ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, August 3, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

by CGTN Hausa and Sulaiman
12 months ago
Kasa

A duk ranar 19 ga watan Agusta ne ake bikin ranar jin kai ta duniya, ranar da asali aka kirkire ta domin alhinin jami’an jin kai da aka kashe, ko aka jikkata yayin da suke bakin aiki, tare da jinjinawa daukacin ma’aikatan jin kai da na lafiya dake ci gaba da samar da hidimomin ceton rayukan jama’a, da kare mutanen dake cikin matsanancin yanayin bukatar agaji.

 

To sai dai kuma a bana, bikin ranar ya zo daidai gabar da yanayin da ake ciki, ke kara tunatar da duniya irin muggan laifukan da ake aikatawa ga bil’adama musamman a yankin gabas ta tsakiya.

ADVERTISEMENT
  • Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025
  • Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

Tashe-tashen hankula na ci gaba da bazuwa tun daga Gaza, zuwa Sudan, da Syria da Yemen, lamarin da ya haifar da mummunan bala’i da yanayin bukatar jin kai, wanda ke nuni da cewa duk da ci gaban da duniya ke samu ta fuskar ilimi, kimiyya da fasahohi, a hannu guda bil’adama na ci gaba da fuskantar manyan kalubalen rayuwa da suka hada da yunwa, da muzgunawa da rashin tsaron rayuka.

 

LABARAI MASU NASABA

Babban Bankin Sin: Za A Ci Gaba Da Gudanar Da Matakan Saukaka Harkokin Kudade

Yawan Tikitin Kallon Fina Finan Sin Da Aka Sayar A 2026 Ya Zarce Yuan Biliyan 23

Alkaluman baya bayan nan na nuna cewa a Gaza, wurin da kusan mutane miliyan biyu ke matse a yankin da bai wuce sakwaya mita 45 ba, adadin mutane da yaki ya hallaka ya munana. Mahukuntan lafiya a wurin na cewa an hallaka sama da mutane 62,000, tun sake barkewar tashin hankali a zirin, ciki har da yara kanana kimanin 18,000. Baya ga karasa gurgunta tsarin kiwon lafiyar birnin, da yunwa da ta haifar da mace-macen jama’a.

 

Haka ma abun yake a Sudan, kasar da tashe-tashen hankula suka raba mutane kimanin miliyan 12 da muhallansu, adadin da ya kai kusan daya bisa hudu na daukacin jama’ar kasar. Wadannan misalai ne na irin matsanancin hali da al’ummun kasashen Yemen da na Syria ke fuskanta, karkashin ayyukan bil’adama ba wai bala’i daga indallahi ba!

 

Don haka, a wannan gaba da ake waiwaye-adon-tafiya, game da wadannan matsaloli na jin kai dake addabar wasu duniya, ya wajaba sassan kasa da kasa, su sauke nauyin dake wuyansu na raya ruhin jin kan bil’adama, ta hanyar shiga tsakani, da warware rigingimu, da gudanar da shawarwarin zaman lafiya, da tallafawa ma’aikatan jin kai, ta yadda za su gudanar da ayyukansu lami lafiya. A hannu guda kuma, a himmatu wajen magance tushen aukuwar tashin hankali a dukkanin sassan duniya, ta yadda za a gudu tare a tsira tare.

Kasa
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Babban Bankin Sin: Za A Ci Gaba Da Gudanar Da Matakan Saukaka Harkokin Kudade
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Yawan Tikitin Kallon Fina Finan Sin Da Aka Sayar A 2026 Ya Zarce Yuan Biliyan 23
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Fitar Da Shirin Shekaru 5 Na Daukaka Tsarin Tallata Da Samar Da Kayayyaki Domin Kyautata Hidimomi A Kauyuka
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Kaddamar Da Tsarin Biyan Kudi Da Kudin RMB A Kasar Kenya
Kasa
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    DSS Da ‘Yan Sa-kai Sun Kashe Fitaccen Jagoran ‘Yan Bindiga Da Mayaƙansa Sama Da 60 A Katsina
  • Sulaiman
    Iran Ta Musanta Iƙirarin Trump Kan Sabbin Tattaunawa da Amurka
  • Sulaiman
    ‘Yan Ta’adda Sun Kashe Sojoji Shida, Sun Sace Mutane 75 A Zamfara
  • Sulaiman
    Alkalin Babbar Kotun Kebbi Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci, Bayan Shafe Mako Guda A Hannun ‘Yan Bindiga

