ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 20, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dole Ne Afrika Ta Mayar Da Hankali Wajen Amfana Da Damarmakin Da Ke Tekunanta – Ɗantsoho

by Bello Hamza
10 months ago
Afrika

Shugaban Ƙungiyar Kula da Tashoshin Jiragen Ruwa ta Gabas da yankin Afirka ta Tsakiya PMAWCA, Dakta Abubakar Ɗantsoho, ya bayyana cewa, dole ne Afirka ta mayar da hankali wajen amfana da damarmakin da ke Tekunanta, domin ƙara bunƙasa tattalin arzikinta.

Ɗantsoho, wanda kuma shi ne, Shugaban Hukumar Hukumar kula da Tashoshin Jiragen Ruwa ta Ƙasa NPA, ya sanar da hakan ne,a jawabinsa a taron Daraktoci da ƙwararrun masu kula da kafar sanada zumunta ta zamani na ƙungiyar ta PMAWCA da ya gudana a yankin Luanda, na ƙasar Angola.

  • Mamakon Ruwan Sama A Wasu Jihohi Na Barazana Ga Harkokin Yau Da Kullum
  • Remi Tinubu Ta Bada Gudunmawar Naira Biliyan 1 Ga Wadanda Ambaliyar Ruwan Neja Ta Shafa

Shugaban ya ce, Afirka ita ce, kan gaba wajen kula da Tekunan Ruwa, inda ya ƙara da cewa, sauran ƙasashen da ke Afirka ta Gabas da kuma waɗanda ke a Afirka ta Tsakiya, ba wai kawai suna kula ta Tekunnansu bane, har da ma musharaka da sauran irin ƙalubalen da suke fuskanta da sauran damarmakin da suke amfana da su.

ADVERTISEMENT

“Yanzu ne, lokacin da ya dace, ake da matuƙar buƙatar mu amfana da sauran damarmakin da ake da sun a Tekuna, “ Inji Ɗantsoho.

“ Dole bai kamata ace, mun fitar da rai ba, wajen una irin ƙarfin iya shugabancin da muke da shi, na shugabantar Tashoshin Jiragen Ruwa, musaman domin ɗorewar muradun ƙarni wato SDGs, domin ci gaba da ɗorewar duniya, musamman Afrika, ta hanyar ci gaba da bai wa Tashohin Ruwan kulawarda ta dace, “ Acewar Shugaban.

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu

Hijira 1448:Za A Samu Yalwar Tattalin Arziƙi A Nijeriya —Sheikh Muhajjadina

“Baya ga alaƙa da Ruwa, ƙasashen da ke Afirka ta Gabas da kuma waɗanda ke a Afrika ta Tsakiya, da suke yi musharaka da irin ƙalubalensu da kuma sauran damarmakinsu, dole ne mu zage mu amfana da tattalin arzikin da ake da shin a Tekuna, musamman ta hanyar haɗa kanmu da kuma yin haɗaka, wanda idan ba a yi hakan ba, tamkar muna kawai yaudarar kawunan mu ne,” Ɗantso ya ce.

A cewar Shugaban na Hukumar NPA, alƙaluman da ake da su, sune za su bamu damar, ci gaba da ɗaukar matakan da suka kamata, na wajen ci gaba da bai wa Tashoshin Jiragen Ruwa na Afrika, kulawar da ta dace.

Kazalika, Shugaban ya kuma jinkinawa shugaban ƙasa Bola Tinubu, kan ƙirƙiro da Ma’aikatar Kula da Tattalin Arziki na Teku, inda ya sanar da cewa, hakan ya samar wa da Hukumar ta NPA sauƙi wajen samar da inagantattun sauye-sauyen a fannin na tafiyar da Tashoshin Jiragen Ruwan ƙasar.

“Gwamnatin mai girma Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu bisa ƙirƙiro da Ma’aikatar Kula da Tattalin Arziki na Teku, hakan ya samar wa da Hukumar mu ta NPA samun sauƙin samar da ingantattun sauye-sauye, a fannin na tafiyar da Tashoshin Jiragen Ruwan Ƙasar nan, inda kuma ta hanyar Ma’aikatar, a ƙara samar da ɗimbin masu zuba hannun jari a fannin tare da kuma amfana da basira ƙwararrun da ke a ƙungiyar ta PMAWCA,” Inji Shugaban.

