• English
  • Business News
Monday, September 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Za Mu Yi Amfani Da Na’urar BVAS Wajen Dakile Magudin Zabe – Farfesa Mahmood

by Sulaiman
3 years ago
in Labarai
0
2023: Za Mu Yi Amfani Da Na’urar BVAS Wajen Dakile Magudin Zabe – Farfesa Mahmood
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC), ta sha alwashin cewa yanzu haka ta na aiki tare da Hukumar Sadarwa ta Ƙasa (NCC), domin magance duk wani cikas ɗin da za a iya fuskanta yayin aikawa da sakamakon zaɓen 2023 ta tsarin yaɗa sakamakon ƙuri’u ta BVAS.

 

Shugaban INEC, Farfesa Mahmoud Yakubu ne ya bayyana haka, ya na mai cewa an fara shiri tun a yanzu domin magance ko da wata matsala za ta bijiro saboda matsalar wuraren da saƙonni ta fasahar zamani ke wahalar isa, wato matsalar ‘network’.

  • Jerin Kayayyakin Da INEC Ta Yi Asara Bayan Kai Mata Hare-hare A Ofisoshinta

 

Yakubu ya bayyana haka a Legas, lokacin da ya ke ganawa da manema labarai, a ranar Juma’a.

Labarai Masu Nasaba

Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja

KEDCO Ta Mayar Da Wutar Lantarki A Asibitin Aminu Kano

 

Wannan ƙarin haske da shugaban na INEC ya yi, ya biyo bayan damuwar da wasu ‘yan Nijeriya su ka fara nunawa cewa, za a iya samun matsala da tsarin BVAS a yankunan da ke fama da cikas ɗin samun saƙo ko yaɗa saƙon ta fasahar zamani.

BVAS
Taron INEC da manema labarai a Legas

Yakubu ya ce a ranar Talata INEC za ta gana da jami’an hukumar sadarwa (NCC), dangane da yadda za a magance matsalar da ka iya tasowa wajen aika sakamakon zaɓe ta hanyar amfani da BVAS.

 

Daga nan sai ya tabbatar wa ‘yan Nijeriya cewa kada su yi fargabar komai dangane da nagartar da zaɓen 2023 zai yi, ta hanyar amfani da BVAS.

 

“INEC ta gano waɗansu wuraren da ke da matsalar ingancin ‘network’ da kuma wuraren da babu ‘network’ ɗin kwata-kwata. Kuma mu na nan mu na aikin tabbatar da cewa ba a samu wata matsala wajen aika sakamakon zaɓen yankunan ba.

 

“Mu na ta aiki da jajircewar ganin tabbas mun aika dukkan saƙonnin sakamakon zaɓe ko ina a faɗin ƙasar nan,” inji shi.

 

Tun da farko sai da Kakakin Yaɗa Labarai na INEC, Festus Okoye ya roƙi kakafen yaɗa labarai su taimaka wa hukumar zaɓen ta hanyar daƙile bayanan ƙarya da labaran shaci-faɗin da ake dangantawa da INEC.

 

Ya ce ga shi dai bai fi sauran kwanaki 85 a yi zaɓe ba, amma labaran bogin da ake yaɗawa kan INEC abin damuwa ne sosai.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yan Bindiga Sun Sace Kwamishina A Binuwai Da Yin Awon-Gaba Da Wasu Mutum 3

Next Post

2023: Tinubu Na Gabatatar Da Jawabi Kan Zabe A Fadar Chatham Da Ke Ingila

Related

Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja
Manyan Labarai

Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja

1 hour ago
KEDCO Ta Mayar Da Wutar Lantarki A Asibitin Aminu Kano
Manyan Labarai

KEDCO Ta Mayar Da Wutar Lantarki A Asibitin Aminu Kano

3 hours ago
Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Fasinjoji 17 A Zamfara
Labarai

Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Fasinjoji 17 A Zamfara

4 hours ago
An Gano Gawar Yarinyar da Ruwan Sama Ya Tafi Da ita A Zariya
Labarai

An Gano Gawar Yarinyar da Ruwan Sama Ya Tafi Da ita A Zariya

16 hours ago
Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba
Manyan Labarai

Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba

17 hours ago
Bayan Fara Kamen Mabarata, An Samu Dalar Amurka, Wuƙa A Kwara
Labarai

Bayan Fara Kamen Mabarata, An Samu Dalar Amurka, Wuƙa A Kwara

19 hours ago
Next Post
2023: Tinubu Na Gabatatar Da Jawabi Kan Zabe A Fadar Chatham Da Ke Ingila

2023: Tinubu Na Gabatatar Da Jawabi Kan Zabe A Fadar Chatham Da Ke Ingila

LABARAI MASU NASABA

Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja

Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja

September 15, 2025
Arewa Ba Zata Ƙarɓi Mulki A 2027 Ba, Gwamna  Bago

Arewa Ba Zata Ƙarɓi Mulki A 2027 Ba, Gwamna  Bago

September 15, 2025
KEDCO Ta Mayar Da Wutar Lantarki A Asibitin Aminu Kano

KEDCO Ta Mayar Da Wutar Lantarki A Asibitin Aminu Kano

September 15, 2025
Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Fasinjoji 17 A Zamfara

Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Fasinjoji 17 A Zamfara

September 15, 2025
Barcelona Ta Farfaɗo Zuwa Matsayi Na Biyu Bayan Lallasa Valencia A Johan Cruyff

Barcelona Ta Farfaɗo Zuwa Matsayi Na Biyu Bayan Lallasa Valencia A Johan Cruyff

September 15, 2025
Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)

Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)

September 14, 2025
Sin Da Amurka Sun Fara Gudanar Da Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Madrid

Sin Da Amurka Sun Fara Gudanar Da Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Madrid

September 14, 2025
An Gano Gawar Yarinyar da Ruwan Sama Ya Tafi Da ita A Zariya

An Gano Gawar Yarinyar da Ruwan Sama Ya Tafi Da ita A Zariya

September 14, 2025
Kano Pillars Ta Samu Nasarar Farko A Gasar Firimiyar Nijeriya Ta Bana

Kano Pillars Ta Samu Nasarar Farko A Gasar Firimiyar Nijeriya Ta Bana

September 14, 2025
Za A Kaddamar Da Fim Mai Taken 731 A Sassan Duniya

Za A Kaddamar Da Fim Mai Taken 731 A Sassan Duniya

September 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.