• English
  • Business News
Saturday, July 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jerin Kayayyakin Da INEC Ta Yi Asara Bayan Kai Mata Hare-hare A Ofisoshinta

by Sulaiman
3 years ago
in Labarai
0
Jerin Kayayyakin Da INEC Ta Yi Asara Bayan Kai Mata Hare-hare A Ofisoshinta
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC), Farfesa Mahmood Yakubu, ya bayyana cewa hukunta masu kai hare-hare da lalata dukiya da kayayyakin hukumar a faɗin ƙasar nan cikin hanzari ita ce hanyar da za a bi a magance matsalar. 

 

Yakubu ya faɗi haka ne a lokacin buɗe taron kwana biyu don buɗe idon Zaunannun Kwamishinonin Zaɓen hukumar (RECs) da aka yi a Legas a ranar Laraba.

  • 2023: Dallinmu Na Wallafa Kuri’un Zaben Shugaban Kasa Miliyan 187 –INEC

Kamfanin Dillancin Labarai na Nijeriya (NAN) ya ruwaito cewa Hukumar Cigaban Ƙasashe ta Majalisar Ɗinkin Duniya (UNDP) ita ce ta ɗauki nauyin shirya taron.

 

Labarai Masu Nasaba

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

A jawabin sa na buɗe taron, Yakubu ya bayyana cewa a cikin watanni huɗu da su ka gabata, wasu mutane da ba a san ko su waye ba sun kai hare-hare a ofisoshin hukumar da ke ƙananan hukumomi biyar na ƙasar nan.

INEC
Kwamishinonin zaɓe a taron

A cewar sa, muhimman kayayyaki da dukiyoyi sun salwanta a lokacin waɗannan hare-haren, don haka ya kamata a magance abin da ke faruwa a cikin gaggawa.

 

Ya ce: “Waɗannan kayayyakin sun haɗa da jimillar akwatunan zaɓe guda 1,992, da rumfunan zaɓe 399 da janaretocin ba da wuta guda 22, da kuma dubban katinan zaɓe da ba a kai ga karɓa ba, da wasu kayan.

 

“Tilas ne a dakatar da waɗannan hare-haren kuma a kai masu aikata su kotu. Aikin mu shi ne mu gudanar da zaɓe. Hanyar da ta fi dacewa domin magance matsalar ita ce a kama masu kai hare-haren a gurfanar da su a kotu.

 

“Babban maganin matsalar shi ne a kama ɓata-garin a hukunta su saboda ‘yan iska da masu ƙone-ƙone su daina tunanin cewa an amince da aikin assha a ƙasar mu. A gaskiya, abin baƙin ciki ne a ce ana yin wannan a lokacin da zaɓuɓɓuka ke ƙaratowa.

 

“Sai dai kuma, ina so in tabbatar wa da ‘yan Nijeriya cewa za mu ga bayan waɗannan hare-haren, za a maye gurbin waɗannan kayan. To amma akwai iyakar yadda za mu iya ci gaba da maye gurbin kayayyakin da mu ka rasa a yayin da ya rage mana kwana 86 kacal kafin ranar babban zaɓe.”

 

A cewar sa, hukumar za ta ci gaba da yin aiki tare da hukumomin tsaro, sarakunan gargajiya da shugabannin al’umma da dukkan mutanen kirki ‘yan Nijeriya domin hana hare-haren.

 

Ya ce INEC ta duƙufa wajen tabbatar da cewa babu abin da zai hana a gudanar da zaɓuɓɓuka kamar yadda aka tsara, “kuma muradin al’ummar Nijeriya zai cika. Wannan shi ne mu ke ƙara tabbatar wa da ‘yan Nijeriya.”

 

A game da taron buɗe idon, Yakubu ya ce wani ɓangare ne na shirye-shiryen da ake yi domin manyan zaɓuɓɓukan shekarar 2023.

 

Ya ce: “Mu na yin taro ne da dukkan Zaunannun Kwamishinonin Zaɓe domin mu na sane da cewa an rantsar da 19 daga cikin su kimanin mako huɗu da su ka gabata.

