• English
  • Business News
Sunday, August 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Jerin Ayyukan Ma’aikatan Zabe Na Dindindin Da Na Wucin Gadi

by Sulaiman
2 years ago
in Labarai
0
2023: Jerin Ayyukan Ma’aikatan Zabe Na Dindindin Da Na Wucin Gadi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwanan nan Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta fara horas da ma’aikatan wucin-gadi fiye da miliyan 1.2, domin su san makamar aikin gudanar da zaɓen 2023 da ke gaban su. Waɗannan ma’aikatan wucin-gadi ne tare da sauran ma’aikatan dindindin na INEC nauyin gudanar da sahihi kuma karɓaɓben zaɓe ke hannun su.

 

Kafin zuwan ranar zaɓe, ya kamata mai karatu ya san matsayi da ayyukan waɗannan ma’aikata a ranakun zaɓe.

  • 2023: Kashi 90 Na Shirye-Shiryen Zabe Ya Kammala – INEC

Yayin da saura makonni biyu a jefa ƙuri’ar zaɓen shugaban ƙasa da na ‘yan majalisun tarayya, a ranakun 25 ga Fabrairu da 11 ga Maris, masu karatu za su so jin ayyuka, matsayi da muhimmancin wasu manyan jami’an Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) a lokacin zaɓe.

 

Labarai Masu Nasaba

Dangote Ya Ɗauki Nauyin Bikin Baje Kolin Gidajen Afrika Da Mahalarta Ƙasashe 21

ADC Ta Yi Allah-wadai Da Rufe Gidan Rediyon Badeggi FM A Neja

Kwamishinonin Zaɓe Na Jihohi (RECs), waɗanda a Turance ake kira ‘Resident Electoral Commissioners’: Su ne INEC ta ɗora wa nauyin kula da kuma sa-ido wajen gudanar da zaɓuka a jihohi da FCT, Abuja.

 

Su ne kuma INEC ke damƙa wa kayan zaɓe na sirri da su ka haɗa da takardun sirri irin su ƙuri’u da sauran kayan aikin zaɓe. Su ne kuma ke rarraba su ga dukkanin jami’an gudanar da zaɓe. Kuma su ne ke da alhakin ɗaukar ma’aitakan zaɓe na wucin-gadi da kuma horas da su ƙa’idojin da su ka shafi aikin zaɓe.

 

Baturen Zaɓe: Shi Baturen Zaɓe, wato ‘Electoral Officer’ aikin shi gudanar da zaɓe da sa-ido kan zaɓen a ƙaramar hukuma ko gundumomi idan a FCT Abuja ne.

 

Kuma su na karɓar kayan aikin zaɓe daga hannun Kwamishinan Zaɓe na Tarayya a Jiha (REC). Su kuma za su raba wa Dubagarin Baturen Zaɓe (Supervisory Presiding Officers) su rarraba wa Jami’an Zaɓe (Presiding Officers)

 

Dubagarin Jami’an Zaɓe (Supervisory Presiding Officers): Aikin su shi ne sa-ido wajen kula da yadda ake gudanar da zaɓuɓɓuka a rumfunan zaɓe. Kuma su na taimakawa wajen horas da Jami’an Zaɓe da sauran su. Kuma aikin su ya haɗa da tabbatarwa dukkan kayan zaɓe sun isa rumfunan zaɓe a wadace kuma a kan lokaci.

 

Kuma aikin su ne su riƙa zagayawa rumfunan zaɓe daban-daban su na jin ko akwai ƙorafe-ƙorafen da wata rumfar zaɓe ke son a magance mata cikin gaggawa.

 

Haka nan kuma aikin waɗannan jami’ai ne su ga cewa lallai sakamakon zaɓen rumfunan zaɓen da ke ƙarƙashin su ya isa a cibiyar tattara sakamakon zaɓe daga hannun jami’in zaɓe zuwa hannun jami’in tattara sakamakon zaɓe (collation officer).

 

Sannan kuma aikin sa ne ya tabbatar an mayar da dukkan kayan zaɓe a hannun Baturen Zaɓe da zarar an kammala gudanar da zaɓe.

 

Jami’an Tattara Sakamakon Zaɓe: Su ne a Turance ake kira ‘Collation Officers’, kuma aikin su ya haɗa tattara sakamakon zaɓe tsakanin rumfunan zaɓe a cikin yankunan karkara da kuma mazaɓa sukutum.

