ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, September 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Afrika Ba Ta Cikin Jerin Fannonin Da Muke Ba Fifiko – Amurka

by Rabi'u Ali Indabawa
1 year ago
Amurka

Shugaban Amurka Donald Trump ya riga ya kwashe watanni shida yana mulki a ƙasarsa. Ayyukan da ya yi a waɗannan watanni sun bayyanawa ƙasashen Afirka ƙarara cewa, Afirka ba ta cikin jerin fannoni da ƙasar Amurka ta bai wa fifiko.

Idan aka kwatanta da wa’adin shugaba Trump na farko, wanda ya ƙunshi yadda ya yi wa ƙasashen Afirka wulaƙanci ta hanyar kiransu da laƙabai marasa daɗin ji, da rashin kulawa da ya nuna wa nahiyar (ya gana da shugabannin ƙasashen Afirka biyu kaɗai, kuma bai taɓa ziyartar Afirka ba), shugaba Trump ya ƙara ɗaukar matakai kan Afirka a wa’adinsa na biyu.

  • Kamfanin Sinotruk Na Kasar Sin Ya Kaddamar Da Sabbin Motocin Dakon Kaya A Kenya
  • Shin Amurka Ta Manta Da Azabar “Babban Koma-Baya” Tare Da Haraji Mafi Yawa a Lokacin Na Tsawon Kusan Karni?

Misali, ya rufe Hukumar Raya Ƙasashen Duniya ta Amurka (USAID), tare da rage yawan tallafin da ƙasar take bai wa Afirka. Ya kuma bayyana shirinsa na soke shirin ƙasarsa na tallafa wa ƙoƙarin yaƙi da cutar kanjamau a duniya (PEPFAR), duk da cewa lamarin zai iya haddasa asarar miliyoyin rayuka a Afirka.

ADVERTISEMENT

Kazalika, manufar karɓar karin harajin fito da shugaba Trump ya ƙaddamar za ta ƙara wa ƙasashen Afirka nauyi sosai. Kana wani umurnin da ya saka masa hannu a baya-bayan nan shi ne taƙaita damar ‘yan ƙasashen Afirka bakwai, ciki har da Najeriya da Kamaru, ta fuskar bizar zuwa Amurka.

Afirka ta Kudu yana ɗaya daga cikin ƙasashen Afirka da suka fuskanci matsin lamba na musamman daga Shugaba Trump: Amurka ta kori jakadanta, kuma manyan jami’an Ƙasar Amurka sun kaucewa dukkan taruka masu alaƙa da G20, da Afirka ta Kudu ta karɓi baƙunci. Ban da haka, ganawar da shugaba Trump ya yi da shugaban Afirka ta Kudu Cyril Ramaphosa ma ta riƙide, har ta zama tamkar cacar baka a wani lokaci. Abubuwan da aka yi tababa a kai sun haɗa da zargin da Amurka ɗin ta yi wa Afirka ta Kudu, cewa wai tana yi wa al’ummarta ‘yan asalin Turai “kisan kiyashi”, da yadda Afirka ta Kudu ta kasance mamba a ƙungiyar BRICS, da kuma yadda ƙasar ke ɗora muhimmanci kan batun sauyin yanayi a lokacin da take shugabancin ƙungiyar G20.

LABARAI MASU NASABA

Nijar Da Canada Sun Ƙulla Yarjejeniyar Gina Sabuwar Matatar Mai A Jihar Dosso

Kotun ICC Ta Yi Watsi Da Sabbin Takunkuman Amurka Kan Jami’anta

Ganawar da shugaba Trump ya yi a baya-bayan nan da shugabannin wasu ƙasashe biyar dake nahiyar Afirka, ita ma ta janyo hankalin al’ummun duniya. Inda shugaba Trump ya yabawa shugaban ƙasar Laberiya Joseph Boakai kan yadda ya iya Turancin Ingilishi sosai, lamarin da ya bayyana rashin fahimtarsa kan alaƙar tarihi tsakanin ƙasar Laberiya da Amurka. Bugu da ƙari, Trump ya katse maganar shugaban Ƙasar Mauritaniya Mohammed Ghazouani, inda ya nemi ya yi magana da sauri.

A hakika, rashin mutuntawa da shugaba Trump ya nuna a fili, ta bayyana ainihin dalilin da ya sa aka gayyaci shugabannin Afirka biyar zuwa wajen ganawar, ba domin neman ƙarfafa dangantaka ba ne, sai dai don tabbatar wa Amurka ɗin damar samun ma’adanan da take buƙata, da yiwuwar sanya waɗannan ƙasashen dake nahiyar Afirka amincewa da karɓar baƙin haure da ake korarsu daga Amurka.

