ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Jerin Ayyukan Ma’aikatan Zabe Na Dindindin Da Na Wucin Gadi

by Sulaiman
4 years ago
INEC

Kwanan nan Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta fara horas da ma’aikatan wucin-gadi fiye da miliyan 1.2, domin su san makamar aikin gudanar da zaɓen 2023 da ke gaban su. Waɗannan ma’aikatan wucin-gadi ne tare da sauran ma’aikatan dindindin na INEC nauyin gudanar da sahihi kuma karɓaɓben zaɓe ke hannun su.

 

Kafin zuwan ranar zaɓe, ya kamata mai karatu ya san matsayi da ayyukan waɗannan ma’aikata a ranakun zaɓe.

ADVERTISEMENT
  • 2023: Kashi 90 Na Shirye-Shiryen Zabe Ya Kammala – INEC

Yayin da saura makonni biyu a jefa ƙuri’ar zaɓen shugaban ƙasa da na ‘yan majalisun tarayya, a ranakun 25 ga Fabrairu da 11 ga Maris, masu karatu za su so jin ayyuka, matsayi da muhimmancin wasu manyan jami’an Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) a lokacin zaɓe.

 

LABARAI MASU NASABA

Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

Kwamishinonin Zaɓe Na Jihohi (RECs), waɗanda a Turance ake kira ‘Resident Electoral Commissioners’: Su ne INEC ta ɗora wa nauyin kula da kuma sa-ido wajen gudanar da zaɓuka a jihohi da FCT, Abuja.

 

Su ne kuma INEC ke damƙa wa kayan zaɓe na sirri da su ka haɗa da takardun sirri irin su ƙuri’u da sauran kayan aikin zaɓe. Su ne kuma ke rarraba su ga dukkanin jami’an gudanar da zaɓe. Kuma su ne ke da alhakin ɗaukar ma’aitakan zaɓe na wucin-gadi da kuma horas da su ƙa’idojin da su ka shafi aikin zaɓe.

 

Baturen Zaɓe: Shi Baturen Zaɓe, wato ‘Electoral Officer’ aikin shi gudanar da zaɓe da sa-ido kan zaɓen a ƙaramar hukuma ko gundumomi idan a FCT Abuja ne.

 

Kuma su na karɓar kayan aikin zaɓe daga hannun Kwamishinan Zaɓe na Tarayya a Jiha (REC). Su kuma za su raba wa Dubagarin Baturen Zaɓe (Supervisory Presiding Officers) su rarraba wa Jami’an Zaɓe (Presiding Officers)

 

Dubagarin Jami’an Zaɓe (Supervisory Presiding Officers): Aikin su shi ne sa-ido wajen kula da yadda ake gudanar da zaɓuɓɓuka a rumfunan zaɓe. Kuma su na taimakawa wajen horas da Jami’an Zaɓe da sauran su. Kuma aikin su ya haɗa da tabbatarwa dukkan kayan zaɓe sun isa rumfunan zaɓe a wadace kuma a kan lokaci.

 

Kuma aikin su ne su riƙa zagayawa rumfunan zaɓe daban-daban su na jin ko akwai ƙorafe-ƙorafen da wata rumfar zaɓe ke son a magance mata cikin gaggawa.

 

Haka nan kuma aikin waɗannan jami’ai ne su ga cewa lallai sakamakon zaɓen rumfunan zaɓen da ke ƙarƙashin su ya isa a cibiyar tattara sakamakon zaɓe daga hannun jami’in zaɓe zuwa hannun jami’in tattara sakamakon zaɓe (collation officer).

 

Sannan kuma aikin sa ne ya tabbatar an mayar da dukkan kayan zaɓe a hannun Baturen Zaɓe da zarar an kammala gudanar da zaɓe.

 

Jami’an Tattara Sakamakon Zaɓe: Su ne a Turance ake kira ‘Collation Officers’, kuma aikin su ya haɗa tattara sakamakon zaɓe tsakanin rumfunan zaɓe a cikin yankunan karkara da kuma mazaɓa sukutum.

