ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Kotu Ta Aike Da Mawallafin Jaridar WikkiTimes Gidan Yari Kan Zargin Haifar Da Fitina

by Khalid Idris Doya
3 years ago
WikkiTimes

Wata kotun majistire mai lamba 3 a jihar Bauchi ta tura mawallafin jaridar yanar gizo ta WikkiTimes, Malam Haruna Muhammad Salisu zuwa gidan gyara hali kan zargin tayar da zaune-tsaye da munana wa gwamnan jihar Bauchi Bala Muhammad.

 

Alkalin Kotun, Ahmed Musa shi ne ya aike da dan jaridan gidan yari har zuwa ranar Laraba domin yanke hukunci kan bukatar bayar da beli kan kes din da kwamishinan ‘yan sandan jihar Bauchi, CP Aminu Alhassan ya shigar a kan dan jaridan.

ADVERTISEMENT
  • Kotu Ta Yi Watsi Da Bukatar Neman A Sauke Babban Sufeton ‘Yansanda

‘Yansandan dai sun zargi dan jaridan da yin hayar wasu mata domin ganin an kawo tsaiko ga zaman lafiya da kuma tayar da zaune tsaye a kusa da rumfar zabe a kauyen Duguri da ke karamar hukumar Alkaleri gami da zargin munana wa gwamna Bala a mazabarsa lamarin da ya saba wa sashi 114 na Final Kod.

 

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

Dangote Ya Rage Farashin Fetur Zuwa N1,125 Kan Kowace Lita

Da aka gabatar da karar a ranar Talata, dan jaridan ya musanta dukkanin zarge-zargen da ake masa tare da cewa ‘bai aikata laifi ba’.

 

Lauyan kariya, Idris Gambo (SG Idrees) ya gabatar da bukatar bada belin wanda ake zargi. Idris Gambo dai ya ce, bisa la’akari da zargin da ake yi wa Haruna, za a biya bada belinsa, don haka ne ya nemi kotun ta amince da bayar da belin nasa.

 

Amma lauyan masu kara ya yi suka bisa kan bukatar belin. Lauyan ya ce, abun da ya sanya suka ki amincewa da belin shi ne rayuwar Harunan na cikin hatsari domin wasu da suke waje suna zaman jiran su far masa ta hanyar daukan doka a hannu.

 

Sai dai Lauyan Haruna, Barista Gambo ya shure dukkanin batutuwan lauyan masu karan.

 

Yana mai cewa, kamatuwa ya yi gwamnati da ‘yansanda da su tashi tsaye su fuskanci wadanda ake ce su na shirin farmakar wanda yake karewa.

 

Sai dai kuma wani lauya daga ofishin Antoni-janar na jihar Bauchi, Haruna Ibrahim ya bayyana a gaban kotun inda ya sanar da cewa, Antoni-janar na shigar na son zai karbi ragamar cigaba da kes din daga hannun ‘yansanda domin cigaba bisa amfani da kundin tsarin mulkin kasa na 1999.

WikkiTimes

Daga bisani ne dai kotun ta dage shari’ar zuwa ranar 1 ga watan Maris domin cigaba da sauraron bukatar bayar da beli.

 

Rahotonni na nuni da cewa, an cafke Haruna ne a yayin da ake zaben shugaban kasa da ‘yan majalisun tarayya a ranar Asabar inda ke daukan bidiyon wasu mata da ke zanga-zangar bayyana abun da ke damunsu a lokacin da ake gudanar da zaben a kusa da mahaiyar gwamna Bala a kauyen Duguri.

 

Sai dai, editan jaridar WikkiTimes, Yakubu Mohammed ya bayyana ta cikin wata sanarwa da ya fitar cewa, gwamnan Bauchi, Bala Muhammad na da hannu a shari’ar, ya zargi gwamnan da kokarin tauye wa dan jaridan ‘yancinsa.

WikkiTimes
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa

MASU ALAKA

Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara
Labarai

Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

June 25, 2026
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN
Labarai

Dangote Ya Rage Farashin Fetur Zuwa N1,125 Kan Kowace Lita

June 25, 2026
Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Sabon Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano
Manyan Labarai

Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Sabon Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

June 25, 2026
Next Post
Sanarwar Cikakken Zama Na Biyu Na Kwamitin Kolin Jam’iyyar Kwaminis Ta Kasar Sin Karo Na 20

Sanarwar Cikakken Zama Na Biyu Na Kwamitin Kolin Jam’iyyar Kwaminis Ta Kasar Sin Karo Na 20

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

June 25, 2026
Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta

Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta

June 25, 2026
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN

Dangote Ya Rage Farashin Fetur Zuwa N1,125 Kan Kowace Lita

June 25, 2026
Adadin Injunan Samar Da Wutar Lantarki Da Sin Ya Wuce Kilowatts Awa Biliyan 4, Wato Ya Kai Ga Matsayi Na Farko A Duniya

Adadin Injunan Samar Da Wutar Lantarki Da Sin Ya Wuce Kilowatts Awa Biliyan 4, Wato Ya Kai Ga Matsayi Na Farko A Duniya

June 25, 2026
Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Sabon Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Sabon Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

June 25, 2026
Wani Gidan Adana Kayan Tarihi Na Sin Ya Fitar Da Rahoton Yadda Dakarun Japan Suka Rika Zubawa Mutane Jinin Dabbobi Yayin Yakin Duniya Na Biyu

Wani Gidan Adana Kayan Tarihi Na Sin Ya Fitar Da Rahoton Yadda Dakarun Japan Suka Rika Zubawa Mutane Jinin Dabbobi Yayin Yakin Duniya Na Biyu

June 25, 2026
Wang Yi Ya Yi Kira Da A Gaggauta Bude Mashigin Hormuz

Wang Yi Ya Yi Kira Da A Gaggauta Bude Mashigin Hormuz

June 25, 2026
Ƙungiyar NPCF Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Ga Tinubu

Ƙungiyar NPCF Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Ga Tinubu

June 25, 2026
Firaministan Sin Ya Halarci Taron Tattaunawa Da Wakilan ‘Yan Kasuwa Mahalarta Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na DAVOS

Firaministan Sin Ya Halarci Taron Tattaunawa Da Wakilan ‘Yan Kasuwa Mahalarta Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na DAVOS

June 25, 2026
Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.