• English
  • Business News
Tuesday, October 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Babban Titin ‘Trans-Sahara’ Zai Ƙarfafa Haɗin Gwiwa Da Ƙarin Damar Tattalin Arziki – Minista

by Sulaiman
2 months ago
Trans-sahara

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya ce an tsara babban titin ‘Trans-Sahara’ ne domin ƙarfafa haɗin gwiwar yankuna da buɗe damarmakin tattalin arziki.

 

Idris ya bayyana hakan ne a ranar Juma’a yayin da ya jagoranci tawagar Gwamnatin Tarayya wajen duba aikin wanda ake ci gaba da yi mai tsawon kilomita 118 da ya tashi daga Kalaba zuwa Ibonyi.

  • UNICEF Ya Jaddada Muhimmancin Yi Wa Yaran Afirka Rajistar Haihuwa
  • Tattakin Arba’in: Muna Farin Ciki Da Yadda Gwamnati Ta Fahimci Ayyukan Mu Na Addini – Ahlul-Baiti

Ya bayyana babban titin a matsayin ɗaya daga cikin manyan ayyukan gwamnati da ake aiwatarwa a ƙarƙashin shirin Sabunta Fata na Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu.

 

LABARAI MASU NASABA

An Kashe Mutum 10 A Harin Ramuwar Gayya A Jihar Kebbi

Zargin Almundahana: An Ɗage Shari’ar  Ganduje Da Matarsa Saboda Rashin Miƙa Takardu

Ministan ya bayyana cewa gina gada mai tsawon mita 700 da faɗin 12 a kan titin zai magance matsalar ambaliyar da ta daɗe tana addabar yankin Bakin Ruwa na N’dibe tare da dawo da damar zirga-zirga ga al’ummomin da abin ya shafa.

 

A cewar sa, yanzu ne karon farko da Jihar Ibonyi take samun manyan ayyuka masu yawa na Gwamnatin Tarayya a lokaci guda, wanda hakan alama ce ta jajircewar gwamnati wajen tabbatar da cigaba daidaitacce.

 

Haka kuma ya shawarci masu kwangilar aikin da su kiyaye inganci tare da hanzarta kammala aikin, yana tabbatar wa da jama’ar Nijeriya cewa gwamnati ta mayar da hankali kan ayyukan raya ƙasa da za su inganta rayuwa da hanyoyin samun abin dogaro a duk faɗin ƙasar nan.

 

Ana gina babban titin ‘Trans-Sahara’ ɗin ne ta hannun kamfanin Infouest Nigeria Limited a kan kuɗin da ya kai naira biliyan 445, kuma yana da shimfiɗar kankare mai ƙarfi, sannan ya haɗa Kalaba, Ibonyi, Binuwai, Nasarawa da Abuja.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Mutum 18 Sun Mutu, 40 Sun Jikkata A Hatsarin Mota A Kebbi 
Labarai

An Kashe Mutum 10 A Harin Ramuwar Gayya A Jihar Kebbi

October 28, 2025
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka
Labarai

Zargin Almundahana: An Ɗage Shari’ar  Ganduje Da Matarsa Saboda Rashin Miƙa Takardu

October 28, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe Masu Yi Wa ISWAP 4 Safarar Makamai A Borno

October 28, 2025
Next Post
An Yi Gwaji Na Biyu Na Bikin Tunawa Da Nasarar Sinawa A Yakin Kin Harin Japan 

An Yi Gwaji Na Biyu Na Bikin Tunawa Da Nasarar Sinawa A Yakin Kin Harin Japan 

LABARAI MASU NASABA

Mutum 18 Sun Mutu, 40 Sun Jikkata A Hatsarin Mota A Kebbi 

An Kashe Mutum 10 A Harin Ramuwar Gayya A Jihar Kebbi

October 28, 2025
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka

Zargin Almundahana: An Ɗage Shari’ar  Ganduje Da Matarsa Saboda Rashin Miƙa Takardu

October 28, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

Sojoji Sun Kashe Masu Yi Wa ISWAP 4 Safarar Makamai A Borno

October 28, 2025
Trans-sahara

APC Ta Yi Barazanar Dakatar Duk Kwamishinan Da Bai Sanya Irin Hular Tinubu Ba

October 27, 2025
An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka

An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka

October 27, 2025
Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani

Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani

October 27, 2025
Ribar Manyan Masana’antun Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.2 Cikin Dari A Watanni Tara Na Farkon Bana

Ribar Manyan Masana’antun Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.2 Cikin Dari A Watanni Tara Na Farkon Bana

October 27, 2025
Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Da Burgediya Janar Yake a Matsayin Sarkin Ƙabilar Sayawa

Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Da Burgediya Janar Yake a Matsayin Sarkin Ƙabilar Sayawa

October 27, 2025
Yawan Jigilar Kayayyakin Dake Bukatar Kankara a Kasar Sin Ya Zarce Tan Miliyan 117 a Watannin Yuni Da Yuli Da Agusta

Yawan Jigilar Kayayyakin Dake Bukatar Kankara a Kasar Sin Ya Zarce Tan Miliyan 117 a Watannin Yuni Da Yuli Da Agusta

October 27, 2025
Sin Za Ta Yi Tsayin Daka Wajen Kare Tsarin Cinikayya Tsakanin Mabanbantan Sassa

Sin Za Ta Yi Tsayin Daka Wajen Kare Tsarin Cinikayya Tsakanin Mabanbantan Sassa

October 27, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.