• English
  • Business News
Saturday, November 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

by Shehu Yahaya
2 months ago
Makaranta

Biyo bayan dokar da Hukumar tabbatar da ingancin makarantu ta jihar Kaduna (KSSƘAA), ta sanyawa makarantu masu zaman kansu dangane da matsalar yawaitar ƙara ku ɗaɗan makaranta ba bisa ƙa’ida ba da kuma ƙara litattafan ɗalibai da dai sauransu Manufar dokar ita ce, inganta ingancin koyarwa da kuma kare haƙƙin ɗalibai da iyayensu.

A kwanan baya  ne hukumar tabbatar da ingancin makarantu ta jihar Kaduna (KSSƘAA), ta gargaɗi masu makarantu masu zaman kansu kan ƙara kuɗin makaranta ba tare da samun amincewar gwamnatin jihar a hukumance ba.

A wata takarda mai kwanan ranar 7 ga Satumba, 2023, wacce Mercy Bainta Kude, Daraktar Sashen Makarantu masu zaman kansu ta sanya wa hannu a madadin Darakta-Janar, Hukumar ta jaddada Tewa “babu wani ko wata mai makaranta da zai ko za ta ƙara kuɗin makaranta ko inganta makarantar ba tare da amincewar KSSƘAA ba. Ƙarin kuɗin makarantu a irin Wannan zagon karatun wato zagon na karatu yana ciwa iyaye tuwo a ƙwarya musamman ganin lokacine da ake biyan kuɗin makarantar ɗalibai da sayan littafan karatu lamarin da sanya wasu makarantu yin amfani da wata dama wajen ƙara kuɗin makaranta ba bisa ƙa’idaba.

  • Dawowa Hutu Ya Tayar Da Hankalin Iyaye Saboda Ƙarin Kuɗin Makaranta
  • Gwamnatin Bauchi Ta Cire Shugaban Makaranta Kan Satar Kayan Gwamnati

Hakazalika , masana harkar ilimi Sunce matakin kafa dokoki masu tsauri kan makarantun masu zaman kansu yana fuskantar barazana da ƙalubale iri-iri, musamman tun bayan sanarwar kwanan baya na hana ƙara kuɗin makaranta ba tare da amincewa daga gwamnati ba.

Duk da cewa akwai wasu ƙalubale, da dama daga cikin jama’a na goyon bayan wannan doka.

LABARAI MASU NASABA

Mabiya Mazhabar Shi’a Sun Yi Zanga-Zanga A Kano Kan Barazanar Trump Ga Nijeriya

Bisa Rakiyar Jami’an Tsaro Na Ke Ganawa Da Ƴan Bindiga – Sheikh Gumi

Muhawara game da sanya doka a kan makarantu masu zaman kansu yana ta ci gaba a  ciki da wajen jihar Kaduna saboda ƙaruwar makarantun masu zaman kansu a cikin ƴ an shekarun nan musamman a cikin sabbin unguwanni da ke cikin ƙwaryar Kaduna.

Abubuwan da jama’a ke magana a kai sun haɗa da tabbatar da inganci, kare haƙƙoƙin ɗalibai, da daidaita kuɗaɗe.

Masu mallakar makarantun masu zaman kansu sun koka da yawan haraji da tsadar aiki, wanda ya sa su yi tsayin daka  wajen ƙara kuɗin makaranta.

Sanya doka mai tsauri na iya ƙara musu nauyi kuma ya tilasta wasu rufe makarantunsu.

Sai dai masana harkar ilimi Sun bayyana cewa daidaitawa da haɓaka inganci: dokar za ta sa makarantu masu zaman kansu su bi ƙa’idojin koyarwa na jihar Kaduna, wanda hakan zai inganta ingancin ilimi ga kowa.

Hakazalika,  dokar za ta taimaka wajen kare iyalai daga biyan kuɗi mai tsoka da kuma tabbatar da cewa suna samun ilimi mai inganci a farashi mai sauƙi Hasalima, da yawa daga cikin wadannan makarantun  wato makarantu masu zaman kansu  suna da ƙarancin inganci saboda suna ɗaukar ma’aikatan da ba su da cikakkiyar horo saboda rashin son biyan su albashi mai tsoka.

Wannan matsala na tattare da ingancin ilimi ga zalibai. Da dama daga cikin makarantun masu zaman kansu ba su da kayan aiki da ya kamata, kamar ɗakunan karatu da ɗakunan gwaje-gwaje. Wasu daga cikinsu suna amfani da gine-gine masu haɗari da ba a duba ingancinsu ba, wanda hakan yana haifar da haɗari ga ɗalibai.

Hakan ya sanya da  dama daga cikin jama’a na goyon bayan dokar da gwamnatin jihar Kaduna ta sanya; suna ganin cewa hakan zai daidaita ingancin koyarwa da kuma sa makarantu su riƙa bin ƙa’idoji.

Binciken leadership Hausa ya gani cewa wasu masu makarantun masu zaman kansu sun nuna damuwa game da dokar, suna jin cewa hakan zai ƙara musu nauyi da kuma rage musu damar samun riba.

