ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 11, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dole Ne Afrika Ta Mayar Da Hankali Wajen Amfana Da Damarmakin Da Ke Tekunanta – Ɗantsoho

by Bello Hamza
11 months ago
Afrika

Shugaban Ƙungiyar Kula da Tashoshin Jiragen Ruwa ta Gabas da yankin Afirka ta Tsakiya PMAWCA, Dakta Abubakar Ɗantsoho, ya bayyana cewa, dole ne Afirka ta mayar da hankali wajen amfana da damarmakin da ke Tekunanta, domin ƙara bunƙasa tattalin arzikinta.

Ɗantsoho, wanda kuma shi ne, Shugaban Hukumar Hukumar kula da Tashoshin Jiragen Ruwa ta Ƙasa NPA, ya sanar da hakan ne,a jawabinsa a taron Daraktoci da ƙwararrun masu kula da kafar sanada zumunta ta zamani na ƙungiyar ta PMAWCA da ya gudana a yankin Luanda, na ƙasar Angola.

  • Mamakon Ruwan Sama A Wasu Jihohi Na Barazana Ga Harkokin Yau Da Kullum
  • Remi Tinubu Ta Bada Gudunmawar Naira Biliyan 1 Ga Wadanda Ambaliyar Ruwan Neja Ta Shafa

Shugaban ya ce, Afirka ita ce, kan gaba wajen kula da Tekunan Ruwa, inda ya ƙara da cewa, sauran ƙasashen da ke Afirka ta Gabas da kuma waɗanda ke a Afirka ta Tsakiya, ba wai kawai suna kula ta Tekunnansu bane, har da ma musharaka da sauran irin ƙalubalen da suke fuskanta da sauran damarmakin da suke amfana da su.

ADVERTISEMENT

“Yanzu ne, lokacin da ya dace, ake da matuƙar buƙatar mu amfana da sauran damarmakin da ake da sun a Tekuna, “ Inji Ɗantsoho.

“ Dole bai kamata ace, mun fitar da rai ba, wajen una irin ƙarfin iya shugabancin da muke da shi, na shugabantar Tashoshin Jiragen Ruwa, musaman domin ɗorewar muradun ƙarni wato SDGs, domin ci gaba da ɗorewar duniya, musamman Afrika, ta hanyar ci gaba da bai wa Tashohin Ruwan kulawarda ta dace, “ Acewar Shugaban.

LABARAI MASU NASABA

NDLEA Ta Cafke Ƴar Shekara 67 Da Hodar Iblis Da Aka Ɓoye A Cikin Ayaba

Duk Da Faɗuwar Farashin Ɗanyen Mai Ƴan Nijeriya Na Fama Da Tsadar Man Fetur

“Baya ga alaƙa da Ruwa, ƙasashen da ke Afirka ta Gabas da kuma waɗanda ke a Afrika ta Tsakiya, da suke yi musharaka da irin ƙalubalensu da kuma sauran damarmakinsu, dole ne mu zage mu amfana da tattalin arzikin da ake da shin a Tekuna, musamman ta hanyar haɗa kanmu da kuma yin haɗaka, wanda idan ba a yi hakan ba, tamkar muna kawai yaudarar kawunan mu ne,” Ɗantso ya ce.

A cewar Shugaban na Hukumar NPA, alƙaluman da ake da su, sune za su bamu damar, ci gaba da ɗaukar matakan da suka kamata, na wajen ci gaba da bai wa Tashoshin Jiragen Ruwa na Afrika, kulawar da ta dace.

Kazalika, Shugaban ya kuma jinkinawa shugaban ƙasa Bola Tinubu, kan ƙirƙiro da Ma’aikatar Kula da Tattalin Arziki na Teku, inda ya sanar da cewa, hakan ya samar wa da Hukumar ta NPA sauƙi wajen samar da inagantattun sauye-sauyen a fannin na tafiyar da Tashoshin Jiragen Ruwan ƙasar.

“Gwamnatin mai girma Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu bisa ƙirƙiro da Ma’aikatar Kula da Tattalin Arziki na Teku, hakan ya samar wa da Hukumar mu ta NPA samun sauƙin samar da ingantattun sauye-sauye, a fannin na tafiyar da Tashoshin Jiragen Ruwan Ƙasar nan, inda kuma ta hanyar Ma’aikatar, a ƙara samar da ɗimbin masu zuba hannun jari a fannin tare da kuma amfana da basira ƙwararrun da ke a ƙungiyar ta PMAWCA,” Inji Shugaban.

Ɗantsoho ya ci gaba da cewa, ƙwararrun da ke kula da kafar sadarwar, suma suna ci gaba da taimaka wa wajen ƙara samar da horo domin a amfana da damarmakin da ke a Tashoshin na Jiragen Ruwan, musamman ta hanyar amfani da tsarukan PCS NSW.