Wataƙila, shugaba Trump ba ya mai da hankali sosai kan ɗa’a a fannin diflomasiyya, amma idan aka kwatanta da shugabannin ƙasar Amurka da suka gabace shi, to, a ƙalla yana bayyana komai a fili ba tare da rufa-rufa ba.

Maganarsa da matakan da ya ɗauka, dukkansu na isar da saƙo zuwa ga ƙasashen Afirka cewa: “Ba ku cikin jerin fannonin da Amurka take nunawa fifiko.”

“Za mu iya musayar wasu abubuwa, amma kada ku yi tsammanin za ku samu riba ko alfanu sosai.”

Amurka
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙungiya Ta Gudanar Da Zaɓen Sabbin Shugabanninta A Abuja
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Jihar Katsina Da UNICEF Sun Ceto Rayuwar Yara Ta Hanyar Samar Da Abinci Mai Gina Jiki
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Yadda Tinubu Ya Kashe Naira Biliyan 37.64 A Tafiye-tafiye
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ta’addaci: Mutum 14,500 Sun Bace A Arewa Maso Gabas

MASU ALAKA

Amurka
Kasashen Ketare

Nijar Da Canada Sun Ƙulla Yarjejeniyar Gina Sabuwar Matatar Mai A Jihar Dosso

August 23, 2026
Amurka
Kasashen Ketare

Kotun ICC Ta Yi Watsi Da Sabbin Takunkuman Amurka Kan Jami’anta

August 23, 2026
Amurka
Kasashen Ketare

Rasha Da Ukraine Sun Zafafa Hare-hare Kan Juna Bayan Yaƙinsu Ya Ɗauki Sabon Salo

August 22, 2026
Next Post
Tinubu Ya Gwangwaje Ƴan Wasan Ƙwallon Kwando Ta Mata Da Dala $100,000 Kowace

Jerin Ƴan Wasa Mata Da Suka Samu Kyautar Dala 100,000 Daga Gwamnatin Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

NSCDC Ta Kama Ɓarayin Mota, Ta Ƙwato AK-47 A Abuja

NSCDC Ta Kama Ɓarayin Mota, Ta Ƙwato AK-47 A Abuja

September 15, 2026
Gwamnatin Zamfara Za Ta Mayar Da Yara 453,602 Makaranta

Gwamnatin Zamfara Za Ta Mayar Da Yara 453,602 Makaranta

September 15, 2026
’Yan Ta’adda Sun Kai Wa Ƙauyuka 2 Hari A Adamawa

Boko Haram Sun Kashe Mutane 4 Tare Da Ƙone Gidaje A Adamawa

September 15, 2026
Wani Mutum Ya Kashe Kishiyar Mahaifiyarsa A Kogi

’Yan Ta’adda Na Shirin Kai Hare-Hare Makarantu, Wuraren Ibada Da Sansanonin NYSC – ’Yansanda

September 15, 2026
Gwamnatin Sakkwato Ta Rufe Masallacin Sheikh Lukuwa Bayan Harin Da Aka Kai Masa

Gwamnatin Sakkwato Ta Rufe Masallacin Sheikh Lukuwa Bayan Harin Da Aka Kai Masa

September 15, 2026
Hannun Jari: Dangote Ya Yi Wa ’Yan Nijeriya Alƙawarin Samun Gaggwaɓar Riba

Hannun Jari: Dangote Ya Yi Wa ’Yan Nijeriya Alƙawarin Samun Gaggwaɓar Riba

September 15, 2026
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

Arziƙin Dangote Ya Haura Dala Biliyan 50 Bayan Fara Sayar Da Hannun Jarin Matatarsa – Forbes

September 15, 2026
Jawabin Xi A Taron BRICS, Mafita Ce Ga Matsalolin Duniya

Jawabin Xi A Taron BRICS, Mafita Ce Ga Matsalolin Duniya

September 14, 2026
Duk Wani Yunkuri Na Karfafa Burin Japan Na Fadada Karfin Soji Zai Jefa Yankin Cikin Hadari

Duk Wani Yunkuri Na Karfafa Burin Japan Na Fadada Karfin Soji Zai Jefa Yankin Cikin Hadari

September 14, 2026
Tsohon Firaminsitan Jordan: Kasar Sin Tana Kan Gaba Wajen Gudanar Da Fasahar AI A Duniya

Tsohon Firaminsitan Jordan: Kasar Sin Tana Kan Gaba Wajen Gudanar Da Fasahar AI A Duniya

September 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.