ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Kotu Ta Aike Da Mawallafin Jaridar WikkiTimes Gidan Yari Kan Zargin Haifar Da Fitina

by Khalid Idris Doya
3 years ago
WikkiTimes

Wata kotun majistire mai lamba 3 a jihar Bauchi ta tura mawallafin jaridar yanar gizo ta WikkiTimes, Malam Haruna Muhammad Salisu zuwa gidan gyara hali kan zargin tayar da zaune-tsaye da munana wa gwamnan jihar Bauchi Bala Muhammad.

 

Alkalin Kotun, Ahmed Musa shi ne ya aike da dan jaridan gidan yari har zuwa ranar Laraba domin yanke hukunci kan bukatar bayar da beli kan kes din da kwamishinan ‘yan sandan jihar Bauchi, CP Aminu Alhassan ya shigar a kan dan jaridan.

ADVERTISEMENT
  • Kotu Ta Yi Watsi Da Bukatar Neman A Sauke Babban Sufeton ‘Yansanda

‘Yansandan dai sun zargi dan jaridan da yin hayar wasu mata domin ganin an kawo tsaiko ga zaman lafiya da kuma tayar da zaune tsaye a kusa da rumfar zabe a kauyen Duguri da ke karamar hukumar Alkaleri gami da zargin munana wa gwamna Bala a mazabarsa lamarin da ya saba wa sashi 114 na Final Kod.

 

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

Da aka gabatar da karar a ranar Talata, dan jaridan ya musanta dukkanin zarge-zargen da ake masa tare da cewa ‘bai aikata laifi ba’.

 

Lauyan kariya, Idris Gambo (SG Idrees) ya gabatar da bukatar bada belin wanda ake zargi. Idris Gambo dai ya ce, bisa la’akari da zargin da ake yi wa Haruna, za a biya bada belinsa, don haka ne ya nemi kotun ta amince da bayar da belin nasa.

 

Amma lauyan masu kara ya yi suka bisa kan bukatar belin. Lauyan ya ce, abun da ya sanya suka ki amincewa da belin shi ne rayuwar Harunan na cikin hatsari domin wasu da suke waje suna zaman jiran su far masa ta hanyar daukan doka a hannu.

 

Sai dai Lauyan Haruna, Barista Gambo ya shure dukkanin batutuwan lauyan masu karan.

 

Yana mai cewa, kamatuwa ya yi gwamnati da ‘yansanda da su tashi tsaye su fuskanci wadanda ake ce su na shirin farmakar wanda yake karewa.

 

Sai dai kuma wani lauya daga ofishin Antoni-janar na jihar Bauchi, Haruna Ibrahim ya bayyana a gaban kotun inda ya sanar da cewa, Antoni-janar na shigar na son zai karbi ragamar cigaba da kes din daga hannun ‘yansanda domin cigaba bisa amfani da kundin tsarin mulkin kasa na 1999.

WikkiTimes

Daga bisani ne dai kotun ta dage shari’ar zuwa ranar 1 ga watan Maris domin cigaba da sauraron bukatar bayar da beli.

 

Rahotonni na nuni da cewa, an cafke Haruna ne a yayin da ake zaben shugaban kasa da ‘yan majalisun tarayya a ranar Asabar inda ke daukan bidiyon wasu mata da ke zanga-zangar bayyana abun da ke damunsu a lokacin da ake gudanar da zaben a kusa da mahaiyar gwamna Bala a kauyen Duguri.

 

Sai dai, editan jaridar WikkiTimes, Yakubu Mohammed ya bayyana ta cikin wata sanarwa da ya fitar cewa, gwamnan Bauchi, Bala Muhammad na da hannu a shari’ar, ya zargi gwamnan da kokarin tauye wa dan jaridan ‘yancinsa.

WikkiTimes
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa

MASU ALAKA

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026
Manyan Labarai

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano
Labarai

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026
Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi
Manyan Labarai

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
Next Post
Sanarwar Cikakken Zama Na Biyu Na Kwamitin Kolin Jam’iyyar Kwaminis Ta Kasar Sin Karo Na 20

Sanarwar Cikakken Zama Na Biyu Na Kwamitin Kolin Jam’iyyar Kwaminis Ta Kasar Sin Karo Na 20

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026
APC Ta Dage Yakin Zaben Shugaban Kasarta A Kano

An Dakatar Da Shugaban APC Na Kebbi Da Kwamishina Kan Zaɓen Cike Gurbin Zuru

June 25, 2026
Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.