 

Jami’an Zaɓe Masu Kula Da Rumfunan Zaɓe: Wato su ne ‘Presiding Officers’, waɗanda aikin su shi ne kula da yadda ake gudanar da zaɓe a rumfunan zaɓe.

 

Kuma dai ne masu tantancewa, ƙirgawa da bayyana sakamakon zaɓe a rumfunan zaɓe, bayan sun yi jadawalin sakamakon yawan ƙuri’un da kowace jam’iyya ta samu, tare da ƙididdige yawan adadin ƙuri’un a aka jefa.

 

Waɗannan jami’ai tilas su riga kowa zuwa rumfar zaɓe a ranar zaɓe, domin su tsara yadda komai zai tafi daidai, ciki har da wayar wa masu zaɓe kai dangane da yadda za su kaɗa ƙuri’a.

 

Sannan kuma aikin su ne damƙa wa mai jefa ƙuri’a takardar ƙuri’ar da zai dangwala yatsa a kan ta.

 

Daga nan zai tabbatar cewa wanda ya zai jefa ƙuri’a ya dangwala mata yatsa kafin ya jefa cikin akwatin tattara ƙuri’u.

 

Jami’an Taimaka Wa Masu Aiki Da Na’urori: Za su riƙa bayar da taimakon gaggawa a wurare daban daban-daban.

 

Su ne za su riƙa yin gaggawar kai ɗauki wurin da duk aka samu matsala da na’urar BVAS. Za su yi gaggawar gyarawa ko canja wadda ta wajaba a canja nan da nan.

 

Sannan aikin su tabbatar da sakamakon zaɓen da rumfar zaɓe ta fitar aka loda a shafin manhajar tattara sakamakon zaɓe.

 

Jami’an Daidaita Gungun Masu Jefa Ƙuri’a (Polling Team): Wannan tawaga ba ta rasa kaiwa mutum huɗu a kowace rumfar zaɓe. Za su binciki rajistar sunayen masu jefa ƙuri’a, miƙa ƙuri’a ga wanda zai dangwala mata yatsa da kuma tabbatar da cewa masu jefa ƙuria sun shiga layi.

 

Jami’an Kula Da Zaɓe: Waɗannan ma’aikatan INEC ne na dindindin. Aikin su shi ne duba yadda zaɓe ke gudana a shiyyoyi, Ƙananan Hukumomi da Mazaɓu.

 

Baturen Bayyana Sakamakon Zaɓe: Shi ne ‘Returning Officer’, wanda aka ɗora wa aikin bayyana sakamakon zaɓen Sanata, Majalisar Dokoki ta Tarayya da ta Jihohi, sai kuma bayyana sakamakon zaɓen gwamnoni.

 

Babban Baturen Bayyana Sakamakon Zaɓe: Wannan kuma shi ne Shugaban INEC na ƙasa. Shi ke tattara sakamakon zaɓen shugaban ƙasa daga kowace jiha. Idan ya kammala tattarawar shi ne daga nan sai ya bayyana sakamakon zaɓen shugaban ƙasa.

INEC
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki
  • Sulaiman
    Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna
  • Sulaiman
    Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba
  • Sulaiman
    Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

MASU ALAKA

INEC
Labarai

Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote

September 10, 2026
INEC
Labarai

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

September 10, 2026
Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato
Manyan Labarai

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
Next Post
2023: Duka Ma’aikatan Wucin Gadi Sai Sun Yi Rantsuwar Yin Adalci Ga Kowacce Jam’iyya – INEC

2023: Duka Ma'aikatan Wucin Gadi Sai Sun Yi Rantsuwar Yin Adalci Ga Kowacce Jam'iyya - INEC

LABARAI MASU NASABA

Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

September 10, 2026
INEC

Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote

September 10, 2026
INEC

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

September 10, 2026
Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026
Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

September 10, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026
’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

September 10, 2026
2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.