 

Jami’an Zaɓe Masu Kula Da Rumfunan Zaɓe: Wato su ne ‘Presiding Officers’, waɗanda aikin su shi ne kula da yadda ake gudanar da zaɓe a rumfunan zaɓe.

 

Kuma dai ne masu tantancewa, ƙirgawa da bayyana sakamakon zaɓe a rumfunan zaɓe, bayan sun yi jadawalin sakamakon yawan ƙuri’un da kowace jam’iyya ta samu, tare da ƙididdige yawan adadin ƙuri’un a aka jefa.

 

Waɗannan jami’ai tilas su riga kowa zuwa rumfar zaɓe a ranar zaɓe, domin su tsara yadda komai zai tafi daidai, ciki har da wayar wa masu zaɓe kai dangane da yadda za su kaɗa ƙuri’a.

 

Sannan kuma aikin su ne damƙa wa mai jefa ƙuri’a takardar ƙuri’ar da zai dangwala yatsa a kan ta.

 

Daga nan zai tabbatar cewa wanda ya zai jefa ƙuri’a ya dangwala mata yatsa kafin ya jefa cikin akwatin tattara ƙuri’u.

 

Jami’an Taimaka Wa Masu Aiki Da Na’urori: Za su riƙa bayar da taimakon gaggawa a wurare daban daban-daban.

 

Su ne za su riƙa yin gaggawar kai ɗauki wurin da duk aka samu matsala da na’urar BVAS. Za su yi gaggawar gyarawa ko canja wadda ta wajaba a canja nan da nan.

 

Sannan aikin su tabbatar da sakamakon zaɓen da rumfar zaɓe ta fitar aka loda a shafin manhajar tattara sakamakon zaɓe.

 

Jami’an Daidaita Gungun Masu Jefa Ƙuri’a (Polling Team): Wannan tawaga ba ta rasa kaiwa mutum huɗu a kowace rumfar zaɓe. Za su binciki rajistar sunayen masu jefa ƙuri’a, miƙa ƙuri’a ga wanda zai dangwala mata yatsa da kuma tabbatar da cewa masu jefa ƙuria sun shiga layi.

 

Jami’an Kula Da Zaɓe: Waɗannan ma’aikatan INEC ne na dindindin. Aikin su shi ne duba yadda zaɓe ke gudana a shiyyoyi, Ƙananan Hukumomi da Mazaɓu.

 

Baturen Bayyana Sakamakon Zaɓe: Shi ne ‘Returning Officer’, wanda aka ɗora wa aikin bayyana sakamakon zaɓen Sanata, Majalisar Dokoki ta Tarayya da ta Jihohi, sai kuma bayyana sakamakon zaɓen gwamnoni.

 

Babban Baturen Bayyana Sakamakon Zaɓe: Wannan kuma shi ne Shugaban INEC na ƙasa. Shi ke tattara sakamakon zaɓen shugaban ƙasa daga kowace jiha. Idan ya kammala tattarawar shi ne daga nan sai ya bayyana sakamakon zaɓen shugaban ƙasa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ganduje Ya Yi Barazanar Daukar Mataki Kan Bankunan Da Suka Ki Karbar Tsaffin Kudi

Next Post

2023: Duka Ma’aikatan Wucin Gadi Sai Sun Yi Rantsuwar Yin Adalci Ga Kowacce Jam’iyya – INEC

Related

Dangote Ya Ɗauki Nauyin Bikin Baje Kolin Gidajen Afrika Da Mahalarta Ƙasashe 21
Labarai

Dangote Ya Ɗauki Nauyin Bikin Baje Kolin Gidajen Afrika Da Mahalarta Ƙasashe 21

58 minutes ago
Ministan Yaɗa Labarai Ya Buƙaci A Kwantar Da Hankali Kan Dakatar Da Gidan Rediyon Badeggi FM
Labarai

ADC Ta Yi Allah-wadai Da Rufe Gidan Rediyon Badeggi FM A Neja

6 hours ago
Gwamnatin Katsina Ta Gabatar Da Matsayarta A Taron Jin Ra’ayiyin Jama’a
Labarai

