ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: INEC Za Ta Dauki Ma’aikata Miliyan 1.4 Domin Horar Da Su Fasahar BVAS – Okoye

by Sulaiman
4 years ago
INEC

Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC), ta ce ta fara shirye-shiryen ɗaukar ma’aikatan wucin-gadi domin fara horas da su yadda za su yi aiki da na’urar tantance masu katin shaidar rajistar zaɓe, wato BVAS.

 

Kakakin Yaɗa Labaran INEC, Festus Okoye ne ya bayyana haka a wata tattaunawa da akayi da shi ƙarshen makon jiya, a gidan talbijin na Channels TV.

ADVERTISEMENT
  • Babu Wata Kafa Na Yin Magudin Zabe A 2023 – INEC

Ya ce akwai buƙatar bayar da horon ƙwarewa wajen yin amfani da BVAS ɗin, ta yadda a lokacin zaɓuka ba za a riƙa samun jinkiri ba, wanda hakan ka iya sa masu jefa ƙuri’a yin ƙorafi da tsarin tantance su ta hanyar amfani da BVAS ɗin.

 

LABARAI MASU NASABA

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Okoye ya ce za a wadatar da BVAS a dukkan rumfunan zaɓe 176,846 da ke faɗin ƙasar nan.

 

Wani bincike kuma, Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta tabbatar har yanzu akwai aƙalla mutum milyan 1.7 da ba su karɓi katin shaidar rajistar zaɓe ba, wato PVC, a Jihar Legas.

 

Rahotanni sun nuna cewa ya zuwa ranar Asabar, mutum 5,816,528 ne su ka karɓi shaidar rajistar zaɓe a Jihar Legas.

 

Tuni dai Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta fara kokawa da yadda karɓar katin shaidar rajistar zaɓe ke tafiyar-hawainiya a wasu jihohin, ganin yadda jama’a ba su bayar da himma sosai wajen tururuwar zuwa a karɓi katin, wanda sai da shi ne mutum zai iya jefa ƙuri’a a zaɓukan Nijeriya.

 

Hakan ya sa cikin makon jiya INEC ta je Jihar Cross River, inda ta riƙa wayar wa jama’a kai cewa su hanzarta su je su karɓi katin shaidar rajistar zaɓen su.

 

Hukumar ta yi wannan kiran ne a wurin gagarimin taron kalankuwar ‘Calabar Carnival’.

 

A Jihar Akwa Ibom ma hukumar ta koka ganin yadda jama’a ba su yin tururuwar zuwa karɓar katin shaidar rajistar zaɓe.

 

A Gundumar Babban Birnin Tarayya (FCT) kuwa, rahotanni sun nuna cewa har yanzu akwai katin shaidar rajistar zaɓen da ba a karɓa ba, tun daga 2011 zuwa 2022, har guda 460,643.

 

Rahotannin sun nuna cewa daga 2011 zuwa 2019 akwai katin da har yanzu ba a karɓa ba, guda 230,007.

 

Sai kuma waɗanda aka yi wa rajista amma ba su karɓa ba daga 2021 zuwa 2022 har guda 230,636.

 

A wata tattaunawa da aka yi da shi a gidan talbijin na Channels, Kakakin Yaɗa Labaran INEC, Festus Okoye, ya jaddada cewa INEC za ta yi amfani da na’urar tantance mai rajistar katin zaɓe, wato BVAS a dukkan rumfunan zaɓen ƙasar nan guda 176,846.

 

Sannan ya ce tuni INEC ta fara aikin yadda za ta ɗauki ma’aikatan wucin-gadi fiye da milyan 1.4 waɗanda za a bai wa horon aiki da na’urar BVAS a lokacin zaɓukan shugaban ƙasa, na ‘yan majalisar tarayya, gwamnoni da na majalisar dokoki ta jihohi.

INEC
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta
  • Sulaiman
    Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
  • Sulaiman
    Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

MASU ALAKA

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa
Manyan Labarai

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta
Manyan Labarai

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje
Manyan Labarai

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Next Post
Albarkacin Hutun Sabuwar Shekara An Gudanar Da Yawon Bude Ido Miliyan 52.7 A Kasar Sin

Albarkacin Hutun Sabuwar Shekara An Gudanar Da Yawon Bude Ido Miliyan 52.7 A Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.