An gano karin gawarwaki uku daga ragowar ashirin da shida (26) wadanda jirgin ruwa ya kife a ranar Lahadi a kauyen Kojiyo da ke karamar hukumar Goronyo a jihar Sokoto, a ranar Talata.
Wata majiya mai tushe ta ce, masunta ne suka gano gawarwakin a yammacin ranar Talata a wurare uku daban-daban.
- NNPP Za Ta Iya Goyon Bayan Takarar Tinubu A 2027 – Sakataren Jam’iyyar
- Ronaldo Ya Samu Kyakkyawar Tarba A Hong Kong
“A yayin da ake ci gaba da neman karin gawarwakin mutanen da hatsarin kwale-kwale ya rutsa da su a ranar Lahadin da ta gabata, an gano gawarwaki uku.
“Masunta ne suka gano gawarwakin uku a wurare daban-daban da suka hada da Kojiyo, Bare da kuma wani kauye a karamar hukumar Wurno, a yayin da suke aikin ceto gawarwakin inda reshen bishiya ya sargafe gawarwakin,” inji majiyar.
An Sallaci gawarwakin tare da birne su kamar yadda addinin Musulunci ya tanada.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp