Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar NNPP, Dakta Rabi’u Musa Kwankwaso a ranar Laraba ya bukaci al’ummar jihar Delta da su yi wa jam’iyyar NNPP ruwan kuri’u a zaben 2023 mai zuwa.
Kwankwaso ya yi wannan kiran ne a lokacin da yake jawabi jim kadan bayan kaddamar da ofishin yakin neman zaben Hon. Onochie Anthony Ochie a Ogwashi-Uku, da ke Jihar Delta.
Ya ce jam’iyyar NNPP, jam’iyya ce ta kasa da za ta iya samun nasara a duk fadin Nijeriya.
Kwankwaso ya kuma yi kira ga daukacin ‘yan takarar jam’iyyar NNPP da su dukufa wajen ganin jam’iyyar ta samu nasara a zaben.
Kwakwaso ya yi alkawarin gina ajujuwa 500 a cikin shekaru uku, tare da mayar da yaran da basu samu damar yin karatu ba zuwa ajujuwa sannan kuma zai samar da dimbin ayyukan yi ga jama’ar Nijeriya.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp