• English
  • Business News
Sunday, October 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Mutum 9 Da Harsasai 4,264 Da Muggan Makamai A Nasarawa 

by Zubairu M Lawal and Sulaiman
2 months ago
Makamai

Kwamishinan ‘Yansandan jihar Nasarawa CP. Shattima Muhammad ya bayyanawa manema labarai rawar da Rundunar ‘yansandan jihar suka taka wajen kama masu aikata miyagun laifuka. Kwamishinan ya bayyana cewa rundunar ta kama mutum 9 tare da kwato harsasai 4,264 a wasu ayyukan sintiri da aka gudanar a ƙananan hukumomi 13 na jihar.

 

CP Shattima Mohammed, ne ya bayyana hakan a taron manema labarai da aka gudanar a ofishin rundunar a Lafia, babban birnin jihar.

  • Jarin Da Sin Ta Zuba Kai Tsaye A Kasashe Cikin Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Ya Karu Da Kashi 22.9% A 2024
  • Nan Gaba TIinubu A Wajen Opay Da Moniepoint Zai Nemi Rancen Kuɗi – Dino Melaye

Yayin da yake bayyana alkaluman a babban birnin jihar, Lafia, CP Mohammed ya ce, “A ranar 7 ga Satumba, 2025, da misalin ƙarfe 6:30 na yamma, bisa sahihan bayanan sirri cewa, wasu da ake zargin masu safarar makamai daga jihar Benuwe sun isa wani daji da ke iyakar Kadarko, a karamar hukumar Keana , suna sauke makamai da harsasai domin rarraba wa abokan harkarsu.

 

LABARAI MASU NASABA

Ɗan Majalisa Ya Ce Ba Zai Sake Takara Ba, Ya Sadaukar Da Ita Ga Matasa

Abin Da Ya Sa Aka Yi Watsi Da Tashar Jiragen Ruwa Ta Kan Tudu Da Ke Jihar Kaduna

“Da samun rahoton, babban jami’in ‘yansanda na yankin, ya jagoranci tawagar jami’an ‘yansanda kai tsaye zuwa wurin.

 

“Da suka hango jami’anmu, sai suka ajiye kayan suka tsere cikin daji. Binciken wurin ya haifar da gano makaman nan: bindigogi AK-49 guda huɗu, bindigogi AK-47 guda uku, bindiga G3 guda ɗaya, bindiga ƙarama (Sub-Machine Gun) guda ɗaya, mujallu harsasai guda goma sha ɗaya, harsasai 7.62mm guda 4,046, harsasai 5.5mm guda goma sha ɗaya, harsasai 38mm guda 132, da harsashi guda 75.”

 

CP Mohammed ya ƙara da cewa, a wani samame da aka yi ranar 6 ga Satumba, 2025, bisa bayanan sirri, an kama wani mutum mai suna John Paul daga Abuja a tashar motar Akwanga-Wamba yayin da yake kan hanyarsa zuwa Abuja. Da aka binciki jikinsa, an gano bindigogi biyar kirar gida, kuma wanda ake zargin ya bayyana cewa da akwai abokan harkansa. Tuni ‘yansanda suka bazama nimansu.

 

Haka kuma da misalin ƙarfe 3:00 na dare jami’an da ke ofishin ‘E’ Division a Shabu, cikin Lafia, sun kama manyan masu ƙera bindigogi biyu, James Philip da Alpha Philip, dukkansu maza ne daga unguwar Faferuwa, Lafia.

 

“Bincike ya kai ga kama manyan masu saye da sai da bindigogin da aka kirar gida , waɗanda suka haɗa da Usman Abubakar daga Shendam Road, Lafia Yakubu Danladi daga Mararaba Akunza, Lafia; Usman Kasimu wanda aka fi sani da Bobo daga Bukan Sidi, Lafia; da Abdullahi Adamu daga Bukan Sidi, Lafia.

 

Abubuwan da aka kwato daga hannunsu sun haɗa da: bindigogi dogaye guda 13, bindigogi ƙanana guda 10, bindiga Revolver guda ɗaya, takuba guda uku, Rigunan sanye na ƴan sanda guda uku da hulun su, injinan ƙera bindiga guda uku da kayan aiki,

 

Yayin da yake yabawa jajircewar jami’an sa, CP Shattima Mohammed ya tabbatar wa mazauna jihar cewa rundunar ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen kawar da miyagun mutane a Nasarawa.

 

Ya ce, “Ina kira ga kowa ya kasance mai lura, mai bin doka, kuma ya rika bayar da bayanai ga Rundunar yan sanda.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ɗan Majalisa Ya Ce Ba Zai Sake Takara Ba, Ya Sadaukar Da Ita Ga Matasa
Labarai

Ɗan Majalisa Ya Ce Ba Zai Sake Takara Ba, Ya Sadaukar Da Ita Ga Matasa

October 26, 2025
Abin Da Ya Sa Aka Yi Watsi Da Tashar Jiragen Ruwa Ta Kan Tudu Da Ke Jihar Kaduna
Labarai

Abin Da Ya Sa Aka Yi Watsi Da Tashar Jiragen Ruwa Ta Kan Tudu Da Ke Jihar Kaduna

October 26, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Wasu Mutum Biyu Da Ake Zargi Da Haɗa Baki Da ‘Yan Bindiga A Kano

October 26, 2025
Next Post
Kasar Sin Ta Samar Da Kaso 30 Na Jimillar Kason Ci Gaban Masana’antun Duniya A Tsakanin 2021 Zuwa 2025

Kasar Sin Ta Samar Da Kaso 30 Na Jimillar Kason Ci Gaban Masana'antun Duniya A Tsakanin 2021 Zuwa 2025

LABARAI MASU NASABA

Ɗan Majalisa Ya Ce Ba Zai Sake Takara Ba, Ya Sadaukar Da Ita Ga Matasa

Ɗan Majalisa Ya Ce Ba Zai Sake Takara Ba, Ya Sadaukar Da Ita Ga Matasa

October 26, 2025
Abin Da Ya Sa Aka Yi Watsi Da Tashar Jiragen Ruwa Ta Kan Tudu Da Ke Jihar Kaduna

Abin Da Ya Sa Aka Yi Watsi Da Tashar Jiragen Ruwa Ta Kan Tudu Da Ke Jihar Kaduna

October 26, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

‘Yansanda Sun Kama Wasu Mutum Biyu Da Ake Zargi Da Haɗa Baki Da ‘Yan Bindiga A Kano

October 26, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwamnatin Kaduna Tare Da  AUDA–NEPAD Sun Tallafa Wa Manoma 400 Da Kayan Noma

October 26, 2025
Tornadoes Ta Doke Pillars A Wasan Farko Na Babaganaru

Tornadoes Ta Doke Pillars A Wasan Farko Na Babaganaru

October 26, 2025
Gwarzon Kamfanin Samar Da Kayayyakin Gida Na Mai Da Gas Na Shekarar 2025 Kamfanin GEIL

Gwarzon Kamfanin Samar Da Kayayyakin Gida Na Mai Da Gas Na Shekarar 2025 Kamfanin GEIL

October 26, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwarzon Ɗan Majalisa Na Shekarar 2025: Benjamin Okezie Kalu

October 26, 2025
An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

October 25, 2025

Nafisa Abdullahi Aminu: Yarinyar Da Ta Ɗaukaka Darajar Nijeriya A Idon Duniya

October 25, 2025
Sin Da Amurka Sun Fara Tattaunawa Kan Tattalin arziki Da Cinikayya A Kuala Lumpur

Sin Da Amurka Sun Fara Tattaunawa Kan Tattalin arziki Da Cinikayya A Kuala Lumpur

October 25, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.