• English
  • Business News
Tuesday, September 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Kotu Ta Aike Da Mawallafin Jaridar WikkiTimes Gidan Yari Kan Zargin Haifar Da Fitina

by Khalid Idris Doya
3 years ago
in Labarai
0
2023: Kotu Ta Aike Da Mawallafin Jaridar WikkiTimes Gidan Yari Kan Zargin Haifar Da Fitina
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wata kotun majistire mai lamba 3 a jihar Bauchi ta tura mawallafin jaridar yanar gizo ta WikkiTimes, Malam Haruna Muhammad Salisu zuwa gidan gyara hali kan zargin tayar da zaune-tsaye da munana wa gwamnan jihar Bauchi Bala Muhammad.

 

Alkalin Kotun, Ahmed Musa shi ne ya aike da dan jaridan gidan yari har zuwa ranar Laraba domin yanke hukunci kan bukatar bayar da beli kan kes din da kwamishinan ‘yan sandan jihar Bauchi, CP Aminu Alhassan ya shigar a kan dan jaridan.

  • Kotu Ta Yi Watsi Da Bukatar Neman A Sauke Babban Sufeton ‘Yansanda

‘Yansandan dai sun zargi dan jaridan da yin hayar wasu mata domin ganin an kawo tsaiko ga zaman lafiya da kuma tayar da zaune tsaye a kusa da rumfar zabe a kauyen Duguri da ke karamar hukumar Alkaleri gami da zargin munana wa gwamna Bala a mazabarsa lamarin da ya saba wa sashi 114 na Final Kod.

 

Labarai Masu Nasaba

Majalisar Dokokin Kano Ta Amince Da Ƙarin Kasafin Naira Biliyan 215.3 A Na 2025

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda, Sun Ceto Mata Da Yara A Zamfara

Da aka gabatar da karar a ranar Talata, dan jaridan ya musanta dukkanin zarge-zargen da ake masa tare da cewa ‘bai aikata laifi ba’.

 

Lauyan kariya, Idris Gambo (SG Idrees) ya gabatar da bukatar bada belin wanda ake zargi. Idris Gambo dai ya ce, bisa la’akari da zargin da ake yi wa Haruna, za a biya bada belinsa, don haka ne ya nemi kotun ta amince da bayar da belin nasa.

 

Amma lauyan masu kara ya yi suka bisa kan bukatar belin. Lauyan ya ce, abun da ya sanya suka ki amincewa da belin shi ne rayuwar Harunan na cikin hatsari domin wasu da suke waje suna zaman jiran su far masa ta hanyar daukan doka a hannu.

 

Sai dai Lauyan Haruna, Barista Gambo ya shure dukkanin batutuwan lauyan masu karan.

 

Yana mai cewa, kamatuwa ya yi gwamnati da ‘yansanda da su tashi tsaye su fuskanci wadanda ake ce su na shirin farmakar wanda yake karewa.

 

Sai dai kuma wani lauya daga ofishin Antoni-janar na jihar Bauchi, Haruna Ibrahim ya bayyana a gaban kotun inda ya sanar da cewa, Antoni-janar na shigar na son zai karbi ragamar cigaba da kes din daga hannun ‘yansanda domin cigaba bisa amfani da kundin tsarin mulkin kasa na 1999.

WikkiTimes

Daga bisani ne dai kotun ta dage shari’ar zuwa ranar 1 ga watan Maris domin cigaba da sauraron bukatar bayar da beli.

 

Rahotonni na nuni da cewa, an cafke Haruna ne a yayin da ake zaben shugaban kasa da ‘yan majalisun tarayya a ranar Asabar inda ke daukan bidiyon wasu mata da ke zanga-zangar bayyana abun da ke damunsu a lokacin da ake gudanar da zaben a kusa da mahaiyar gwamna Bala a kauyen Duguri.

 

Sai dai, editan jaridar WikkiTimes, Yakubu Mohammed ya bayyana ta cikin wata sanarwa da ya fitar cewa, gwamnan Bauchi, Bala Muhammad na da hannu a shari’ar, ya zargi gwamnan da kokarin tauye wa dan jaridan ‘yancinsa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gyare-gyare Sun Sa Zaman Al’umma Samun Ci Gaba

Next Post

Sanarwar Cikakken Zama Na Biyu Na Kwamitin Kolin Jam’iyyar Kwaminis Ta Kasar Sin Karo Na 20

Related

Majalisar Kano Na Shirin Zartar Da Dokar Gwajin Kwayoyin Jini, Kanjamau Da Cutar Hanta Kafin Aure
Manyan Labarai

Majalisar Dokokin Kano Ta Amince Da Ƙarin Kasafin Naira Biliyan 215.3 A Na 2025

10 hours ago
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda, Sun Ceto Mata Da Yara A Zamfara
Labarai

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda, Sun Ceto Mata Da Yara A Zamfara

11 hours ago
NAPTIP Da Hisbah Sun Ceto Mata 12 Da Aka Yi Safararsu A Kano Zuwa Saudiyya
Labarai

NAPTIP Da Hisbah Sun Ceto Mata 12 Da Aka Yi Safararsu A Kano Zuwa Saudiyya

12 hours ago
Tinubu Ya Yi Adalci Ga Dukkan Yankunan Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai
Manyan Labarai

Tinubu Ya Yi Adalci Ga Dukkan Yankunan Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai

14 hours ago
Gwamnan Neja Ya Kori Kwamishinoninsa Gaba ÆŠaya
Manyan Labarai

Gwamnan Neja Ya Kori Kwamishinoninsa Gaba ÆŠaya

18 hours ago
Ƴansanda Sun Gano Motocin Sata 2 A Adamawa
Labarai

Ƴansanda Sun Gano Motocin Sata 2 A Adamawa

19 hours ago
Next Post
Sanarwar Cikakken Zama Na Biyu Na Kwamitin Kolin Jam’iyyar Kwaminis Ta Kasar Sin Karo Na 20

Sanarwar Cikakken Zama Na Biyu Na Kwamitin Kolin Jam’iyyar Kwaminis Ta Kasar Sin Karo Na 20

LABARAI MASU NASABA

Xi Ya Gabatar Da Shawarar Tsarin Shugabanci Na Duniya 

Xi Ya Gabatar Da Shawarar Tsarin Shugabanci Na Duniya 

September 1, 2025
Peng Liyuan Da Matan Shugabannin Kasashe Membobin SCO Masu Halartar Taron SCO Sun Ziyarci Kogin Haihe Na Tianjin

Peng Liyuan Da Matan Shugabannin Kasashe Membobin SCO Masu Halartar Taron SCO Sun Ziyarci Kogin Haihe Na Tianjin

September 1, 2025
Tottenham Ta Dauki Aron Kolo Muani Daga PSG

Tottenham Ta Dauki Aron Kolo Muani Daga PSG

September 1, 2025
AU: Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Bunkasa Noma Na Da Matukar Muhimmanci

AU: Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Bunkasa Noma Na Da Matukar Muhimmanci

September 1, 2025
Majalisar Kano Na Shirin Zartar Da Dokar Gwajin Kwayoyin Jini, Kanjamau Da Cutar Hanta Kafin Aure

Majalisar Dokokin Kano Ta Amince Da Ƙarin Kasafin Naira Biliyan 215.3 A Na 2025

September 1, 2025
Shugaban Zimbabwe Ya Sauka Beijing Domin Halartar Bikin Cika Shekaru 80 Da Cimma Nasarar Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan

Shugaban Zimbabwe Ya Sauka Beijing Domin Halartar Bikin Cika Shekaru 80 Da Cimma Nasarar Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan

September 1, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda, Sun Ceto Mata Da Yara A Zamfara

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda, Sun Ceto Mata Da Yara A Zamfara

September 1, 2025
Xi Ya Gabatar Da Jawabin Bude Taron Majalisar Shugabannin Kasashe Membobin Kungiyar SCO

Xi Ya Gabatar Da Jawabin Bude Taron Majalisar Shugabannin Kasashe Membobin Kungiyar SCO

September 1, 2025
NAPTIP Da Hisbah Sun Ceto Mata 12 Da Aka Yi Safararsu A Kano Zuwa Saudiyya

NAPTIP Da Hisbah Sun Ceto Mata 12 Da Aka Yi Safararsu A Kano Zuwa Saudiyya

September 1, 2025
Antonio Guterres: Xi Jinping Shugaban Kasa Ne Mai Sanin Ya Kamata

Antonio Guterres: Xi Jinping Shugaban Kasa Ne Mai Sanin Ya Kamata

September 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.