• English
  • Business News
Saturday, August 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya da Ofishin Jakadancin Amurka Sun Haɗa Gwiwa Don Wayar Da Kan ‘Yan Nijeriya Kan Sababbin Ƙa’idojin Samun Biza

by Sulaiman
16 hours ago
in Labarai
0
Gwamnatin Tarayya da Ofishin Jakadancin Amurka Sun Haɗa Gwiwa Don Wayar Da Kan ‘Yan Nijeriya Kan Sababbin Ƙa’idojin Samun Biza
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Tarayya ta haɗa gwiwa da Ofishin Jakadancin Amurka a Nijeriya domin wayar da kan ‘yan Nijeriya kan sababbin ƙa’idojin neman bizar Amurka tare da tabbatar da bin ƙa’ida yayin neman.

 

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, shi ne ya bayyana haka a taron manema labarai da ya gudana tare da Jakaden Amurka a Nijeriya, Richard M. Mills Jr., a Abuja ranar Juma’a.

  • Sin Ta Mika Sabon Kason Tallafin Abinci Ga Zimbabwe
  • Bango Ya Kashe Mutum 6, Ya Raunata Wasu A Katsina

Ya ce wannan yekuwar wayar da kan ta zama dole saboda Amurka tana ci gaba da zama ɗaya daga cikin wuraren da ‘yan Nijeriya suke yawan ziyarta.

 

Labarai Masu Nasaba

An Naɗa Farfesa Adamu Muƙamin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja

Gwamnan Kano Ya Sallami Mataimaka Biyu Kan Zargin Karkatar Da Kayan Tallafi

Idris ya ce a tsawon shekaru ‘yan Nijeriya suna tafiya Amurka saboda dalilai daban-daban, ciki har da yawon buɗe ido, kasuwanci, karatu, da kuma neman magani.

 

Ya ce: “An san Nijeriya a duniya a matsayin ƙasar da ‘yan ƙasar ta suke yawan yin tafiya zuwa ƙasashe daban-daban, suna hulɗa da ƙasashen duniya ta fuskar harkar kasuwanci, ilimi, yawon buɗe ido, da sauran muhimman fannoni. Amurka na ci gaba da kasancewa ɗaya daga cikin wuraren da ‘yan Nijeriya suka fi ziyarta, abin da ke nuna zurfin dangantaka mai tsawo tsakanin ƙasashen biyu.

 

“Yawancin ‘yan Nijeriya suna zuwa Amurka ne domin karatu, aiki, neman magani, ziyartar ‘yan’uwa, yawon buɗe ido, da damar zuba jari.

 

“Wannan mu’amala mai ƙarfi tana ci gaba da bunƙasa al’ummomin biyu.

 

“Sababbin abubuwan da Ofishin Jakadancin Amurka ya bayyana game da sauye-sauye a ayyukan ofishin jakadancin da hanyoyin neman bizar sun jima suna cikin labarai kwanan nan.

 

“Waɗannan sauye-sauyen, kamar yadda Ofishin Jakadancin Amurka ya bayyana, wani ɓangare ne na ƙoƙarin inganta bayar da sabis, ƙara saurin aiki, da mayar da martani ga sauye-sauyen buƙatun ayyukan jakadanci.”

 

Ministan ya yaba wa gwamnatin Amurka bisa ƙoƙarin yin bayani kai-tsaye ga ‘yan Nijeriya a wannan taro tare da tabbatar da samun sahihan bayanai na zamani ga kowa.

 

Haka kuma ya jaddada girmamawa da haɗin gwiwa tsakanin Nijeriya da Amurka da kuma jajircewar Ofishin Jakadancin wajen sanar da matafiya ‘yan Nijeriya.

 

A nasa jawabin, Jakaden Amurka, Ambasada Mills, ya ce bin ƙa’idojin neman biza da dokokin Amurka na ‘yan Nijeriya abu ne mai muhimmanci wajen ƙarfafa dangantaka tsakanin ƙasashen biyu.

 

“Bin dokokin neman biza na Amurka ba kawai wani nauyi ba ne, amma ginshiƙi ne na amincewa da girmama juna tsakanin ƙasashen biyu,” inji Ambasada Millis.

 

Ya ƙara da cewa: “Kamar yadda Minista ya bayyana, ni da shi mun yi tattaunawa mai amfani game da dokokin biza na Amurka da kuma yadda za mu isar wa ‘yan Nijeriya muhimmancin bin waɗannan dokokin.

 

“Bari in fayyace cewa Amurka tana daraja ƙarfaffar dangantakar ta da Nijeriya da kuma nau’o’in hulɗa da yawa da ke tsakanin ƙasashen biyu.

 

“Bizar Amurka na taka muhimmiyar rawa wajen ci gaba da riƙe waɗannan lamurran dangantaka da ƙarfafa su, ko ta hanyar bai wa mutane damar tafiya domin ilimi, kasuwanci, yawon buɗe ido, ko musayar al’adu.”

 

Jakaden ya jaddada cewa ya zama dole a yi amfani da biza bisa ga dokoki da ƙa’idojin Amurka.

 

Ya ce: “Tabbas, muna maraba da baƙi ‘yan Nijeriya a Amurka kamar yadda Nijeriya take maraba da ‘yan Amurka masu zuwa wannan ƙasa. Dukkan gwamnatoci suna son baƙi su girmama dokokin ƙasashen mu da ƙa’idojin mu.”

 

Ya gargaɗi masu neman biza cewa yin amfani da ita ba bisa ƙa’ida ba ko bayar da bayanan ƙarya yayin neman ta yana iya rage amincewar juna a tsakanin ƙasashen biyu.

