• English
  • Business News
Saturday, September 20, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

by Shehu Yahaya
8 hours ago
in Manyan Labarai
0
Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Biyo bayan dokar da Hukumar tabbatar da ingancin makarantu ta jihar Kaduna (KSSƘAA), ta sanyawa makarantu masu zaman kansu dangane da matsalar yawaitar ƙara ku ɗaɗan makaranta ba bisa ƙa’ida ba da kuma ƙara litattafan ɗalibai da dai sauransu Manufar dokar ita ce, inganta ingancin koyarwa da kuma kare haƙƙin ɗalibai da iyayensu.

A kwanan baya  ne hukumar tabbatar da ingancin makarantu ta jihar Kaduna (KSSƘAA), ta gargaɗi masu makarantu masu zaman kansu kan ƙara kuɗin makaranta ba tare da samun amincewar gwamnatin jihar a hukumance ba.

A wata takarda mai kwanan ranar 7 ga Satumba, 2023, wacce Mercy Bainta Kude, Daraktar Sashen Makarantu masu zaman kansu ta sanya wa hannu a madadin Darakta-Janar, Hukumar ta jaddada Tewa “babu wani ko wata mai makaranta da zai ko za ta ƙara kuɗin makaranta ko inganta makarantar ba tare da amincewar KSSƘAA ba. Ƙarin kuɗin makarantu a irin Wannan zagon karatun wato zagon na karatu yana ciwa iyaye tuwo a ƙwarya musamman ganin lokacine da ake biyan kuɗin makarantar ɗalibai da sayan littafan karatu lamarin da sanya wasu makarantu yin amfani da wata dama wajen ƙara kuɗin makaranta ba bisa ƙa’idaba.

  • Dawowa Hutu Ya Tayar Da Hankalin Iyaye Saboda Ƙarin Kuɗin Makaranta
  • Gwamnatin Bauchi Ta Cire Shugaban Makaranta Kan Satar Kayan Gwamnati

Hakazalika , masana harkar ilimi Sunce matakin kafa dokoki masu tsauri kan makarantun masu zaman kansu yana fuskantar barazana da ƙalubale iri-iri, musamman tun bayan sanarwar kwanan baya na hana ƙara kuɗin makaranta ba tare da amincewa daga gwamnati ba.

Duk da cewa akwai wasu ƙalubale, da dama daga cikin jama’a na goyon bayan wannan doka.

Labarai Masu Nasaba

Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

Nan Ba Da Jimawa Ba Hauhawar Farashin Kayayyaki Za Ta Zama Tarihi —Fadar Shugaban

Muhawara game da sanya doka a kan makarantu masu zaman kansu yana ta ci gaba a  ciki da wajen jihar Kaduna saboda ƙaruwar makarantun masu zaman kansu a cikin ƴ an shekarun nan musamman a cikin sabbin unguwanni da ke cikin ƙwaryar Kaduna.

Abubuwan da jama’a ke magana a kai sun haɗa da tabbatar da inganci, kare haƙƙoƙin ɗalibai, da daidaita kuɗaɗe.

Masu mallakar makarantun masu zaman kansu sun koka da yawan haraji da tsadar aiki, wanda ya sa su yi tsayin daka  wajen ƙara kuɗin makaranta.

Sanya doka mai tsauri na iya ƙara musu nauyi kuma ya tilasta wasu rufe makarantunsu.

Sai dai masana harkar ilimi Sun bayyana cewa daidaitawa da haɓaka inganci: dokar za ta sa makarantu masu zaman kansu su bi ƙa’idojin koyarwa na jihar Kaduna, wanda hakan zai inganta ingancin ilimi ga kowa.

Hakazalika,  dokar za ta taimaka wajen kare iyalai daga biyan kuɗi mai tsoka da kuma tabbatar da cewa suna samun ilimi mai inganci a farashi mai sauƙi Hasalima, da yawa daga cikin wadannan makarantun  wato makarantu masu zaman kansu  suna da ƙarancin inganci saboda suna ɗaukar ma’aikatan da ba su da cikakkiyar horo saboda rashin son biyan su albashi mai tsoka.

Wannan matsala na tattare da ingancin ilimi ga zalibai. Da dama daga cikin makarantun masu zaman kansu ba su da kayan aiki da ya kamata, kamar ɗakunan karatu da ɗakunan gwaje-gwaje. Wasu daga cikinsu suna amfani da gine-gine masu haɗari da ba a duba ingancinsu ba, wanda hakan yana haifar da haɗari ga ɗalibai.

Hakan ya sanya da  dama daga cikin jama’a na goyon bayan dokar da gwamnatin jihar Kaduna ta sanya; suna ganin cewa hakan zai daidaita ingancin koyarwa da kuma sa makarantu su riƙa bin ƙa’idoji.