MASU ALAKA

Babban Bankin Sin: Za A Ci Gaba Da Gudanar Da Matakan Saukaka Harkokin Kudade
Daga Birnin Sin

Babban Bankin Sin: Za A Ci Gaba Da Gudanar Da Matakan Saukaka Harkokin Kudade

August 2, 2026
Yawan Tikitin Kallon Fina Finan Sin Da Aka Sayar A 2026 Ya Zarce Yuan Biliyan 23
Daga Birnin Sin

Yawan Tikitin Kallon Fina Finan Sin Da Aka Sayar A 2026 Ya Zarce Yuan Biliyan 23

August 2, 2026
Sin Ta Fitar Da Shirin Shekaru 5 Na Daukaka Tsarin Tallata Da Samar Da Kayayyaki Domin Kyautata Hidimomi A Kauyuka
Daga Birnin Sin

Sin Ta Fitar Da Shirin Shekaru 5 Na Daukaka Tsarin Tallata Da Samar Da Kayayyaki Domin Kyautata Hidimomi A Kauyuka

August 2, 2026
Next Post
Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Taimaka Wa Ballewar Daurarru A Gidan Yari

Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Taimaka Wa Ballewar Daurarru A Gidan Yari

LABARAI MASU NASABA

DSS

DSS Da ‘Yan Sa-kai Sun Kashe Fitaccen Jagoran ‘Yan Bindiga Da Mayaƙansa Sama Da 60 A Katsina

August 3, 2026
Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Fahimtar Juna Da Aka Cimma Tsakanin Amurka Da Iran

Iran Ta Musanta Iƙirarin Trump Kan Sabbin Tattaunawa da Amurka

August 3, 2026
Zamfara

‘Yan Ta’adda Sun Kashe Sojoji Shida, Sun Sace Mutane 75 A Zamfara

August 3, 2026
Alkalin Babbar Kotun Kebbi Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci, Bayan Shafe Mako Guda A Hannun ‘Yan Bindiga

Alkalin Babbar Kotun Kebbi Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci, Bayan Shafe Mako Guda A Hannun ‘Yan Bindiga

August 3, 2026
Kamfanin Abinci Na ‘BUA Foods’ Ya Samu Ribar ₦292.27bn A Rabin Farkon 2026

Kamfanin Abinci Na ‘BUA Foods’ Ya Samu Ribar ₦292.27bn A Rabin Farkon 2026

August 3, 2026
Kasa

WAFCON 2026: Ƴan Wasan Nijeriya 2 Ba Zasu Buga Wasan Ƙarshe Na Rukunin C Ba

August 2, 2026
Babban Bankin Sin: Za A Ci Gaba Da Gudanar Da Matakan Saukaka Harkokin Kudade

Babban Bankin Sin: Za A Ci Gaba Da Gudanar Da Matakan Saukaka Harkokin Kudade

August 2, 2026
Yawan Tikitin Kallon Fina Finan Sin Da Aka Sayar A 2026 Ya Zarce Yuan Biliyan 23

Yawan Tikitin Kallon Fina Finan Sin Da Aka Sayar A 2026 Ya Zarce Yuan Biliyan 23

August 2, 2026
Kasa

Sojoji Sun Daƙile Harin Ƴan Ta’adda, Sun Ceto Mutane 9 A Zamfara

August 2, 2026
Sin Ta Fitar Da Shirin Shekaru 5 Na Daukaka Tsarin Tallata Da Samar Da Kayayyaki Domin Kyautata Hidimomi A Kauyuka

Sin Ta Fitar Da Shirin Shekaru 5 Na Daukaka Tsarin Tallata Da Samar Da Kayayyaki Domin Kyautata Hidimomi A Kauyuka

August 2, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.