ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Kotu Ta Aike Da Mawallafin Jaridar WikkiTimes Gidan Yari Kan Zargin Haifar Da Fitina

by Khalid Idris Doya
3 years ago
WikkiTimes

Wata kotun majistire mai lamba 3 a jihar Bauchi ta tura mawallafin jaridar yanar gizo ta WikkiTimes, Malam Haruna Muhammad Salisu zuwa gidan gyara hali kan zargin tayar da zaune-tsaye da munana wa gwamnan jihar Bauchi Bala Muhammad.

 

Alkalin Kotun, Ahmed Musa shi ne ya aike da dan jaridan gidan yari har zuwa ranar Laraba domin yanke hukunci kan bukatar bayar da beli kan kes din da kwamishinan ‘yan sandan jihar Bauchi, CP Aminu Alhassan ya shigar a kan dan jaridan.

ADVERTISEMENT
  • Kotu Ta Yi Watsi Da Bukatar Neman A Sauke Babban Sufeton ‘Yansanda

‘Yansandan dai sun zargi dan jaridan da yin hayar wasu mata domin ganin an kawo tsaiko ga zaman lafiya da kuma tayar da zaune tsaye a kusa da rumfar zabe a kauyen Duguri da ke karamar hukumar Alkaleri gami da zargin munana wa gwamna Bala a mazabarsa lamarin da ya saba wa sashi 114 na Final Kod.

 

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

Da aka gabatar da karar a ranar Talata, dan jaridan ya musanta dukkanin zarge-zargen da ake masa tare da cewa ‘bai aikata laifi ba’.

 

Lauyan kariya, Idris Gambo (SG Idrees) ya gabatar da bukatar bada belin wanda ake zargi. Idris Gambo dai ya ce, bisa la’akari da zargin da ake yi wa Haruna, za a biya bada belinsa, don haka ne ya nemi kotun ta amince da bayar da belin nasa.

 

Amma lauyan masu kara ya yi suka bisa kan bukatar belin. Lauyan ya ce, abun da ya sanya suka ki amincewa da belin shi ne rayuwar Harunan na cikin hatsari domin wasu da suke waje suna zaman jiran su far masa ta hanyar daukan doka a hannu.

 

Sai dai Lauyan Haruna, Barista Gambo ya shure dukkanin batutuwan lauyan masu karan.

 

Yana mai cewa, kamatuwa ya yi gwamnati da ‘yansanda da su tashi tsaye su fuskanci wadanda ake ce su na shirin farmakar wanda yake karewa.

 

Sai dai kuma wani lauya daga ofishin Antoni-janar na jihar Bauchi, Haruna Ibrahim ya bayyana a gaban kotun inda ya sanar da cewa, Antoni-janar na shigar na son zai karbi ragamar cigaba da kes din daga hannun ‘yansanda domin cigaba bisa amfani da kundin tsarin mulkin kasa na 1999.

WikkiTimes

Daga bisani ne dai kotun ta dage shari’ar zuwa ranar 1 ga watan Maris domin cigaba da sauraron bukatar bayar da beli.

 

Rahotonni na nuni da cewa, an cafke Haruna ne a yayin da ake zaben shugaban kasa da ‘yan majalisun tarayya a ranar Asabar inda ke daukan bidiyon wasu mata da ke zanga-zangar bayyana abun da ke damunsu a lokacin da ake gudanar da zaben a kusa da mahaiyar gwamna Bala a kauyen Duguri.

 

Sai dai, editan jaridar WikkiTimes, Yakubu Mohammed ya bayyana ta cikin wata sanarwa da ya fitar cewa, gwamnan Bauchi, Bala Muhammad na da hannu a shari’ar, ya zargi gwamnan da kokarin tauye wa dan jaridan ‘yancinsa.

WikkiTimes
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ATBU Ta Janye Filin Ginin Masallaci Da Ta Bai wa TIMSAN, Ta Amince Kowa Ya Yi Addininsa Yadda Ya Fahimta
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu

MASU ALAKA

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027
Labarai

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

July 16, 2026
Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu
Manyan Labarai

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

July 16, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai
Siyasa

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

July 16, 2026
Next Post
Sanarwar Cikakken Zama Na Biyu Na Kwamitin Kolin Jam’iyyar Kwaminis Ta Kasar Sin Karo Na 20

Sanarwar Cikakken Zama Na Biyu Na Kwamitin Kolin Jam’iyyar Kwaminis Ta Kasar Sin Karo Na 20

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 16, 2026
Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

July 16, 2026
Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

July 16, 2026
Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

July 16, 2026
Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam

Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam

July 16, 2026
Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

July 16, 2026
Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

July 16, 2026
Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

July 16, 2026
An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

July 16, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

July 16, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.