Gwamnatin Katsina Ta Gabatar Da Matsayarta A Taron Jin Ra’ayiyin Jama’a

7 hours ago
Borno Za Ta Sake Tsugunar Da ‘Yan Gudun Hijira 5,000 Kafin Damuna Ta Kare
Manyan Labarai

Borno Za Ta Sake Tsugunar Da ‘Yan Gudun Hijira 5,000 Kafin Damuna Ta Kare

8 hours ago
Ministan Yaɗa Labarai Ya Buƙaci A Kwantar Da Hankali Kan Dakatar Da Gidan Rediyon Badeggi FM
Labarai

Ministan Yaɗa Labarai Ya Buƙaci A Kwantar Da Hankali Kan Dakatar Da Gidan Rediyon Badeggi FM

9 hours ago
Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto
Labarai

Etsu Nupe Ya Jaddada Buƙatar Sama Wa Sarakunan Gargajiya Gurbi A Tsarin Mulki

23 hours ago
Next Post
2023: Duka Ma’aikatan Wucin Gadi Sai Sun Yi Rantsuwar Yin Adalci Ga Kowacce Jam’iyya – INEC

2023: Duka Ma'aikatan Wucin Gadi Sai Sun Yi Rantsuwar Yin Adalci Ga Kowacce Jam'iyya - INEC

LABARAI MASU NASABA

Dangote Ya Ɗauki Nauyin Bikin Baje Kolin Gidajen Afrika Da Mahalarta Ƙasashe 21

Dangote Ya Ɗauki Nauyin Bikin Baje Kolin Gidajen Afrika Da Mahalarta Ƙasashe 21

August 3, 2025
An Fara Bayar Da Hidimomin Da Suka Shafi Sauka Da Tashi Domin Gasar Wasanni Ta Duniya Ta Chengdu

An Fara Bayar Da Hidimomin Da Suka Shafi Sauka Da Tashi Domin Gasar Wasanni Ta Duniya Ta Chengdu

August 3, 2025
Rikici Ya Ɓarke A Zaɓen Ribas, Ƴan PDP Sun Fito A Matsayin Ƴan Takarar APC

Rikici Ya Ɓarke A Zaɓen Ribas, Ƴan PDP Sun Fito A Matsayin Ƴan Takarar APC

August 3, 2025
Ana Gaggauta Ayyukan Gyara Tituna Da Gadojin Da Ambaliya Ta Lalata A Arewacin Kasar Sin

Ana Gaggauta Ayyukan Gyara Tituna Da Gadojin Da Ambaliya Ta Lalata A Arewacin Kasar Sin

August 3, 2025
Shugabar Tanzania Ta Kaddamar Da Cibiyar Cinikayya Da Jigila Da Sin Ta Gina A Kasar

Shugabar Tanzania Ta Kaddamar Da Cibiyar Cinikayya Da Jigila Da Sin Ta Gina A Kasar

August 3, 2025
Manoma Sun Caccaki Tinubu Kan Ƙarfafa Shigo Da Shinkafa Da Masara Daga Ƙasashen Waje

Manoma Sun Caccaki Tinubu Kan Ƙarfafa Shigo Da Shinkafa Da Masara Daga Ƙasashen Waje

August 3, 2025
Amurka Ta Gargaɗi Ƴan Nijeriya Kan Zuwa Ƙasarta Domin Haihuwa

Amurka Ta Gargaɗi Ƴan Nijeriya Kan Zuwa Ƙasarta Domin Haihuwa

August 3, 2025
Ministan Yaɗa Labarai Ya Buƙaci A Kwantar Da Hankali Kan Dakatar Da Gidan Rediyon Badeggi FM

ADC Ta Yi Allah-wadai Da Rufe Gidan Rediyon Badeggi FM A Neja

August 3, 2025
Gwamnatin Katsina Ta Gabatar Da Matsayarta A Taron Jin Ra’ayiyin Jama’a

Gwamnatin Katsina Ta Gabatar Da Matsayarta A Taron Jin Ra’ayiyin Jama’a

August 3, 2025
Borno Za Ta Sake Tsugunar Da ‘Yan Gudun Hijira 5,000 Kafin Damuna Ta Kare

Borno Za Ta Sake Tsugunar Da ‘Yan Gudun Hijira 5,000 Kafin Damuna Ta Kare

August 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.