
in Labarai
0
2023: INEC Za Ta Dauki Ma’aikata Miliyan 1.4 Domin Horar Da Su Fasahar BVAS – Okoye
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC), ta ce ta fara shirye-shiryen ɗaukar ma’aikatan wucin-gadi domin fara horas da su yadda za su yi aiki da na’urar tantance masu katin shaidar rajistar zaɓe, wato BVAS.

 

Kakakin Yaɗa Labaran INEC, Festus Okoye ne ya bayyana haka a wata tattaunawa da akayi da shi ƙarshen makon jiya, a gidan talbijin na Channels TV.

  • Babu Wata Kafa Na Yin Magudin Zabe A 2023 – INEC

Ya ce akwai buƙatar bayar da horon ƙwarewa wajen yin amfani da BVAS ɗin, ta yadda a lokacin zaɓuka ba za a riƙa samun jinkiri ba, wanda hakan ka iya sa masu jefa ƙuri’a yin ƙorafi da tsarin tantance su ta hanyar amfani da BVAS ɗin.

 

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Yusuf Ya Jagoranci Tawagar Kano Zuwa Jana’izar Marigayi Aminu Dantata A Madina

Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

Okoye ya ce za a wadatar da BVAS a dukkan rumfunan zaɓe 176,846 da ke faɗin ƙasar nan.

 

Wani bincike kuma, Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta tabbatar har yanzu akwai aƙalla mutum milyan 1.7 da ba su karɓi katin shaidar rajistar zaɓe ba, wato PVC, a Jihar Legas.

 

Rahotanni sun nuna cewa ya zuwa ranar Asabar, mutum 5,816,528 ne su ka karɓi shaidar rajistar zaɓe a Jihar Legas.

 

Tuni dai Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta fara kokawa da yadda karɓar katin shaidar rajistar zaɓe ke tafiyar-hawainiya a wasu jihohin, ganin yadda jama’a ba su bayar da himma sosai wajen tururuwar zuwa a karɓi katin, wanda sai da shi ne mutum zai iya jefa ƙuri’a a zaɓukan Nijeriya.

 

Hakan ya sa cikin makon jiya INEC ta je Jihar Cross River, inda ta riƙa wayar wa jama’a kai cewa su hanzarta su je su karɓi katin shaidar rajistar zaɓen su.

 

Hukumar ta yi wannan kiran ne a wurin gagarimin taron kalankuwar ‘Calabar Carnival’.

 

A Jihar Akwa Ibom ma hukumar ta koka ganin yadda jama’a ba su yin tururuwar zuwa karɓar katin shaidar rajistar zaɓe.

 

A Gundumar Babban Birnin Tarayya (FCT) kuwa, rahotanni sun nuna cewa har yanzu akwai katin shaidar rajistar zaɓen da ba a karɓa ba, tun daga 2011 zuwa 2022, har guda 460,643.

 

Rahotannin sun nuna cewa daga 2011 zuwa 2019 akwai katin da har yanzu ba a karɓa ba, guda 230,007.

 

Sai kuma waɗanda aka yi wa rajista amma ba su karɓa ba daga 2021 zuwa 2022 har guda 230,636.

 

A wata tattaunawa da aka yi da shi a gidan talbijin na Channels, Kakakin Yaɗa Labaran INEC, Festus Okoye, ya jaddada cewa INEC za ta yi amfani da na’urar tantance mai rajistar katin zaɓe, wato BVAS a dukkan rumfunan zaɓen ƙasar nan guda 176,846.

 

Sannan ya ce tuni INEC ta fara aikin yadda za ta ɗauki ma’aikatan wucin-gadi fiye da milyan 1.4 waɗanda za a bai wa horon aiki da na’urar BVAS a lokacin zaɓukan shugaban ƙasa, na ‘yan majalisar tarayya, gwamnoni da na majalisar dokoki ta jihohi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Tashar Jiragen Ruwa Ta Shanghai Ta Kasance Mafi Hada-Hadar Kwantenoni A Duniya A 2022

Next Post

Albarkacin Hutun Sabuwar Shekara An Gudanar Da Yawon Bude Ido Miliyan 52.7 A Kasar Sin

Related

Gwamna Yusuf Ya Jagoranci Tawagar Kano Zuwa Jana’izar Marigayi Aminu Dantata A Madina
Manyan Labarai

Gwamna Yusuf Ya Jagoranci Tawagar Kano Zuwa Jana’izar Marigayi Aminu Dantata A Madina

2 hours ago
Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

11 hours ago
Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu
Labarai

Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

14 hours ago
Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 
Labarai

Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

18 hours ago
Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto
Labarai

Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

20 hours ago
Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo
Labarai

Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

20 hours ago
Next Post
Albarkacin Hutun Sabuwar Shekara An Gudanar Da Yawon Bude Ido Miliyan 52.7 A Kasar Sin

Albarkacin Hutun Sabuwar Shekara An Gudanar Da Yawon Bude Ido Miliyan 52.7 A Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Yusuf Ya Jagoranci Tawagar Kano Zuwa Jana’izar Marigayi Aminu Dantata A Madina

Gwamna Yusuf Ya Jagoranci Tawagar Kano Zuwa Jana’izar Marigayi Aminu Dantata A Madina

June 30, 2025
Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

June 29, 2025
Sharrin Ƴan Adawa Ne, Gwamnati Ta Ƙaryata Labarin Cire SGF Akume 

Sharrin Ƴan Adawa Ne, Gwamnati Ta Ƙaryata Labarin Cire SGF Akume 

June 29, 2025
An Sauya Sunan Makarantar Wasanni Don Girmama Ƴan Kano Da Suka Yi Hatsari

An Sauya Sunan Makarantar Wasanni Don Girmama Ƴan Kano Da Suka Yi Hatsari

June 29, 2025
Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

June 29, 2025
Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar

Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar

June 29, 2025
Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

June 29, 2025
2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu

2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu

June 29, 2025
Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya

Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya

June 29, 2025
Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

June 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.