 

“Mun yi tunanin cewa ya kamata a shirya masu taron buɗe ido domin su fahimci hanyoyi da ƙa’idojin aiki saboda za a yi zaɓe nan da kwana 86.”

 

Shugaban na INEC ya ce taron buɗe idon zai kuma mai da hankali ga ainihin ƙa’idar aiki kan karɓar katittikan zaɓe, da ƙa’idojin rarraba masu zaɓe zuwa rumfunan zaɓe, da tsarin yadda ake raba kayan zaɓe, da dokokin ɗabi’u da halayyar membobi da jami’ai da ma’aikatan hukumar.

 

Yakubu ya ce za a rarraba kwafe-kwafe na dokokin ɗabi’ar membobi da jami’ai da ma’aikatan hukumar ga kowa da kowa.

 

Ya ƙara da cewa: “Ina so in nanata cewa samun nasarar mu a ƙarshe ya dogara ne kan mutuncin mu. Tilas mu zama ba mu kowane ɓangare kuma ba mu goyon bayan kowa.

 

“Hukumar ba jam’iyyar siyasa ba ce. Hukumar ba ta da ‘yan takara a zaɓuɓɓukan da ke tafe.

 

“Dukkan jam’iyyun siyasa daidai su ke da juna a wajen hukumar. Zaɓi ya rage wa ‘yan Nijeriya, wato masu zaɓe.

 

“Aikin mu shi ne mu tabbatar da darajar ƙuri’u, ba daɗi ba ƙari.”

 

Da ya ke magana kan ji-ta-ji-tar da ake yaɗawa wai mutum zai iya kaɗa ƙuri’a ba tare da katin zaɓe ba a ranar zaɓe, Yakubu ya bayyana wannan maganar da cewa “ko kaɗan ba gaskiya ba ce,” ya na cewa, “kafin kowane mutum ya yi zaɓe, sai ya kasance ya yi rajista a matsayin mai zaɓe, kuma an ba shi katin zaɓe.

 

“Tun tuni hukumar ta fito da dokar cewa ‘ba katin zaɓe, ba zaɓe’. Babu abin da ya canza. Dokar ce ta tanadar da hakan, saboda haka in aka yi wani abu daban to an karya dokar.

 

“Ina kira ga ‘yan Nijeriya da su yi watsi da irin waɗannan shaci-faɗin cewa wai mutum zai iya kaɗa ƙuri’a a ranar zaɓe ba tare da katin zaɓe ba.”

 

Da ya ke yaba wa UNDP saboda ɗaukar nauyin shirya taron da ta yi, Yakubu ya ce haɗin gwiwar da ta daɗe ta na yi da INEC ya jima kuma ya taimaka gaya wajen yauƙaƙa cigaban da ake samu a wajen harkokin shirya zaɓe.

 

A saƙon sa na fatan alheri, Mista Deryck Fritz, wanda shi ne babban mashawarcin UNDP, ya yi kira ga kwamishinonin da su dage sosai wajen aiwatar da tsare-tsaren hukumar kuma su kasance kan gaba wajen masu magance matsaloli idan sun taso.

 

Ya ce su ne za su sa ido kan aiwatar da dukkan ayyukan da su ka rataya a wuyan hukumar kamar yadda aka ba su amana.

 

Ya ce: “Ku ne waɗanda za su yi aiki ba tare da goyon baya ba da ‘yan siyasa.

 

“Ku ne waɗanda za su yi aiki da abokan hulɗa da ke yankunan ku da ƙungiyoyin ‘yan sa kai, da hukumomin jiha, da goyon bayan ƙungiyoyin sufuri, da sauran masu ayyuka, da ‘yan sanda da sauran hukumomin tsaro.

 

“A wannan waƙati na gasar Kofin Duniya, ana tuna mana da cewa zaɓuɓɓuka masu nasara, kamar gasannin ƙwallon ƙwafa masu nasara, su na samuwa ne sakamakon haɗin kai tare da aiki tare.”

 

Fritz ya ce a yadda wasu ke kallon abin, wannan cigaba da ake samu wajen aikin shirya zaɓe ba zai taɓa sauyawa ba, amma kamar yadda ya ke faruwa a kowane zaɓe, akwai matsalolin da ka taso, kamar siyasar kasuwa da kuma matsalolin tsaro.

 

Ya ce irin waɗannan ƙalubale za su jarraba ƙarfin hanyoyi da dokokin INEC, har ma da sadaukarwar ma’aikatan ta.

 

Ya ce tsarin dimokiraɗiyya, a sassa da dama na duniya, ya na fuskantar barazana, ya ƙara da cewa samar da tsari mai ƙarfi ne zai yi maganin wannan barazanar.

 

Ya ce, “Idan kuma ana kokwanto kan tsarin da ke akwai game da ɗabi’ar tsarin, ko ana zargin masu gudanar da zaɓe, ko ma a ce an yi murɗiya, ya na da muhimmanci ya kasance akwai tsari mai nagarta wanda aka amince da shi da zai tunkari waɗannan matsalolin, a madadin a yi tarzomar zaɓe da rikicin siyasa.

 

“INEC a matsayin ta na hukumar da tsarin mulki ya ba alhaki, tilas ta kasance kuma a ga ta kasance ba ta nuna wariya a matsayin ta na alƙalin zaɓe.”

 

Dukkan Zaunannun Kwamishinonin Zaɓe na INEC da manyan ma’aikatan hukumar sun halarci taron.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Matan Tubabbun ‘Yan Boko Haram Sun Haifi Jarirai 262 A Wata 4 Kacal

Next Post

Dalilin Ci Gaba Da Fuskantar Karancin Mai A Fadin Nijeriya – Dillalai

Related

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai
Ra'ayi Riga

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

10 hours ago
2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a
Rahotonni

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

11 hours ago
Illar Kakaba Wa Majalisa Ta 10 Shugabanni Ga Gwamnatin Tinubu – Dattawan Arewa
Labarai

Majalisar Tarayya Ta Karrama NPA Da Kyautar Gaskiya Da Riƙon Amana Ta 2025

13 hours ago
Sojoji Sun Sake Ceto ‘Yan Matan Makarantar Chibok 2
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kama Mutum 2 Da AK-47 A Taraba

14 hours ago
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa
Labarai

Amurka Ta Rage Wa’adin Bizar ‘Yan Nijeriya Zuwa Wata Uku

15 hours ago
Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Alaƙanta Shettima Da Kwatanta Jonathan Da Tinubu Kan Batun Tsige Gwamna
Labarai

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Alaƙanta Shettima Da Kwatanta Jonathan Da Tinubu Kan Batun Tsige Gwamna

16 hours ago
Next Post
Dalilin Ci Gaba Da Fuskantar Karancin Mai A Fadin Nijeriya – Dillalai

Dalilin Ci Gaba Da Fuskantar Karancin Mai A Fadin Nijeriya – Dillalai

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

July 11, 2025
Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

July 11, 2025
Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

July 11, 2025
Nijeriya Na Fuskantar Siyasa Mara Tabbas —  Peter Obi

2027: Takarar Shugaban Kasa Zan Yi Ba Mataimaki Ba – Peter Obi

July 11, 2025
“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

July 11, 2025
2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

July 11, 2025
Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

July 11, 2025
Fahimtar Kyawun Bambance-Bambance Kyakkawar Hanya Ce Ta Wanzar Da Zaman Jituwa A Duniya

Fahimtar Kyawun Bambance-Bambance Kyakkawar Hanya Ce Ta Wanzar Da Zaman Jituwa A Duniya

July 11, 2025
Illar Kakaba Wa Majalisa Ta 10 Shugabanni Ga Gwamnatin Tinubu – Dattawan Arewa

Majalisar Tarayya Ta Karrama NPA Da Kyautar Gaskiya Da Riƙon Amana Ta 2025

July 11, 2025
FRCN Ya Kaddamar Da Shirin Koyar Da Sinanci Mai Taken “Hello China”

FRCN Ya Kaddamar Da Shirin Koyar Da Sinanci Mai Taken “Hello China”

July 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.