Shugaban na Hukumar ta NPA ya ƙara da cewa, dole ne, a ci gaba da yin ƙoƙarin da ake gudanarwa kafaɗa da kafaɗa, ta hanyar haɗa kai da sauran ‘ya’yan ƙungiyar ta PMAWCA.

“Manufofin yarjejeniyar kasuwanci marar shinge ta Afrika wato AfCFTA, sun haɗa da kawar da haraji da kuma duk wani harajin da ke sanya wa, na gudanar da hada-hadar kasuwanci, wanda hakan zai kuma ƙara samar da sauran damarmaki a fannnin da kuma ƙara samun ɗaukaka fannin,” Inji Ɗantsoho.

Ɗantsoho ya ƙara da cewa, a taron da Dakaratocin na ƙungiyar ta PMAWCA suka gudanar, sun yi nazari kan samakon ayyukan da ƙungiyar ta gudanar shekarar 2024 tare da kuma auna shawarwarin da mahalarta taron suka bayar, a lokcin taron, inda suke tsara matakan da za su ɗauka nag aba, domin ƙungiyar, ta ƙara samun ci gaba.

Afrika
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Shugaban Miyetti Allah, Bodejo Ya Karyata Zargin Halatta Kudin Haram A Zaman Kotu
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Kafa Cibiyar NIPHID: NCDC Ta Yi Kuskuren Fahimtar Ƙudirin Dokar
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Uwargidan Shugaban Ƙasa Ta Ƙaddamar Da Muhimman Ayyukan Ci Gaba A Jihar Jigawa
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Ƙungiyar Kansilolin APC Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Idan Ba A Daina Zargin Sanata Yari Ba

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Tsaro

NDLEA Ta Cafke Ƴar Shekara 67 Da Hodar Iblis Da Aka Ɓoye A Cikin Ayaba

July 11, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Manyan Labarai

Duk Da Faɗuwar Farashin Ɗanyen Mai Ƴan Nijeriya Na Fama Da Tsadar Man Fetur

July 11, 2026
2027: Tinubu Ya Sake Zaɓar Shettima A Matsayin Abokin Takararsa
Da ɗumi-ɗuminsa

2027: Tinubu Ya Sake Zaɓar Shettima A Matsayin Abokin Takararsa

July 10, 2026
Next Post
ADC Ta Yi Allah-wadai Da Rufe Gidan Rediyon Badeggi FM A Neja

An Maka Gwamnatin Neja Da NBC A Kotu Kan Barazanar Rufe Gidan Rediyon Badeggi FM

LABARAI MASU NASABA

Ronaldo Da Ƴanwasan Da Suka Buga Kofin Duniya Na Ƙarshe A Rayuwarsu

July 11, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

NDLEA Ta Cafke Ƴar Shekara 67 Da Hodar Iblis Da Aka Ɓoye A Cikin Ayaba

July 11, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar

July 11, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Duk Da Faɗuwar Farashin Ɗanyen Mai Ƴan Nijeriya Na Fama Da Tsadar Man Fetur

July 11, 2026
Kasar Sin Ta Fitar Da Shirin Kai Wa Matakin Koli Na Fitar Da Hayakin Carbon

Kasar Sin Ta Fitar Da Shirin Kai Wa Matakin Koli Na Fitar Da Hayakin Carbon

July 10, 2026
Sin Ta Yi Nasarar Dawo Da Rokar Da Ake Sarrafa Dawowarta A Tashin Farko Na Samfurin Long March-10B

Sin Ta Yi Nasarar Dawo Da Rokar Da Ake Sarrafa Dawowarta A Tashin Farko Na Samfurin Long March-10B

July 10, 2026
CMG Ya Gabatar Da Shiri Na Musamman Mai Taken “Samun Nasara Dangane Da AI+” A Ketare

CMG Ya Gabatar Da Shiri Na Musamman Mai Taken “Samun Nasara Dangane Da AI+” A Ketare

July 10, 2026
Zargin Da Wasu Sassa Ke Yiwa Kasar Sin Na Takure Sauran Kasashe Masu Tasowa Ba Shi da Tushe Ko Makama

Zargin Da Wasu Sassa Ke Yiwa Kasar Sin Na Takure Sauran Kasashe Masu Tasowa Ba Shi da Tushe Ko Makama

July 10, 2026
2027: Tinubu Ya Sake Zaɓar Shettima A Matsayin Abokin Takararsa

2027: Tinubu Ya Sake Zaɓar Shettima A Matsayin Abokin Takararsa

July 10, 2026
Taron Kara Wa Juna Sani Na Duniya Ya Yi Nazari Kan Kwarewar Kasar Sin Wajen Rage Talauci

Taron Kara Wa Juna Sani Na Duniya Ya Yi Nazari Kan Kwarewar Kasar Sin Wajen Rage Talauci

July 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.