• English
  • Business News
Wednesday, October 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mafi Ƙarancin Albashin ₦70,000 Ba Zai Iya Tsamo ‘Yan Nijeriya Daga Ƙangin Talauci Ba – Amurka

by Sulaiman
2 months ago
Albashi

Gwamnatin Amurka ta bayyana damuwarta kan dorewar sabon mafi karancin albashin Nijeriya, inda ta yi gargadin cewa ma’aunin na ₦70,000 da aka amince da shi a baya-bayan nan bai isa ya fitar da ‘yan kasar daga kangin talauci ba saboda tabarbarewar tattalin arzikin kasar.

 

A cikin rahotonta na kasa na 2024 kan ayyukan kare hakkin bil’adama, wanda Ofishin Jakadancin Amurka na Ofishin Dimokuradiyya, Kare Hakkokin Dan Adam da kwadago, ya fitar a ranar 12 ga Agusta, 2025, Washington ta yi nuni da cewa, mafi karancin albashi, wanda a halin yanzu ya kai kusan dala 47.90 a kowane wata a kan farashin canji akan N1,500 na dala, yanzu ya ci gaba saboda faduwar darajar Naira.

  • Ac Milan Na Tattaunawa Da Bayern Leverkusen Akan Yunkurin Daukar Boniface
  • Za A Shigar Da Karin Makudan Kudade Domin Ayyukan Kyautata Rayuwar Al’ummun Jihar Xizang Ta Kasar Sin

Rahoton ya lura cewa, duk da cewa dokar ta 2024 (wacce aka yi wa kwaskwarima) ta mafi ƙarancin albashin ma’aikata, ta ninka inda ta baro a baya, amma aiwatar da ita ya zama babban kalubale a duk faɗin ƙasar.

 

LABARAI MASU NASABA

Kano Ta Bai Wa Mata 5,200 Tallafin Naira Miliyan 260

Majalisar Dattawa Ta Maido Da Ranar Tantance Sabbin Shugabannin Sojoji Zuwa Laraba

Ya kara da cewa gwamnatin Nijeriya ba kasafai take tabbatar da bin doka ba, yayin da wasu jihohi suka ki aiwatar da dokar, saboda matsalar kudi.

 

“Kamfanoni da yawa suna da kasa da ma’aikata 25, kuma wannan doka ta fadi a kansu,” in ji rahoton, yana mai jaddada cewa dokar ta shafi kamfanoni ne da ke da ma’aikata 25 ko fiye da haka.

 

Ya kuma kara da cewa, ma’aikatan aikin gona da ma’aikatan wucin gadi, da wadanda ke kan aikin kwangiloli, su ma wannan dokar ta fadi a kansu.

 

Rahoton ya kuma ce, tsakanin kashi 70 zuwa 80 cikin 100 na ma’aikatan Nijeriya na aiki ne a karkashin kansu, suma haka, wannan doka ta fadi a kansu.

 

Bisa kididdigar da Amurka ta yi, yawan masu sa ido kan ayyukan kwadago a kasar bai isa ba wajen sa ido kan yadda ake bin doka da oda, lamarin da ya sa miliyoyin ma’aikata ke fuskantar cin zarafi.

 

Wannan tantancewar dai na zuwa ne a daidai lokacin da Nijeriya ke ci gaba da samun sauye-sauyen tattalin arziki da suka hada da batun cire tallafin man fetur da kuma hada-hadar canjin kudi, wadanda suka haifar da hauhawar farashin kayayyaki da kuma tabarbarewar tsadar rayuwa ga talakawan Nijeriya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kano Ta Bai Wa Mata 5,200 Tallafin Naira Miliyan 260
Manyan Labarai

Kano Ta Bai Wa Mata 5,200 Tallafin Naira Miliyan 260

October 28, 2025
gaza
Manyan Labarai

Majalisar Dattawa Ta Maido Da Ranar Tantance Sabbin Shugabannin Sojoji Zuwa Laraba

October 28, 2025
An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato
Manyan Labarai

An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato

October 28, 2025
Next Post
Nijeriya Ta Kori Ƙarin ‘Yan Ƙasashen Waje 51 Da Aka Ɗaure Bisa Laifin Ta’addanci Da Zamba A Intanet

Nijeriya Ta Kori Ƙarin 'Yan Ƙasashen Waje 51 Da Aka Ɗaure Bisa Laifin Ta'addanci Da Zamba A Intanet

LABARAI MASU NASABA

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

October 28, 2025
JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

October 28, 2025
An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

October 28, 2025
Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

October 28, 2025
Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

October 28, 2025
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe

October 28, 2025
Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Jama’a Ga Tsarin Jagoranci Na Sin

Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Jama’a Ga Tsarin Jagoranci Na Sin

October 28, 2025
Kano Ta Bai Wa Mata 5,200 Tallafin Naira Miliyan 260

Kano Ta Bai Wa Mata 5,200 Tallafin Naira Miliyan 260

October 28, 2025
An Kusa Kammala Shirye-shiryen Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas

An Kusa Kammala Shirye-shiryen Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas

October 28, 2025
Gwamna Bago Ya Amince Da Biyan Karin Albashin Naira 20,000 Ga Ma’aikata 

Gwamnatin Neja Ta Bayar Da Hutun Kwanaki 2 Don Zaɓen Ƙananan Hukumomi

October 28, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.