• English
  • Business News
Sunday, September 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Kungiyoyin Firimiyar Ingila Suka Shirya Wa Kakar Bana

by Abba Ibrahim Wada and Sulaiman
3 weeks ago
in Wasanni
0
Yadda Kungiyoyin Firimiyar Ingila Suka Shirya Wa Kakar Bana
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kawo yanzu dai kungiyoyin gasar Premier League ta Ingila sun kashe sama da fan biliyan biyu a bazarar nan, amma har yanzu akwai cinikin da ba a kammala ba kafin rufe kasuwar a ranar Litinin, 1 ga watan Satumba, wanda kuma daga nan ne idan aka rufe kasuwar ba za a sake budewa ba sai a cikin watan Janairu na sabuwar shekarar 2026 kamar yadda a dokar hukumar kwallon kafa ta duniya.

Tuni sababbin ‘yan wasan da suka samu shiga wasu daga cikin kungiyoyi sun fara bayyana kawunansu ta hanyar zura kwallaye a raga kamar yadda muka ga yadda dan wasa Hugo Ekitike ya zura kwallaye biyu cikin wasanni biyu da ya buga a gasar Firimiya da kuma dan wasa Biktor Gyokeres wanda shima ya zura kwallaye biyu a was ana biyu da ya bugawa Arsenal.

 

Arsenal

Yayin da ake tunanin Arsenal ta kammala komai bayan daukar ‘yanwasa ciki har da lamba 9 Biktor Gyokeres. Sai kuma lissafi ya sauya saboda raunin da danwasan gaba Kai Habertz ya ji, wanda ya sa ta fara neman danwasan Crystal Palace Eberechi Eze, wanda tuni ya rattaba hannu a kan kwantiragin shekara biyar kuma zai saka riga mai lamba goma a sabuwar kungiyar tasa.

Labarai Masu Nasaba

Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

Barcelona Ta Farfaɗo Zuwa Matsayi Na Biyu Bayan Lallasa Valencia A Johan Cruyff

Da ma can an yi ta ba da shawara cewa ya kamata Arsenal ta dauki danwasa mai buga gefen hagu kamar Gabriel Martinelli, amma ba ta ce komai ba har sai yanzu. Bayan da cinikin Eze ya fada, yanzu kuma kungiyar ta Arsenal ta sake mayar da hankalinta wajen sayan dan wasan baya daga kungiyar kwallon kafa ta Bayer Liberkusen, wato Piero Hincapie.

 

Chelsea

Da alama har yanzu mai horarwa Enzo Maresca bai hakura da karin cefane ba kafin rufe kasuwar, yayin da yake neman Alejandro Garnacho na Man United da danwasan RB Leipzig Dabi Simons. Sai dai komai zai dogara ne da yawan ‘yanwasan da ta iya sayarwa kamar Nicolas Jackson da Christopher Nkunku da Tyrikue George, wadanda duka kungiyar ta saka a kasuwa. Kociyan zai kuma so ya karfafa bayansa saboda yadda aka ce Lebi Colwill ba zai buga mafi yawan gasar bana ba saboda rauni a gwiwarsa.

 

Crystal Palace

Kungiyar kwallon kafa ta Crystal Palace ba ta yi wata sayayyar kirki ba zuwa yanzu, amma ana sa ran abubuwa za su sauya nan gaba kadan saboda mai horarwa Oliber Glasner na neman danwasan gaba da na baya. Za a yi yunkurin ne saboda makomar ɗanbaya kuma kyaftin dinta Marc Guehi, wanda Liberpool da Manchester City suke zawarci sai kuma danwasan gaba Eberechi Eze, wanda tuni ya koma Arsenal. Ana ci gaba da alakanta Palace da Jeremy Jackuet na Rennes, yayin da kuma take harin danwasan tsakiya Bilal El Khannouss na Leicester City.

 

Liverpool

Mai koyar da ‘yan wasan Liberpool Arne Slot ya samu kudaden cefane masu yawa a bana wadanda ya sayi Florian Wirtz, da Jeremie Frimpong, da Milos Kerkez, da Hugo Ekitike, da Giobanni Leoni. Amma duk da haka yana fatan sake kashe miliyoyi wajen maye gurbin danwasan baya Jarell Kuansah da kuma sama wa Birgil ban Dijk abokin aiki. Ana sa ran za ta nemi Marc Guehi na Crystal Palace. Sai kuma turka-turkar sayen danwasan gaba Aledander Isak daga Newcastle, wanda har yanzu Liberpool bata fitar da ran za ta saya ba.

 

Manchester City

Manchester City ta sayi mafi yawan ‘yanwasanta tun kafin gasar Club World Cup, kuma wasu majiyoyi sun bayyana cewa ta gama sayayya. An yi ta rade-radin cewa tana son daukar mai tsaron ragar kungiyar kwallon kafa ta Paris Saint-Germain Gianluigi Donnarumma, amma tabbas wannan zai danganta ne da mai tsaron raga Ederson, wanda ake ganin shima zai iya barin kungiyar. Tottenham ta nuna sha’awar daukar Sabinho amma City ta ki amincewa zuwa yanzu. Amma idan ta yarda to hakan zai iya ba ta damar sayen danwasan Real Madrid Rodrygo.

