• English
  • Business News
Wednesday, August 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dole Ne Afrika Ta Mayar Da Hankali Wajen Amfana Da Damarmakin Da Ke Tekunanta – Ɗantsoho

by Bello Hamza
3 days ago
in Labarai
0
Dole Ne Afrika Ta Mayar Da Hankali Wajen Amfana Da Damarmakin Da Ke Tekunanta – Ɗantsoho
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban Ƙungiyar Kula da Tashoshin Jiragen Ruwa ta Gabas da yankin Afirka ta Tsakiya PMAWCA, Dakta Abubakar Ɗantsoho, ya bayyana cewa, dole ne Afirka ta mayar da hankali wajen amfana da damarmakin da ke Tekunanta, domin ƙara bunƙasa tattalin arzikinta.

Ɗantsoho, wanda kuma shi ne, Shugaban Hukumar Hukumar kula da Tashoshin Jiragen Ruwa ta Ƙasa NPA, ya sanar da hakan ne,a jawabinsa a taron Daraktoci da ƙwararrun masu kula da kafar sanada zumunta ta zamani na ƙungiyar ta PMAWCA da ya gudana a yankin Luanda, na ƙasar Angola.

  • Mamakon Ruwan Sama A Wasu Jihohi Na Barazana Ga Harkokin Yau Da Kullum
  • Remi Tinubu Ta Bada Gudunmawar Naira Biliyan 1 Ga Wadanda Ambaliyar Ruwan Neja Ta Shafa

Shugaban ya ce, Afirka ita ce, kan gaba wajen kula da Tekunan Ruwa, inda ya ƙara da cewa, sauran ƙasashen da ke Afirka ta Gabas da kuma waɗanda ke a Afirka ta Tsakiya, ba wai kawai suna kula ta Tekunnansu bane, har da ma musharaka da sauran irin ƙalubalen da suke fuskanta da sauran damarmakin da suke amfana da su.

“Yanzu ne, lokacin da ya dace, ake da matuƙar buƙatar mu amfana da sauran damarmakin da ake da sun a Tekuna, “ Inji Ɗantsoho.

“ Dole bai kamata ace, mun fitar da rai ba, wajen una irin ƙarfin iya shugabancin da muke da shi, na shugabantar Tashoshin Jiragen Ruwa, musaman domin ɗorewar muradun ƙarni wato SDGs, domin ci gaba da ɗorewar duniya, musamman Afrika, ta hanyar ci gaba da bai wa Tashohin Ruwan kulawarda ta dace, “ Acewar Shugaban.

Labarai Masu Nasaba

‘Yansanda Sun Fara Bincike Kan Rasuwar Wani Dan NYSC A Bauchi

EFCC Ta Bayar Da Belin Tambuwal, Ta Yi Allah-wadai Da Zargin Da Jam’iyar ADC Ta Yi

“Baya ga alaƙa da Ruwa, ƙasashen da ke Afirka ta Gabas da kuma waɗanda ke a Afrika ta Tsakiya, da suke yi musharaka da irin ƙalubalensu da kuma sauran damarmakinsu, dole ne mu zage mu amfana da tattalin arzikin da ake da shin a Tekuna, musamman ta hanyar haɗa kanmu da kuma yin haɗaka, wanda idan ba a yi hakan ba, tamkar muna kawai yaudarar kawunan mu ne,” Ɗantso ya ce.

A cewar Shugaban na Hukumar NPA, alƙaluman da ake da su, sune za su bamu damar, ci gaba da ɗaukar matakan da suka kamata, na wajen ci gaba da bai wa Tashoshin Jiragen Ruwa na Afrika, kulawar da ta dace.

Kazalika, Shugaban ya kuma jinkinawa shugaban ƙasa Bola Tinubu, kan ƙirƙiro da Ma’aikatar Kula da Tattalin Arziki na Teku, inda ya sanar da cewa, hakan ya samar wa da Hukumar ta NPA sauƙi wajen samar da inagantattun sauye-sauyen a fannin na tafiyar da Tashoshin Jiragen Ruwan ƙasar.

“Gwamnatin mai girma Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu bisa ƙirƙiro da Ma’aikatar Kula da Tattalin Arziki na Teku, hakan ya samar wa da Hukumar mu ta NPA samun sauƙin samar da ingantattun sauye-sauye, a fannin na tafiyar da Tashoshin Jiragen Ruwan Ƙasar nan, inda kuma ta hanyar Ma’aikatar, a ƙara samar da ɗimbin masu zuba hannun jari a fannin tare da kuma amfana da basira ƙwararrun da ke a ƙungiyar ta PMAWCA,” Inji Shugaban.

Ɗantsoho ya ci gaba da cewa, ƙwararrun da ke kula da kafar sadarwar, suma suna ci gaba da taimaka wa wajen ƙara samar da horo domin a amfana da damarmakin da ke a Tashoshin na Jiragen Ruwan, musamman ta hanyar amfani da tsarukan PCS NSW.

Shugaban na Hukumar ta NPA ya ƙara da cewa, dole ne, a ci gaba da yin ƙoƙarin da ake gudanarwa kafaɗa da kafaɗa, ta hanyar haɗa kai da sauran ‘ya’yan ƙungiyar ta PMAWCA.

