• English
  • Business News
Thursday, October 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

by CGTN Hausa and Sulaiman
2 months ago
Kasa

A duk ranar 19 ga watan Agusta ne ake bikin ranar jin kai ta duniya, ranar da asali aka kirkire ta domin alhinin jami’an jin kai da aka kashe, ko aka jikkata yayin da suke bakin aiki, tare da jinjinawa daukacin ma’aikatan jin kai da na lafiya dake ci gaba da samar da hidimomin ceton rayukan jama’a, da kare mutanen dake cikin matsanancin yanayin bukatar agaji.

 

To sai dai kuma a bana, bikin ranar ya zo daidai gabar da yanayin da ake ciki, ke kara tunatar da duniya irin muggan laifukan da ake aikatawa ga bil’adama musamman a yankin gabas ta tsakiya.

  • Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025
  • Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

Tashe-tashen hankula na ci gaba da bazuwa tun daga Gaza, zuwa Sudan, da Syria da Yemen, lamarin da ya haifar da mummunan bala’i da yanayin bukatar jin kai, wanda ke nuni da cewa duk da ci gaban da duniya ke samu ta fuskar ilimi, kimiyya da fasahohi, a hannu guda bil’adama na ci gaba da fuskantar manyan kalubalen rayuwa da suka hada da yunwa, da muzgunawa da rashin tsaron rayuka.

 

LABARAI MASU NASABA

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Kirkire-kirkire Da Bude Kofa Da Raba Damar Samun Ci Gaba A Colombo

Sin Ta Fitar Da Jerin Sakamakon Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Tawagar Kasar Da Ta Amurka Suka Cimma 

Alkaluman baya bayan nan na nuna cewa a Gaza, wurin da kusan mutane miliyan biyu ke matse a yankin da bai wuce sakwaya mita 45 ba, adadin mutane da yaki ya hallaka ya munana. Mahukuntan lafiya a wurin na cewa an hallaka sama da mutane 62,000, tun sake barkewar tashin hankali a zirin, ciki har da yara kanana kimanin 18,000. Baya ga karasa gurgunta tsarin kiwon lafiyar birnin, da yunwa da ta haifar da mace-macen jama’a.

 

Haka ma abun yake a Sudan, kasar da tashe-tashen hankula suka raba mutane kimanin miliyan 12 da muhallansu, adadin da ya kai kusan daya bisa hudu na daukacin jama’ar kasar. Wadannan misalai ne na irin matsanancin hali da al’ummun kasashen Yemen da na Syria ke fuskanta, karkashin ayyukan bil’adama ba wai bala’i daga indallahi ba!

 

Don haka, a wannan gaba da ake waiwaye-adon-tafiya, game da wadannan matsaloli na jin kai dake addabar wasu duniya, ya wajaba sassan kasa da kasa, su sauke nauyin dake wuyansu na raya ruhin jin kan bil’adama, ta hanyar shiga tsakani, da warware rigingimu, da gudanar da shawarwarin zaman lafiya, da tallafawa ma’aikatan jin kai, ta yadda za su gudanar da ayyukansu lami lafiya. A hannu guda kuma, a himmatu wajen magance tushen aukuwar tashin hankali a dukkanin sassan duniya, ta yadda za a gudu tare a tsira tare.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Kirkire-kirkire Da Bude Kofa Da Raba Damar Samun Ci Gaba A Colombo
Daga Birnin Sin

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Kirkire-kirkire Da Bude Kofa Da Raba Damar Samun Ci Gaba A Colombo

October 30, 2025
Sin Ta Fitar Da Jerin Sakamakon Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Tawagar Kasar Da Ta Amurka Suka Cimma 
Daga Birnin Sin

Sin Ta Fitar Da Jerin Sakamakon Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Tawagar Kasar Da Ta Amurka Suka Cimma 

October 30, 2025
Babban Daraktan Sakatariyar APEC: Sin Tana Ba Da Gudummawar Ba Da Jagoranci A APEC
Daga Birnin Sin

Babban Daraktan Sakatariyar APEC: Sin Tana Ba Da Gudummawar Ba Da Jagoranci A APEC

October 30, 2025
Next Post
Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Taimaka Wa Ballewar Daurarru A Gidan Yari

Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Taimaka Wa Ballewar Daurarru A Gidan Yari

LABARAI MASU NASABA

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Kirkire-kirkire Da Bude Kofa Da Raba Damar Samun Ci Gaba A Colombo

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Kirkire-kirkire Da Bude Kofa Da Raba Damar Samun Ci Gaba A Colombo

October 30, 2025
An Yi Wa Yara Sama Da Miliyan Biyu Allurar Rigakafin Mashaƙo Da Sankarau A Zamfara

An Yi Wa Yara Sama Da Miliyan Biyu Allurar Rigakafin Mashaƙo Da Sankarau A Zamfara

October 30, 2025
Sin Ta Fitar Da Jerin Sakamakon Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Tawagar Kasar Da Ta Amurka Suka Cimma 

Sin Ta Fitar Da Jerin Sakamakon Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Tawagar Kasar Da Ta Amurka Suka Cimma 

October 30, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

‘Yansanda Sun Ceto Mutum Ɗaya, Sun Kama Mace Da Zargin Garkuwa Da Mutane A Dajin Kwara 

October 30, 2025
Babban Daraktan Sakatariyar APEC: Sin Tana Ba Da Gudummawar Ba Da Jagoranci A APEC

Babban Daraktan Sakatariyar APEC: Sin Tana Ba Da Gudummawar Ba Da Jagoranci A APEC

October 30, 2025
Barcelona Na Shirin Ɗauko Victor Osimhen Na Galatasaray

Barcelona Na Shirin Ɗauko Victor Osimhen Na Galatasaray

October 30, 2025
Kasar Sin Ce Ke Da Sama Da Rabin Muhimman Makaloli Na Duniya

Kasar Sin Ce Ke Da Sama Da Rabin Muhimman Makaloli Na Duniya

October 30, 2025
Tinubu Ya Yi Wa Shugabannin Tsaro Ado Da Sabbin Muƙamai

Tinubu Ya Yi Wa Shugabannin Tsaro Ado Da Sabbin Muƙamai

October 30, 2025
Bunkasar Fannin Kirkire-Kirkiren Fasahohi Na Sin Alheri Ne Ga Dukkanin Duniya Ba Barazana Ba

Bunkasar Fannin Kirkire-Kirkiren Fasahohi Na Sin Alheri Ne Ga Dukkanin Duniya Ba Barazana Ba

October 30, 2025
Sheikh Gumi Ya Yabi Tinubu Kan Afuwar Da Ya Yi Wa Maryam Sanda 

Sheikh Gumi Ya Yabi Tinubu Kan Afuwar Da Ya Yi Wa Maryam Sanda 

October 30, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.