 

Ya ce: “Muna kira ga dukkan masu neman biza da su bayar da sahihan bayanai kuma su bi sharuɗɗan biza ɗin su, domin na sani, mafi yawan ‘yan Nijeriya suna yin hakan. Ta yin haka, za mu ƙarfafa ɗorewar zumunci tsakanin ƙasashen mu.”

 

Ambasada Mills ya kuma yaba wa Idris bisa jajircewar sa wajen kare ‘yancin faɗar albarkacin baki a Nijeriya, yana mai jaddada cewa wannan ɗabi’a ce da ta yi daidai da manufofin Amurka.

 

Ya kuma yaba wa haɗin kai da ake samu daga hukumomin Nijeriya, ciki har da Hukumar Wayar da Kan Jama’a ta Ƙasa, Hukumar Shige da Fice ta Nijeriya, Hukumar Kwastan ta Nijeriya, da Fadar Shugaban Ƙasa, wajen wayar da kan jama’a kan ƙa’idojin biza.

 

Haka kuma ya shawarci ‘yan Nijeriya da su nemi sahihan bayanai daga shafin soshiyal midiya na Ofishin Jakadancin Amurka kuma su tabbatar da cewa duk wata tambaya da suke da ita za su samu amsa cikin lokaci.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Shin Amurka Ta Manta Da Azabar “Babban Koma-Baya” Tare Da Haraji Mafi Yawa a Lokacin Na Tsawon Kusan Karni?

Next Post

Xi Jinping Ya Zanta Da Putin Ta Wayar Tarho

Related

An Naɗa Farfesa Adamu Muƙamin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja
Manyan Labarai

An Naɗa Farfesa Adamu Muƙamin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja

4 minutes ago
Gwamnan Kano Ya Sallami Mataimaka Biyu Kan Zargin Karkatar Da Kayan Tallafi
Labarai

Gwamnan Kano Ya Sallami Mataimaka Biyu Kan Zargin Karkatar Da Kayan Tallafi

1 hour ago
Tsohon Shugaban PDP Audu Ogbeh Ya Rasu
Labarai

Tsohon Shugaban PDP Audu Ogbeh Ya Rasu

2 hours ago
Sai An Magance Matsalar Asusun Haɗin Gwiwa, Za A Tabbatar Da Cin Gashin Kan Ƙananan Hukumomi
Labarai

Sai An Magance Matsalar Asusun Haɗin Gwiwa, Za A Tabbatar Da Cin Gashin Kan Ƙananan Hukumomi

4 hours ago
Ƴan Bindiga Sun Sace Fasinjoji 9 A Kogi
Labarai

Ƴan Bindiga Sun Sace Fasinjoji 9 A Kogi

7 hours ago
Bashir Ojulari: Me Ya Sa Ake Tsoron Gaskiya Ta Yi Aiki A NNPC? 
Labarai

Bashir Ojulari: Me Ya Sa Ake Tsoron Gaskiya Ta Yi Aiki A NNPC? 

18 hours ago
Next Post
Xi Jinping Ya Zanta Da Putin Ta Wayar Tarho

Xi Jinping Ya Zanta Da Putin Ta Wayar Tarho

LABARAI MASU NASABA

An Naɗa Farfesa Adamu Muƙamin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja

An Naɗa Farfesa Adamu Muƙamin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja

August 9, 2025
Gwamnan Kano Ya Sallami Mataimaka Biyu Kan Zargin Karkatar Da Kayan Tallafi

Gwamnan Kano Ya Sallami Mataimaka Biyu Kan Zargin Karkatar Da Kayan Tallafi

August 9, 2025
Tsohon Shugaban PDP Audu Ogbeh Ya Rasu

Tsohon Shugaban PDP Audu Ogbeh Ya Rasu

August 9, 2025
Ina Fatan Taka Inda Yayana Ya Taka A Fagen Ƙwallon Ƙafa A Duniya -Jobe Bellingham

Ina Fatan Taka Inda Yayana Ya Taka A Fagen Ƙwallon Ƙafa A Duniya -Jobe Bellingham

August 9, 2025
Sai An Magance Matsalar Asusun Haɗin Gwiwa, Za A Tabbatar Da Cin Gashin Kan Ƙananan Hukumomi

Sai An Magance Matsalar Asusun Haɗin Gwiwa, Za A Tabbatar Da Cin Gashin Kan Ƙananan Hukumomi

August 9, 2025
Tinubu Ya Gwangwaje Ƴan Wasan Ƙwallon Kwando Ta Mata Da Dala $100,000 Kowace

Jerin Ƴan Wasa Mata Da Suka Samu Kyautar Dala 100,000 Daga Gwamnatin Nijeriya

August 9, 2025
Afrika Ba Ta Cikin Jerin Fannonin Da Muke Ba Fifiko – Amurka

Afrika Ba Ta Cikin Jerin Fannonin Da Muke Ba Fifiko – Amurka

August 9, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Fasinjoji 9 A Kogi

Ƴan Bindiga Sun Sace Fasinjoji 9 A Kogi

August 9, 2025
ADA/ADC, APC Da PDP: Jam ’iyyun Siyasa Da Ke Shan Jinin ’Yan Nijeriya

ADA/ADC, APC Da PDP: Jam ’iyyun Siyasa Da Ke Shan Jinin ’Yan Nijeriya

August 9, 2025
Xi Jinping Ya Zanta Da Putin Ta Wayar Tarho

Xi Jinping Ya Zanta Da Putin Ta Wayar Tarho

August 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.