• English
  • Business News
Thursday, August 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasashen Sahel Na Bukatar Agaji Domin Yaki Ta’addanci -Rasha

by Rabi'u Ali Indabawa
4 days ago
in Labarai
0
Kasashen Sahel Na Bukatar Agaji Domin Yaki Ta’addanci -Rasha
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rasha ta yi kira ga kasashen duniya su hada karfi da karfe wajen taimakon hadakar kasashen Alliance of Sahel States wato AES domin ba su taimakon da suke bukata a yakin da suke yi da matsalar tsaro.

Kasashen AES din su ne Mali da Burkina Faso da kuma Nijar wadanda suke karkashin mulkin soja bayan shugabannin mulkin kasashen sun hambarar da gwamnatin fararen hula.

  • Hadin Tuwon Dawa
  • Hanyoyi Goma Sha Daya Da Mace Za Ta Bi Domin Janyo Hankalin Mijinta

Kafar Actualite.bf mai zaman kanta ne ta ruwaito cewa Rasha ta gabatar da wannan kokon baran ne a jawabinta ga kwamitin tsaro na Majalisar Dinkin Duniya, inda wakilinta na dindindin, Dmitry Chumakob ya ce kasashen na bukatar agajin tsaro.

“Domin samun dawwamammen zaman lafiya, ya kamata kasashen duniya su ba kasashen Mali da Burkina Fasp da Nijar gudunmuwa,” in ji Chumakob.

Ya kara da cewa, “kasashen Afirka din ne da kansu suka fi sanin yadda za su magance matsalolin da suke fuskanta, kuma su ne suka fi sanin yadda za su yi yaki da matsalar tsaro da kuma hanyoyin inganta dimokuradiyya da tattalin arzikinsu.”

Labarai Masu Nasaba

Nijeriya Ta Kori Ƙarin ‘Yan Ƙasashen Waje 51 Da Aka Ɗaure Bisa Laifin Ta’addanci Da Zamba A Intanet

Mafi Ƙarancin Albashin ₦70,000 Ba Zai Iya Tsamo ‘Yan Nijeriya Daga Ƙangin Talauci Ba – Amurka

Rasha dai ta zama babbar kawar kasashen na AES, wadanda ke jan jikinsu daga wasu kasashen na yamma, inda Moscow ta kuduri aniyar taimakon kasashen wajen yaki da masu tayar da kayar baya.

 

Nijer Ta Ceto ‘Yan Gudun Hijira Da Suka Makale A Libya

Sojojin Jamhuriyar Nijar sun samu nasarar ceto ‘yancirani guda 50 da suke makala a sahara a hanyarsu ta tafiya kasar Libya.

RFI ta ruwaito cewa mutanen sun makale ne a kusa da bakin iyakar shiga kasar ta Libya bayan motarsu ta lalace a ranar 10 ga watan Agusta.

“Motarsu ta lalace ne a hanyarsu ta tafiya Libya, kasar da ake ratsawa domin tafiya kasashen turai. A ciki akwai fasinjoji 44 kuma motar tana tafiya ne a hanyar Madama-Dao da ke arewacin Nijar a lokacin da ta lalace, ta tsaya cak,” in ji rahoton na RFI.

Daga baya ne aka shiga neman motar, inda sojojin suka samu nasarar ceto su, sannan aka kai su garin Madama, inda ake cigaba da kula da su.

Sai dai har yanzu ba a tabbatar da asalin kasashen da mutanen suka fito ba, da kuma asalin kasar da suke shirin zuwa.

 

M23 Ta Musanta Zargin Kashe Gomman Fararen Hula A Kudancin Kibu

Kungiyar ‘yantawaye ta M23 a Congo ta musanta zarginta da ake yi da kashe gomman fararen hula a Kudancin Kibu na kasar, sannan kuma ta nanata cewa zarginta da ake yi da amfani da kananan yara a yaki kanzon kurege ne.

Kakakin M23, Willy Ngoma ne ya bayyana wa BBC haka, inda ya ce ko kadan ba ya cikin tsarinsu kai farmaki kan fararen hula.

“Ba ma kashe fararen hula. Ta yaya za mu kashe ‘yankasa, wadanda muke fafutikar karewa?