Ɗantsoho ya ci gaba da cewa, ƙwararrun da ke kula da kafar sadarwar, suma suna ci gaba da taimaka wa wajen ƙara samar da horo domin a amfana da damarmakin da ke a Tashoshin na Jiragen Ruwan, musamman ta hanyar amfani da tsarukan PCS NSW.

Shugaban na Hukumar ta NPA ya ƙara da cewa, dole ne, a ci gaba da yin ƙoƙarin da ake gudanarwa kafaɗa da kafaɗa, ta hanyar haɗa kai da sauran ‘ya’yan ƙungiyar ta PMAWCA.

“Manufofin yarjejeniyar kasuwanci marar shinge ta Afrika wato AfCFTA, sun haɗa da kawar da haraji da kuma duk wani harajin da ke sanya wa, na gudanar da hada-hadar kasuwanci, wanda hakan zai kuma ƙara samar da sauran damarmaki a fannnin da kuma ƙara samun ɗaukaka fannin,” Inji Ɗantsoho.

Ɗantsoho ya ƙara da cewa, a taron da Dakaratocin na ƙungiyar ta PMAWCA suka gudanar, sun yi nazari kan samakon ayyukan da ƙungiyar ta gudanar shekarar 2024 tare da kuma auna shawarwarin da mahalarta taron suka bayar, a lokcin taron, inda suke tsara matakan da za su ɗauka nag aba, domin ƙungiyar, ta ƙara samun ci gaba.

Afrika
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Hijira 1448:Za A Samu Yalwar Tattalin Arziƙi A Nijeriya —Sheikh Muhajjadina
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Amfani Da Matar Soja Wajen Isar Da Sakon Bukata

MASU ALAKA

Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
Labarai

Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu

June 20, 2026
Hijira 1448:Za A Samu Yalwar Tattalin Arziƙi A Nijeriya —Sheikh Muhajjadina
Labarai

Hijira 1448:Za A Samu Yalwar Tattalin Arziƙi A Nijeriya —Sheikh Muhajjadina

June 20, 2026
2027:Yadda Kuɗi Da Siyasar Uban-gida Suka Daƙile Hanƙoron Matasa
Rahotonni

2027:Yadda Kuɗi Da Siyasar Uban-gida Suka Daƙile Hanƙoron Matasa

June 20, 2026
Next Post
ADC Ta Yi Allah-wadai Da Rufe Gidan Rediyon Badeggi FM A Neja

An Maka Gwamnatin Neja Da NBC A Kotu Kan Barazanar Rufe Gidan Rediyon Badeggi FM

LABARAI MASU NASABA

Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya

Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya

June 20, 2026
Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu

Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu

June 20, 2026
Hijira 1448:Za A Samu Yalwar Tattalin Arziƙi A Nijeriya —Sheikh Muhajjadina

Hijira 1448:Za A Samu Yalwar Tattalin Arziƙi A Nijeriya —Sheikh Muhajjadina

June 20, 2026
Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

June 20, 2026
Turkiyya Ta Zama Ƙasa Ta Biyu Da Ta Fice Daga Gasar Kofin Duniya

Turkiyya Ta Zama Ƙasa Ta Biyu Da Ta Fice Daga Gasar Kofin Duniya

June 20, 2026
2027:Yadda Kuɗi Da Siyasar Uban-gida Suka Daƙile Hanƙoron Matasa

2027:Yadda Kuɗi Da Siyasar Uban-gida Suka Daƙile Hanƙoron Matasa

June 20, 2026
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho

NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho

June 20, 2026
Kungiyar Manoman Citta Ta Kasa Ta Yaba Wa Gwamnatin Tarayya Kan Tallafin Da Take Ba Su

Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

June 19, 2026
Abinci

Yadda Gwamnatin Kano Ta Samu Nasarar Kashi 80 A Fannin Aikin Noma

June 19, 2026
Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa

Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa

June 19, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.