Ɗaya daga cikin manyan ƙalubale shi ne rashin iya sa ido kan makarantun masu zaman kansu. Akwai haɗarin cin hanci da rashawa, wanda zai iya sa a yi watsi da ƙa’idoji.

Wasu na cewa dokar ba za ta iya magance matsalar ingancin koyarwa ba, matuƙar gwamnati ba ta inganta makarantun ta na gwamnati ba.

A zantawar da Wakilinmu da wasu iyaye Sun bayyana hamsuwarsu dangane da Wannan dokar inda suka sanya dokar tazo a daidai lokacin da ake buƙata.

Hakazalika, Sunce muddin gwamnatin jihar Kaduna Tana son ɗorewar dokar sai ta Samar da Jami’ai waɗanda zasu rinƙa biybiyar makarantun domin tabbatar da dokar Tana aiki yadda ya kamata.

Wasu makarantun da wakilinmu ya Kai ziyara a ƙananan hukumomin Kaduna ta Arewa da ta Kudu da kuma ƙaramar hukumar Igabi wacce tafi kowacce ƙaramar hukuma yawan makarantu masu zaman kansu Sun bayyana cewa idan wannan dokar ta ɗore kuma basu samu Tallafin gwamnatin ba babu shakka akwai yiwuwar durƙushewar makarantu da yawan gaske duba da ganin cewa kuɗaɗan da ɗalibai suke biya dana sayar da littafai sune suke riƙe makarantun suna masu cewa rashin samun hakan zai haifar musu da ƙalubale mai tarin yawa.

Wani mamallakin wata makaranta a garin Hayin Rigasa da Unguwar Kawo sun tabbatarwa da wakilinmu cewa a haƙiƙanin gaskiya basa goyon bayan Wannan dokar muddin ba  za’a basu damar ƙara ɗudin makaranta inda suka ce ƙarin kuɗin man fetur shi kaɗai ya cancanci wasu makarantun su ƙara kuɗinsu domin suma malaman da suke koyarwa Sun samu ƙarin kuɗin abun hawa Wanda dole a ƙara musu albashi.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Mabiya Mazhabar Shi’a Sun Yi Zanga-Zanga A Kano Kan Barazanar Trump Ga Nijeriya
Manyan Labarai

Mabiya Mazhabar Shi’a Sun Yi Zanga-Zanga A Kano Kan Barazanar Trump Ga Nijeriya

November 8, 2025
Bisa Rakiyar Jami’an Tsaro Na Ke Ganawa Da Ƴan Bindiga – Sheikh Gumi
Manyan Labarai

Bisa Rakiyar Jami’an Tsaro Na Ke Ganawa Da Ƴan Bindiga – Sheikh Gumi

November 8, 2025
Barau Zai Yi Ƙarar Kwamitin Yaƙin Neman Zaɓen Gawuna/Garo Kan Zargin Karɓar Cin Hancin Dala Miliyan 10
Manyan Labarai

Barau Zai Yi Ƙarar Kwamitin Yaƙin Neman Zaɓen Gawuna/Garo Kan Zargin Karɓar Cin Hancin Dala Miliyan 10

November 8, 2025
Next Post
Shugaba Xi ya zanta ta wayar tarho da takwaransa na Amurka

Shugaba Xi ya zanta ta wayar tarho da takwaransa na Amurka

LABARAI MASU NASABA

Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

November 8, 2025
Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne

Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne

November 8, 2025
Yadda Aka Tsara Gudanar Da Gasar Kofin Afirka A Moroko

Yadda Aka Tsara Gudanar Da Gasar Kofin Afirka A Moroko

November 8, 2025
CMG Ya Watsa Jerin Shirye-Shirye Don Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

CMG Ya Watsa Jerin Shirye-Shirye Don Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

November 8, 2025
CMG Ya Gabatar Da Jerin Rahotannin Talabijin Kan Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

CMG Ya Gabatar Da Jerin Rahotannin Talabijin Kan Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

November 8, 2025
Xi Ya Yi Kiran Zurfafa Gyare-gyare Da Bude Kofa A Yayin Rangadin Aiki A Guangdong

Xi Ya Yi Kiran Zurfafa Gyare-gyare Da Bude Kofa A Yayin Rangadin Aiki A Guangdong

November 8, 2025
Ta’aziyyar Rasuwar Jarumin Kannywood, Malam Nata’ala

Ta’aziyyar Rasuwar Jarumin Kannywood, Malam Nata’ala

November 8, 2025
Kamfanoni Masu Jarin Waje Na Samun Kwarin Gwiwa Daga CIIE

Kamfanoni Masu Jarin Waje Na Samun Kwarin Gwiwa Daga CIIE

November 8, 2025
Lalacewar Tarbiyar Dalibai Mata A Makarantun Islamiyya Da Na Boko

Lalacewar Tarbiyar Dalibai Mata A Makarantun Islamiyya Da Na Boko

November 8, 2025
Mabiya Mazhabar Shi’a Sun Yi Zanga-Zanga A Kano Kan Barazanar Trump Ga Nijeriya

Mabiya Mazhabar Shi’a Sun Yi Zanga-Zanga A Kano Kan Barazanar Trump Ga Nijeriya

November 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.