 

Manchester United

Shima mai koyar da ‘yanwasan Manchester United Ruben Amorim ya mayar da hankalinsa kan bangaren gaba na tawagar tasa inda ya kashe fan miliyan 200 zuwa yanzu domin sayen Matheus Cunha, da Bryan Mbeumo, da Benjamin Sesko. Amma a bayyane take cewa United na da matsala a mai tsaron raga, yayin da Andre Onana ya gaza kuma shi ma Altay Bayindir ya fara aikata manyan kurakurai a wasansu da Arsenal. United na tunanin daukar Senne Lammens na Royal Antwarp.

 

Newcastle United

Har yanzu makomar Aledander Isak na cikin kokwanto duk da yunkurin mai horarwa Edie Howe na karfafa tawagarsa. Zuwa yanzu kungiyar ta sayi Anthony Elanga daga Bournemouth, da Jacob Ramsey daga Aston Billa, da Malick Thiaw daga AC Milan, kuma har yanzu kungiyar tana neman sayan dan wasan gaba kafin ta saki Aledandre Isak.

Yanzu dai kungiyar ta kwallafa kan Yoane Wissa amma kuma tana fuskantar turjiya daga Brentford saboda yadda ta ki yarda da tayin fan miliyan 40 kan dan wasan mai shekara 28 a duniya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yan Wasan Afirka Da Ake Ganin Za Su Yi Abin Kirki A Kakar Bana

Next Post

Ko Zuwan Rasha Afirka Zai Inganta Tsaro A Yankin Sahel?

Related

Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica
Wasanni

Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

2 days ago
Barcelona Ta Farfaɗo Zuwa Matsayi Na Biyu Bayan Lallasa Valencia A Johan Cruyff
Wasanni

Barcelona Ta Farfaɗo Zuwa Matsayi Na Biyu Bayan Lallasa Valencia A Johan Cruyff

6 days ago
Kano Pillars Ta Samu Nasarar Farko A Gasar Firimiyar Nijeriya Ta Bana
Wasanni

Kano Pillars Ta Samu Nasarar Farko A Gasar Firimiyar Nijeriya Ta Bana

6 days ago
Sama Da Fam Biliyan Uku Aka Kashe A Firimiyar Ingila Wajen Sayen Ƴan Wasa
Wasanni

Sama Da Fam Biliyan Uku Aka Kashe A Firimiyar Ingila Wajen Sayen Ƴan Wasa

6 days ago
Me Ya Sa Bayern Liverkusen Ta Kori Erik Ten Hag Bayan Wasanni Biyu?
Wasanni

Me Ya Sa Bayern Liverkusen Ta Kori Erik Ten Hag Bayan Wasanni Biyu?

6 days ago
Ba Lallai Ne FIFA Ta Cirewa Afrika Ta Kudu Maki 3 Ba – Rayond Hack
Wasanni

Ba Lallai Ne FIFA Ta Cirewa Afrika Ta Kudu Maki 3 Ba – Rayond Hack

1 week ago
Next Post
Ko Zuwan Rasha Afirka Zai Inganta Tsaro A Yankin Sahel?

Ko Zuwan Rasha Afirka Zai Inganta Tsaro A Yankin Sahel?

LABARAI MASU NASABA

Kin Amincewar Japan Game Da Muggan Laifukan Yakin Da Ta Aikata Ya Dakatar Da Bukatar Sin Ga Hukumar UNESCO

Kin Amincewar Japan Game Da Muggan Laifukan Yakin Da Ta Aikata Ya Dakatar Da Bukatar Sin Ga Hukumar UNESCO

September 20, 2025
An Gabatar Da Fim Mai Taken Shen Zhou 13 A Kasar Birtaniya

An Gabatar Da Fim Mai Taken Shen Zhou 13 A Kasar Birtaniya

September 20, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Martaba Hakkokin Kamfanoni

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Martaba Hakkokin Kamfanoni

September 20, 2025
Abin Fashewa Ya Tarwatse A Masana’antar Ƙera Makamai Ta Sojojin Nijeriya A Kaduna

Abin Fashewa Ya Tarwatse A Masana’antar Ƙera Makamai Ta Sojojin Nijeriya A Kaduna

September 20, 2025
Shugaban Kasar Iran Ya Yi Tsokaci Kan Shawarar Tsarin Inganta Jagorancin Duniya

Shugaban Kasar Iran Ya Yi Tsokaci Kan Shawarar Tsarin Inganta Jagorancin Duniya

September 20, 2025
Ko Me Ya Sa Jihar Xinjiang Ta Kasar Sin Ke Kara Janyo Hankalin Al’ummun Duniya?

Ko Me Ya Sa Jihar Xinjiang Ta Kasar Sin Ke Kara Janyo Hankalin Al’ummun Duniya?

September 20, 2025
Wang Yi Ya Gana Da Takwaransa Na Kasar Morocco

Wang Yi Ya Gana Da Takwaransa Na Kasar Morocco

September 20, 2025
Peng Liyuan Ta Halarci Bikin Mika Lambobin Yabo A Fannin Raya Ilimin Yara Mata Da Mata Na Hukumar UNESCO 

Peng Liyuan Ta Halarci Bikin Mika Lambobin Yabo A Fannin Raya Ilimin Yara Mata Da Mata Na Hukumar UNESCO 

September 20, 2025
Mun Kawo Ƙarshen Dogon Layin Mai Na Shekara 50 A Nijeriya – Matatar Dangote

Mun Kawo Ƙarshen Dogon Layin Mai Na Shekara 50 A Nijeriya – Matatar Dangote

September 20, 2025
Sin Da Amurka Na Iya Cimma Manyan Nasara Tare In Ji Shugaba Xi

Sin Da Amurka Na Iya Cimma Manyan Nasara Tare In Ji Shugaba Xi

September 20, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.