Binciken leadership Hausa ya gani cewa wasu masu makarantun masu zaman kansu sun nuna damuwa game da dokar, suna jin cewa hakan zai ƙara musu nauyi da kuma rage musu damar samun riba.

Ɗaya daga cikin manyan ƙalubale shi ne rashin iya sa ido kan makarantun masu zaman kansu. Akwai haɗarin cin hanci da rashawa, wanda zai iya sa a yi watsi da ƙa’idoji.

Wasu na cewa dokar ba za ta iya magance matsalar ingancin koyarwa ba, matuƙar gwamnati ba ta inganta makarantun ta na gwamnati ba.

A zantawar da Wakilinmu da wasu iyaye Sun bayyana hamsuwarsu dangane da Wannan dokar inda suka sanya dokar tazo a daidai lokacin da ake buƙata.

Hakazalika, Sunce muddin gwamnatin jihar Kaduna Tana son ɗorewar dokar sai ta Samar da Jami’ai waɗanda zasu rinƙa biybiyar makarantun domin tabbatar da dokar Tana aiki yadda ya kamata.

Wasu makarantun da wakilinmu ya Kai ziyara a ƙananan hukumomin Kaduna ta Arewa da ta Kudu da kuma ƙaramar hukumar Igabi wacce tafi kowacce ƙaramar hukuma yawan makarantu masu zaman kansu Sun bayyana cewa idan wannan dokar ta ɗore kuma basu samu Tallafin gwamnatin ba babu shakka akwai yiwuwar durƙushewar makarantu da yawan gaske duba da ganin cewa kuɗaɗan da ɗalibai suke biya dana sayar da littafai sune suke riƙe makarantun suna masu cewa rashin samun hakan zai haifar musu da ƙalubale mai tarin yawa.

Wani mamallakin wata makaranta a garin Hayin Rigasa da Unguwar Kawo sun tabbatarwa da wakilinmu cewa a haƙiƙanin gaskiya basa goyon bayan Wannan dokar muddin ba  za’a basu damar ƙara ɗudin makaranta inda suka ce ƙarin kuɗin man fetur shi kaɗai ya cancanci wasu makarantun su ƙara kuɗinsu domin suma malaman da suke koyarwa Sun samu ƙarin kuɗin abun hawa Wanda dole a ƙara musu albashi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: MakarantaSchool
ShareTweetSendShare
Previous Post

Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

Next Post

Shugaba Xi ya zanta ta wayar tarho da takwaransa na Amurka

Related

Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna
Manyan Labarai

Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

9 hours ago
Nan Ba Da Jimawa Ba Hauhawar Farashin Kayayyaki Za Ta Zama Tarihi —Fadar Shugaban
Manyan Labarai

Nan Ba Da Jimawa Ba Hauhawar Farashin Kayayyaki Za Ta Zama Tarihi —Fadar Shugaban

19 hours ago
Ce-ce-kuce Kan Shirin Ƙara Wa Ƴan Siyasa Masu Riƙe Da Madafun Iko Albashi
Manyan Labarai

Ce-ce-kuce Kan Shirin Ƙara Wa Ƴan Siyasa Masu Riƙe Da Madafun Iko Albashi

20 hours ago
NNPP
Manyan Labarai

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

1 day ago
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna
Manyan Labarai

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

1 day ago
Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis
Manyan Labarai

Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

2 days ago
Next Post
Shugaba Xi ya zanta ta wayar tarho da takwaransa na Amurka

Shugaba Xi ya zanta ta wayar tarho da takwaransa na Amurka

LABARAI MASU NASABA

Kamfanin Kasar Sin Ya Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Sudan Ta Kudu

Kamfanin Kasar Sin Ya Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Sudan Ta Kudu

September 19, 2025
Yadda Ciwon Hanta Ke Yaɗuwa Tsakanin Ma’aurauta

Yadda Ciwon Hanta Ke Yaɗuwa Tsakanin Ma’aurauta

September 19, 2025
An Kammala Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan

An Kammala Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan

September 19, 2025
Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Mahawara Na MDD Karo Na 80

Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Mahawara Na MDD Karo Na 80

September 19, 2025
Shugaba Xi ya zanta ta wayar tarho da takwaransa na Amurka

Shugaba Xi ya zanta ta wayar tarho da takwaransa na Amurka

September 19, 2025
Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

September 19, 2025
Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

September 19, 2025
Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Bunkasa Ci Gaban Mata

Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Bunkasa Ci Gaban Mata

September 19, 2025
Ofishin Yada Labarai Na Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Ya Fitar Da Takardar Bayani Mai Taken “Nasarar Aiwatar Da Manufar JKS A Xinjiang A Sabon Zamani”

Ofishin Yada Labarai Na Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Ya Fitar Da Takardar Bayani Mai Taken “Nasarar Aiwatar Da Manufar JKS A Xinjiang A Sabon Zamani”

September 19, 2025
Makaranta

Tarihin Ahmadu Bello Sardaunan Sakkwato Firimiyan Arewa

September 19, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.