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Rasha
ShareTweetSendShare
Previous Post

Tattakin Arba’in: Muna Farin Ciki Da Yadda Gwamnati Ta Fahimci Ayyukan Mu Na Addini – Ahlul-Baiti

Next Post

UNICEF Ya Jaddada Muhimmancin Yi Wa Yaran Afirka Rajistar Haihuwa

Related

Nijeriya Ta Kori Ƙarin ‘Yan Ƙasashen Waje 51 Da Aka Ɗaure Bisa Laifin Ta’addanci Da Zamba A Intanet
Labarai

Nijeriya Ta Kori Ƙarin ‘Yan Ƙasashen Waje 51 Da Aka Ɗaure Bisa Laifin Ta’addanci Da Zamba A Intanet

2 hours ago
Mafi Ƙarancin Albashin ₦70,000 Ba Zai Iya Tsamo ‘Yan Nijeriya Daga Ƙangin Talauci Ba – Amurka
Manyan Labarai

Mafi Ƙarancin Albashin ₦70,000 Ba Zai Iya Tsamo ‘Yan Nijeriya Daga Ƙangin Talauci Ba – Amurka

3 hours ago
Sarkin Musulmi Ya Taya Ladoja Murnar Zama Sabon Sarkin Ƙasar Ibadan 
Manyan Labarai

Sarkin Musulmi Ya Taya Ladoja Murnar Zama Sabon Sarkin Ƙasar Ibadan 

7 hours ago
Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci Cibiyoyin Bayar Da Lamuni Kan Tabbatar Da Gaskiya Da Adalci
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci Cibiyoyin Bayar Da Lamuni Kan Tabbatar Da Gaskiya Da Adalci

19 hours ago
Rajistar Katin Zaɓe: Gwamnatin Kano Za Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Wayar Da Kan Jama’a 
Labarai

Rajistar Katin Zaɓe: Gwamnatin Kano Za Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Wayar Da Kan Jama’a 

20 hours ago
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa
Labarai

Hukumar ‘Yansanda Ta Yi Watsi Ga Ƙarin Girma Ga ASP 179, Ta Ɗaga Darajar 952 Zuwa DSP

22 hours ago
Next Post
UNICEF Ya Jaddada Muhimmancin Yi Wa Yaran Afirka Rajistar Haihuwa

UNICEF Ya Jaddada Muhimmancin Yi Wa Yaran Afirka Rajistar Haihuwa

LABARAI MASU NASABA

Nijeriya Ta Kori Ƙarin ‘Yan Ƙasashen Waje 51 Da Aka Ɗaure Bisa Laifin Ta’addanci Da Zamba A Intanet

Nijeriya Ta Kori Ƙarin ‘Yan Ƙasashen Waje 51 Da Aka Ɗaure Bisa Laifin Ta’addanci Da Zamba A Intanet

August 21, 2025
Mafi Ƙarancin Albashin ₦70,000 Ba Zai Iya Tsamo ‘Yan Nijeriya Daga Ƙangin Talauci Ba – Amurka

Mafi Ƙarancin Albashin ₦70,000 Ba Zai Iya Tsamo ‘Yan Nijeriya Daga Ƙangin Talauci Ba – Amurka

August 21, 2025
Sarkin Musulmi Ya Taya Ladoja Murnar Zama Sabon Sarkin Ƙasar Ibadan 

Sarkin Musulmi Ya Taya Ladoja Murnar Zama Sabon Sarkin Ƙasar Ibadan 

August 21, 2025
Boniface

Ac Milan Na Tattaunawa Da Bayern Leverkusen Akan Yunkurin Daukar Boniface

August 20, 2025
Xi Jinping Zai Duba Faretin Sojoji Ta Kan Titin Chang’an A Ranar Uku Ga Watan Satumba Dake Tafe

Xi Jinping Zai Duba Faretin Sojoji Ta Kan Titin Chang’an A Ranar Uku Ga Watan Satumba Dake Tafe

August 20, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci Cibiyoyin Bayar Da Lamuni Kan Tabbatar Da Gaskiya Da Adalci

Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci Cibiyoyin Bayar Da Lamuni Kan Tabbatar Da Gaskiya Da Adalci

August 20, 2025
Faretin Sojoji Da Sin Za Ta Gudanar Zai Shaida Muhimmancin Zaman Lafiya Da Goyon Bayan Gaskiya Da Adalci Tsakanin Kasa Da Kasa

Faretin Sojoji Da Sin Za Ta Gudanar Zai Shaida Muhimmancin Zaman Lafiya Da Goyon Bayan Gaskiya Da Adalci Tsakanin Kasa Da Kasa

August 20, 2025
Kasar Sin Za Ta Gabatar Da Sabbin Makamai Yayin Faretin Soja Na Ranar 3 Ga Watan Satumba

Kasar Sin Za Ta Gabatar Da Sabbin Makamai Yayin Faretin Soja Na Ranar 3 Ga Watan Satumba

August 20, 2025
Rajistar Katin Zaɓe: Gwamnatin Kano Za Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Wayar Da Kan Jama’a 

Rajistar Katin Zaɓe: Gwamnatin Kano Za Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Wayar Da Kan Jama’a 

August 20, 2025
Xizang A Shekaru 60 Da Kafuwa: Daga Mawuyacin Hali Zuwa Farin Wata Sha Kallo

Xizang A Shekaru 60 Da Kafuwa: Daga Mawuyacin Hali Zuwa Farin Wata Sha Kallo

August 20, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.