“Manufofin yarjejeniyar kasuwanci marar shinge ta Afrika wato AfCFTA, sun haɗa da kawar da haraji da kuma duk wani harajin da ke sanya wa, na gudanar da hada-hadar kasuwanci, wanda hakan zai kuma ƙara samar da sauran damarmaki a fannnin da kuma ƙara samun ɗaukaka fannin,” Inji Ɗantsoho.

Ɗantsoho ya ƙara da cewa, a taron da Dakaratocin na ƙungiyar ta PMAWCA suka gudanar, sun yi nazari kan samakon ayyukan da ƙungiyar ta gudanar shekarar 2024 tare da kuma auna shawarwarin da mahalarta taron suka bayar, a lokcin taron, inda suke tsara matakan da za su ɗauka nag aba, domin ƙungiyar, ta ƙara samun ci gaba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: GaɓaRuwa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Jihar Kogi Ta Kafa Kotuna 9 Don Hukunta Masu Cin Zarafin Mata

Next Post

An Maka Gwamnatin Neja Da NBC A Kotu Kan Barazanar Rufe Gidan Rediyon Badeggi FM

Related

Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa
Labarai

‘Yansanda Sun Fara Bincike Kan Rasuwar Wani Dan NYSC A Bauchi

3 hours ago
EFCC Ta Bayar Da Belin Tambuwal, Ta Yi Allah-wadai Da Zargin Da Jam’iyar ADC Ta Yi
Labarai

EFCC Ta Bayar Da Belin Tambuwal, Ta Yi Allah-wadai Da Zargin Da Jam’iyar ADC Ta Yi

4 hours ago
Babu Neman Afuwa Kan Nuna Goyan Bayan Tinubu Da Na Yi – Soludo
Labarai

Babu Neman Afuwa Kan Nuna Goyan Bayan Tinubu Da Na Yi – Soludo

4 hours ago
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Masallaci Sun Kashe Wani Mutum Da Jikkata Wasu Da Dama A Sokoto

5 hours ago
Gwamnatin Kano Za Ta Horar Da Tubabbun ‘Yandaba 718 Sana’o’i 
Labarai

Gwamnatin Kano Za Ta Horar Da Tubabbun ‘Yandaba 718 Sana’o’i 

6 hours ago
Jiragen saman NAF Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 592, Sun Lalata Kayayyakin Yaki 372
Labarai

Jiragen saman NAF Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 592, Sun Lalata Kayayyakin Yaki 372

7 hours ago
Next Post
ADC Ta Yi Allah-wadai Da Rufe Gidan Rediyon Badeggi FM A Neja

An Maka Gwamnatin Neja Da NBC A Kotu Kan Barazanar Rufe Gidan Rediyon Badeggi FM

LABARAI MASU NASABA

Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

‘Yansanda Sun Fara Bincike Kan Rasuwar Wani Dan NYSC A Bauchi

August 12, 2025
Sin Na Goyon Bayan Duk Wani Mataki Na Warware Batun Ukraine Ta Hanyar Lumana

Sin Na Goyon Bayan Duk Wani Mataki Na Warware Batun Ukraine Ta Hanyar Lumana

August 12, 2025
EFCC Ta Bayar Da Belin Tambuwal, Ta Yi Allah-wadai Da Zargin Da Jam’iyar ADC Ta Yi

EFCC Ta Bayar Da Belin Tambuwal, Ta Yi Allah-wadai Da Zargin Da Jam’iyar ADC Ta Yi

August 12, 2025
Babu Neman Afuwa Kan Nuna Goyan Bayan Tinubu Da Na Yi – Soludo

Babu Neman Afuwa Kan Nuna Goyan Bayan Tinubu Da Na Yi – Soludo

August 12, 2025
Ilimin Fasahar Zamani Dama Ce Ta Samun Kyakkyawar Makoma A Afrika

Ilimin Fasahar Zamani Dama Ce Ta Samun Kyakkyawar Makoma A Afrika

August 12, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Masallaci Sun Kashe Wani Mutum Da Jikkata Wasu Da Dama A Sokoto

August 12, 2025
Sin Ta Ware Yuan Miliyan 170 Domin Ayyukan Tallafi Ga Sassan Da Ambaliyar Ruwa Ta Shafa

Sin Ta Ware Yuan Miliyan 170 Domin Ayyukan Tallafi Ga Sassan Da Ambaliyar Ruwa Ta Shafa

August 12, 2025
Gwamnatin Kano Za Ta Horar Da Tubabbun ‘Yandaba 718 Sana’o’i 

Gwamnatin Kano Za Ta Horar Da Tubabbun ‘Yandaba 718 Sana’o’i 

August 12, 2025
Xi: Sin Da Brazil Na Iya Zama Misalin Hadin Kai Da Dogaro Da Kai Ga Kasashe Masu Tasowa

Xi: Sin Da Brazil Na Iya Zama Misalin Hadin Kai Da Dogaro Da Kai Ga Kasashe Masu Tasowa

August 12, 2025
Jiragen saman NAF Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 592, Sun Lalata Kayayyakin Yaki 372

Jiragen saman NAF Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 592, Sun Lalata Kayayyakin Yaki 372

August 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.