Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) ta bayyana dan takarar jam’iyyar APC, Matthew Dogara Daje a matsayin wanda ya lashe zaben cike gurbi da aka gudanar a mazaɓar Munya ranar Asabar.
Daje ya samu kuri’u 12,556 inda ya kayar da abokin hamayyarsa Sabo Sunday Adabyinlo na jam’iyyar PDP wanda ya samu kuri’u 5,646.
Sakamakon da INEC ta fitar, APC ta samu nasara a unguwanni 10 yayin da jam’iyyar adawa ta PDP ta samu nasara a unguwa daya.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp